14/07/2026
DAN TAKARAR MAJALISSAR WAKILAI NA ADC, HON. BASHIR YAKUBU WADA, YA KAI ZIYARAR JAJE GA AL'UMMAR GARIN MAKAURACHI
A ranar litinin 13-07-2026ne Dan takarar Majalisar Wakilai mai wakiltar Karamar Hukumar Malumfashi a karkashin tutar Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC), Hon. Bashir Yakubu Wada, ya kai ziyarar jaje ga daukacin al'ummar Garin Makaurachi da ke Karamar Hukumar Malumfashi, sak**akon mummunan harin 'yan bindiga da ya yi sanadiyyar rasa rayuka tare da jikkata wasu daga cikin mazauna garin.
A yayin ziyarar, Hon. Bashir Yakubu Wada ya gana da iyalan wadanda s**a rasa rayukansu, inda ya bayyana alhininsa da jimaminsa bisa wannan mummunan lamari. Ya yi addu'ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa mamatan, Ya jikansu da rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsu, tare da bai wa iyalansu hakurin jure wannan babban rashi.
Haka kuma, Hon. Wada ya ziyarci wadanda s**a samu raunuka sak**akon harin, inda ya yi musu addu'ar Allah Ya ba su cikakkiyar lafiya Inda yaroki Allah Ya ba su ikon komawa rayuwarsu ta yau da kullum cikin koshin lafiya.
A ci gaba da ziyarar, Hon. Bashir Yakubu Wada ya kai ziyara ga rundunar tsaron al'umma ta 'Yan Sakai (Vigilante), inda ya yaba matuka da irin jajircewa, sadaukarwa da kuma kokarin da suke yi wajen kare rayuka da dukiyoyin al'umma. Ya bukace su da su ci gaba da gudanar da aikinsu cikin gaskiya da kishin al'umma.
A yayin wannan ziyarar ta jaje, Hon. Wada ya kuma bayar da tallafi ga al'ummar garin domin rage musu radadin halin da suke ciki. Sai dai ya bayyana cewa tallafin da ya bayar ba zai iya maye gurbin rayukan da aka rasa ba, illa dai wata gudummawa ce ta nuna tausayi da goyon baya ga iyalan mamatan, tare da neman al'umma su ci gaba da yi wa mamatan addu'a.
A karshe, Hon. Bashir Yakubu Wada ya yi kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su kara daukar matakan da s**a dace domin kawo karshen hare-haren 'yan bindiga da tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin al'umma a Karamar Hukumar Malumfashi