Comr.Abdulmalik lawal beguwa

Comr.Abdulmalik lawal beguwa My name is Abdulmalik lawal Mahmud,I was born in the of 1990,at malumfashi local government katsina state of Nigeria.

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 20         BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHIZaune suke kewaye da mummy a Falor bayan isha'i,faruk na zaune ...
27/07/2025

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 20
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI
Zaune suke kewaye da mummy a Falor bayan isha'i,faruk na zaune yana latsa waya,jalila da zulaihat suna duba wani littafin adduo'i suna musu akanshi,Anty amarya ta fito cikin daguwar riga mai kyau da tsari,ta gabansu tazo ta wuce duk s**a gaisheta daya bayan daya,ta amsa tana yatsina mummy ko kallon inda take batayi ba,fridge din falor ta bude ta dakko juice ta koma daki,tana jin hon ďin motar daddy tayi maza ta mike ta kara gyara jikinta ta feshe jikinta da ni'imtaccen turare,sai da taji ya shigo sannan ta fito tana tafiyar hawainiya,ta karaso cikin falon ta dan durkusa tace sannu yaya,mummy da mamaki ya isheta ko kallon inda take batayi ba,daddy ya lura tsaf da mummy sannan yabi dukka yaran da kallo dan baiji sun gaisheta ba,haba nan da nan ranshi ya baci sosai ya kalli mummy da ta haďe girar sama da ta kasa yace Aisha bakiji ana gaisheki bane,mummy tace banji ba ta cigaba da kallon tv,daddy ya kalli faruk yace kai dan ubanka baka iya gaisuwa bane,cikin rashin fahimta yace dad-- bai bari ya karasa ba ya shiga surfa musu ruwan bala'i anty amarya na gefenshi tana kukan munafurci tana bashi hakuri,
ya kalli zulaihat da kanta ke sukunye yace harda ke zuwan jiya har an koya miki rashin kunya an nuna miki karki daraja matata to wallahi babu wanda ya isa ya taka min mata ina kallo haka ya dinga masifa mummy bata kalli inda yake ba bare tasan abinda yake fadi,
zagin da taji anty amarya tayi ma zulaihat ne yasata mikewa a fusace,kuma dama tayi hakan ne dan ta harzuka mummy,Cikin fushi mummy ta janyo zulaihat dake rakube a kusa da jalila duk kuka sukeyi,tace Hadiza kikace mata yar matsiyata?
kinsan waye matsiyaci?to ki bude kunnenki dakyau kijini,
matsiyaci shine wanda duk abinda ake bashi baya isar shi sai ya hada dana haram,matsayaci shine wanda yake siyar da mutuncinshi dan ya samu kudi a kirashi da mai arziki,matsiyaci shine mai arzikin dake nuna halin tsiya k**ar yadda k**eyi.
kuma yanada daga cikin siffofin matsiyaci mutum ya zama munafuki algungumi k**ar yadda k**e,sai kiyi alkalanci tsakanin ke da ita waye matsiyaci?
kinga wannan yarinyar,ta fi min ke da duk wani wanda ya rabeki,haushi k**eji saboda na aurawa abba ita ko,to bari kiji ko bayan raina jinina bazai taba haduwa da jinin fasikai irin---- wawan marin da daddy ya dauketa dashi ne ya hanata karasa maganar da takeyi,faruk ya mike da sauri jikinshi na rawa ya fita daga gidan gaba daya idonshi jawur,daddy yace a gabana k**e fifita wata banza akan matata,a gabana k**e kiran matata fasika,lallai Aisha kin cika marar mutunci me manta alkhairi, duk irin biyayyar da hadiza take miki baki gani,yanzu dama akan wannan yarinyar gidana yake neman k**awa da wuta, wallahi badan nasan darajar aure ba da a yau sai yarinyar nan ta bar min gidana,amma kisa a ranki,duk ranar da abba ya dawo yace baya son yarinyar nan,wallahi tallahi zan goya mishi baya dari bisa dari ya auri wacce yakeso.
Dan kinga na kyaleki kina yadda k**eso da ya'yana to komai yazo karshe,ya cigaba da masifarshi mummy dake tsaye rike da kunci hawaye na zuba akansu ta juya ta barshi a gurin yanata masifa,daki s**a wuce ita da jalila da zulaihat dukkansu kuka sukeyi.
Daddy ya zauna bayan yayi masifar mai isarshi muryarshi har ta fara dishewa saboda bai iya masifar ba,ya shiga rarrashin anty amarya dake kuka sosai,yace ya isa hadiza,cikin kuka ta tureshi tace me yasa zaka mareta?
wallahi zafin marin a jikina najishi,wata rana zata gane kuskurenta tasan ni mai kaunarta ce,amma yanxu ka kara goga min bakin jini,yaya ta kasa gane irin son da nake mata,amma da sannu zata gane.""ta kara rushewa da kuka.''yiii-yii....wayyo..wayyo......
ya dinga rarrashinta yanajin tausayinta a zuciyarshi dan yasan tana kaunarsu dukkansu har cikin ranta,to me ya canza Aisha ta tsaneta lokaci daya,me ya canzata take neman rushe farin cikin gidanshi magana yakeyi a zuci baisan ta fito ba.Anty amarya tayi saurin mikewa tace Zulaihat.Shigowar Zulaihat gidan nan yana neman rusa da farin cikin daya ginu lokaci mai tsawo.Irin yaran nan burinsu su auri mutum ya mutu suci gado amma yaya ta kasa ganewa,ni tausayi ma take bani saboda makashinta yana jikinta,daddy ya gyada kanshi ya daura duk akalar tunaninshi akan Zulaihat baiwar Allah.
(kissa tafi magani sunan wani littafi).

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 19       BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHIDakinshi ya wuce ya kwanta yana ta juyi, Astaghfirullah...Astagfi...
27/07/2025

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 19
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI
Dakinshi ya wuce ya kwanta yana ta juyi, Astaghfirullah...
Astagfirullah......Astagfirullah......
Kalmar da ya dinga fadi kenan a bayyane,saboda farat daya zuciyarshi ta kamu da son macen da ta haramta a gareshi har abada,ya dinga godiya ga Allah da yasa ya sani da wuri,tabbas kallo ďaya yayi mata yaji wani abu game da ita,a kallon da yayi mata na biyu zuciyarshi ta fara kitsa mishi wani sabon al'amari mai wuyar faďuwa. Hannunshi ya daga sama yace Allah na gode maka daka sanar dani wacece ita a kallon da nayi mata na uku,Ya lumshe idonshi a hankali yana neman tsari daga sharrin shaidan dan yasan duk aikinshi ne wannan,cikin ikon Allah har bacci yayi gaba dashi....
Kuka sosai anty amarya keyi a gaban daddy,duk wanda ya ganta a wannan lokacin zai dauka daga can cikin zuciyarta take kukan,hankalin daddy ya tashi matuka,yace subhanallahi hadiza lafiya me ya faru,cikin muryar kuka tace babu komai,da sauri yace k**ar yaya babu komai,fada min abinda ke faruwa mana,ta kara narke murya tace banason ace na fara kawo kara,duk abinda akeyi min a cikin gidan nan ina shanye wa na dauki yaya tamkar ita ta haifeni shiyasa kome zatayi min bana daukarshi da zafi,amma bazan jure gaba da ita ba.
Ina matukar shan wahala saboda rashin kulani da bata yi kwata-kwata bata amsa gaisuwata,haka ta hana su jalila gaisheni,yau kwanan faruk hudu a gidan nan ko sau daya bai je inda nake ba bare yayi tunanin gaisheni, dan Allah ka bata hakuri in nayi ma wani laifi ta karasa fadi tana sheshshekar kuka k**ar da gaske,ran daddy ya baci sosai yace ita Aishan ce bata kulaki,anty amarya ta gyada kai tana share hawaye,yace me kikayi mata to,cikin sanyin murya tace babu abinda na mata,daddy ya mike a fusace zai fita tayi maza ta riko shi,tace kayi hakuri daddy bazan juri inga kana ma yaya fada ba dan Allah karka mata magana zata ce kararta na kawo gurinka kuma zai kara zame mana matsala, nidai inason ka lura da kanka idan kaga yadda muke tafiyar da alamuran mu sai kayi mata magana,amna yanzu in ka sameta ai komai baci zaiyi.
Daddy yayi ajiyar zuciya yace wallahi da kin barni naje na sameta,suma su faruk din sai naci mutuncinsu,anty amarya tace kayi hakuri yara ne,kuma ni duk abinda zasu min bazan taba rikeshi ba saboda son da nake musu ko da dan da na haifa banajin zan iya mishi irinshi,ta dangwabe a jikinshi tace ina matukar kaunar jininka fiye da yadda nakeson kaina ma,dadi daddy yaji har cikin ranshi ya rungumota sosai yana rarrashinta nan ta kasheshi da kissarta mai zafi wacce take ma mummy zagon kasa da ita...

◆◆ ZULAIHAT ◆◆ 18 BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.Laila ce ta fara ganinshi ta fadada fara'arta tace faruk yaushe ka da...
08/07/2025

◆◆ ZULAIHAT ◆◆ 18
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.
Laila ce ta fara ganinshi ta fadada fara'arta tace faruk yaushe ka dawo,yace yanzun nan anty ya rankwashi kan jalila dake shan fruit salad yace acici,ta ajiye cokalin din ta rungumeshi tace yaya faruk oyoyo,shine baka fada azo a dauke ka ba,ya harareta yace sai kace wani yaro,anty ina mummina,anty laila tace suna school nasan yanzu zaka gansu,sannu dan autan mijin yau kai zanyi yayi fadi duk abinda kakeso in kawo maka,yayi dariya yace I trust u anty ki kawo min kome kuka dafa,jalila cikin murna tace to Dan uwa,ta kwaso ragowar kayan da basu jera a dining ba ta jera,sannan ta zuba mishi abinci tana mishi hira dan taji dadin dawowarshi,yace to parrot barni in ci abinci,ta turo baki tace kai yaya dan ma kaga ina murna ka dawo shine kake min wulakanci ko,yace sorry sister surutunki ne yayi yawa,tace to shikenan da naso in baka labarai amma na fasa,yace yi hakuri kanwata zauna ki tayani cin abinci in mun gama sai ki bani ko,ta zauna ta zuba abinci s**a ci tare tana mishi hira..Zulaihat na daki tsoro ya hanata fitowa duk tunaninta shine wanda aka daura mata aure dashi,afrah ce ta shigo dakin ta tsaya gabanta tace anty zage min zip mummy tana sallah kuma anty jalila tace bazata zage min ba saboda naki bata ice cream din da daddyn aida ya siyo man.
zulaihat ta janyota ta zage mata zip tace me yasa kika hanata rowa babu kyau,afrah tace ba kowa yasha nashi muna bacci ba;ni bazan bata nawa ba,zulaihat tace to muje in miki wanka sai ki kira amrah ma in mata ko,afrah tace ai anty jalila ta mata saboda ita ta bata nata,zulaihat tayi dariya tace to muje in miki, s**a shiga bayin ta mata wanka s**a fito ta shafa mata mai,tace je ki dakko kayanki in sa miki,ta fita da gudu taje daki ta dakko kayanta da mummy ta fito musu dashi,tayima jalila dake ma amrah kwalliya gwalo ta ruga da gudu jalila tabi bayanta itama da gudu,ihuuu!!! afrah ta dinga yi saboda jalila ta kusa kamota,a tare zulaihat da faruk s**a fito a firgice sun dauka wani abun ne ya sameta,jikin zulaihat afrah ta fada tana maida numfashi tana dariya,jalila ta karaso ta daga hannu zata kai mata duka,faruk dake tsaye yana kallon zulaihat ya daka mata tsawa,yace baki da hankali ne,me ta miki,jalila tace wallahi yaya yarinyar nan ta raina ni,da ta miki me ya fadi yana kallonta,afrah tayi saurin guduwa bayanshi tace (yaya umar sunan da mummy ke kiranshi suma haka suke kiranshi ita da amrah)babu abinda na mata wai dan tace insammata ice cream naki shine taki min wanka kuma ta biyoni zata duke ni,jalila tace wallahi karya take min gwalo fa ta min ni sa'arta ce da zata min gwalo,faruk yace kusan sa'arta dince ke tunda bakinki ya iya kwadayin abun yara komai kika gani sai kinsha,ta turo baki k**ar zatayi kuka tace wallahi yau Allah ne kadai zai kwaceki,afrah ta kara mata gwalo tana dariya,jalila tace yaya kana ganin abinda takemin ko wallahi yau sai naji ma yarinyar nan ciwo,ta wuce daki ranta a bace,zulaihat ta dauki kayan afrah tace zo muje in shiryaki,afrah ta rugo gurin zulaihat s**a wuce daki s**a bar faruk baki sake yana kallonta,wai wacece wannan, ya fadi a fili,yarinyar is so cute,ya daga kafadunshi ya juya daki yana siffanta yanayin zulaihat a zuciyarshi..
Da safe bayan ya dawo sallar asuba ya shiga dakin mummy,zaune ya samesu tare da zulaihat tana kara ma mummy karatu,gefensu ya zauna yana sauraron kira'arta yana bin karatun idonshi a lumshe,sai da s**a idar sannan ya bude idonshi ya kalli zulaihat da ke kwashe qur'anai,ta sunkuya tace ina kwana,yace lafiya lau malama,ta ajiye qur'anan gurin da suke ta fita,ya dawo kusa da mummy yace ina kwana mummy,tace lafiya lau umar ya gajiyar hanya,yace tabi lafiya mummy,nan s**a fara hirar school dinshi,har gurin karfe takwas suna hira,har ya tashi zai tafi ya dawo yace wai mummy a ina kika samo wannan kyakykyawar malamar,mummy tayi dariya tace malama ce amma tá gida,ya zauna yace ban gane ba,tace Amaryar Abba ce,gaban faruk ya fadi sosai yace wane abban,mummy tace na nan gidan yayanka,abinda yasa bamu fada muku ba saboda muna son muyi muku surprise,ko shi abban bai sani ba,faruk yayi ajiyar zuciya yace gaskiya yaya abba ya dace sosai,Allah ya basu zaman lafiya,mummy ta bude murya cikin farin ciki tace ameen umar,yayi murmushi ya tashi ya fita jikinshi a sanyaye..............

08/07/2025
◆◆ ZULAIHAT◆◆ 17BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.Tavern hotel nan naga motar da sanah ta shiga a bakin titin Governor ro...
05/07/2025

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 17
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.
Tavern hotel nan naga motar da sanah ta shiga a bakin titin Governor road tayi parking,Wani hadadden gaye ne ya fito daga cikin motar ya zagayo gefen sanah ya bude mata kofa,ya rungumota suna tafe suna hira har s**a kai ciki,a kofar shiga ne s**ayi karo da wani saurayi shima kyakykyawa,baya ya koma da sauri yana fadin sorry pls,s**a hada ido da saurayin da s**a shigo tare da sanah, bude baki s**ayi dukkansu suna dariya,saurayin dake tare da sanah yace Hilal kana duniya,dayan saurayin ya mika mishi hannu yace ina nan Hafiz 2days ka buya,rabona da kai zai kai 3years fa,hafiz yace hakane kam,ya kake,ya su baba,hilal yace suna nan lafiya tare muke dashi ma suna ciki shi da abokinshi,ya kalli sanah dake makale jikin hafiz tana kallonshi,yace sannu ko yammata,tayi fari da ido tace yauwa,hilal yace hafiz sauri nakeyi zanje in dauko ma su baba abinci a gida bani numberka,yace to ya karbi wayar ya sa mishi number,yace ma sanah ta jirashi ya rakashi****
Hilal ya kalle shi da s**a fita yace hafiz kana nan da neman mata har yanzu,hafiz yayi dariya yace sune ginshikin rayuwa mutumina,wannan ma yau na hadu da ita,dama ina tunanin kwana ni daya a hotel kasan a kano nake yanzu,hilal yace Allah ya shirya to ai gara ka riketa ka aureta dan ta hadu sosai,hafiz yayi tsaki yace wannan ba ta aure bace mutumina macen da daga haduwa ta yarda da kai ai ba irinsu ake aure ba,hilal yayi murmushi yace ka dai ji tsoron Allah ni bari in wuce sai na kiraka,hafiz yace ok sai na jika abokina.
Satin zulaihat uku a gidansu mummy,fatarta ta murje saboda mayukan da take shafawa, ta koyi komai na gidan cikin kankanin lokaci,kullum ita ke karawa mummy karatun qur'ani da littafai,haka wasu ayukan girki tare sukeyi da laila,Wata ranar jumma'a suna tsaye dukkansu a kitchen suna girkin jumma'a k**ar yadda aka saba yi a gidan,kowa da aikin da yakeyi suna hira,jalila ta kalli zulaihat dake haďa salad,cikin tsokana tace anty laila kinga matar yaya abba an dan fara murjewa ji yadda ta daddage tana hada salad,zulaihat tayi murmushi bata kalleta ba dan ta saba da tsokanar jalila,anty laila tace kedai jalila baki da kunya wallahi,matar yayan naki k**e ma iskanci,bari in gama foilin zaki sani dan da mummy zan hada ki,ko kuma in kira abban in fada mishi,jalila tace yauwa anty yaya abba na kiranki kuwa,tace a'a kuma ko na kirashi ma baya ďauka,jiya ma abban aida ke min korafin baya kiranshi,jalila tace umhmm ko mummy baya kira kuma kinsan bai san maganar auren nan ba,laila tace eh ina ganin akwai abin da ya tsareshi ne,jalila ta tabe baki tace babu wani abun da ya tsare shi ai yana kiran anty amarya,laila tace kai jalila bansan sharri,jalila tace Allah anty ba sharri bane,naga missed call dinshi har 7 a wayarta,anty laila tayi jugumm sannan tace to Allah ya kyauta amma baki fada ma mummy ba ko,tace eh ban fada mata ba, tace to kiyi shuru da bakinki..
zulaihat ta mika ma anty laila salad din ta k**a wani aikin,anty laila ta kalleta tace baki gajiya ne ke,kije kiyi wanka fatsin zata karasa gyara kitchen din,zulaihat tace to anty,ta wanke hannunta ta kalli jalila dake mata wani irin kallon tsokana kasa-kasa tana murmushi,ta yarfa mata ruwan hannunta tace kyaji dashi ta fita da gudu,jalila ta kwashe da dariya tana goge fuskarta tace lallai yarinyar nan taci abinci,laila tace aitamin dai-dai,jalila tace zan rama ne aitasan hali naZulaihat na fita daga kitchen tayi karo sosai da mutum wayar dake hannunshi ta faďi,da sauri taja da baya jikinta ya fara rawa ta d**o kai ta kalleshi yana tsaye shima kallonta yakeyi sanye yake da red top da ta karbi fatar jikinshi gashin kanshi a kwance da ganinshi kasan hutu ya gama ratsa shi k**arshi daya da Nurain sai dai yafi nurain kyau,ta tsuguna da sauri ta dauki wayar tace dan Allah kayi hakuri wallahi bansani ba,bai amsa mata ba ya mika hannu ya karba,ta bi ta gefenshi ta wuce ya bita da kallo har ta bace ma ganinshi sannan yayi ajiyar zuciya ya shiga kitchen ......

◆◆ ZULFAH ◆◆ 16       BY COMR.ABDULMALIK LAWAL MALUMFASHISai gurin 11 s**a fita,saloon s**a fara zuwa aka wanke mata kan...
27/06/2025

◆◆ ZULFAH ◆◆ 16
BY COMR.ABDULMALIK LAWAL MALUMFASHI

Sai gurin 11 s**a fita,saloon s**a fara zuwa aka wanke mata kanta da kafa,daga nan s**a wuce kasuwa s**ayi siyayya sosai,atamfofi,laces da material takalma sai sarkoki,sun kashe kudi sosai a kasuwa,ahanyarsu ta komawa gida s**a biya passion cosmetic s**a kwaso mayuka da turaruka masu kyau da tsada,zulaihat dai kallonsu kawai takeyi k**ar basu jin zafin kudin haka take fadi a ranta,"senegls"nan s**a je karshe inda tela ya gwada zulaihat,jalila tace kayi mata styles masu kyau fa,ina material dina,yace saura kadan kinsan aikin akwai wahala,tace haka dai ka ke cewa ka iya yawa wollah.Yaushe zaka kawo wadannan to,yayi jumm sannan yace tunda express ne kuma kunce Inji mummy zan gama nan da 1month,anty laila ta rike baki tace lallai Hayatu baka da mutumci,ka bari sai nan da shekara daya ma wannan kai da mummy,Hayatu yayi dariya yace anty kayan da yawa zanyi kokarin gamawa cikin 1wk insha Allahu,anty laila tace ok now you are right.jalila tace Allah yasa dan ban yadda ba,hayatu yace aiko zan baki mamaki;tace da dai wani ne bakai ba,ta fita tana dariya....sadik itama dawowarta gidan kenan,sannu da gida s**a ce mata gaba dayansu sannan s**ayi hanyar dakin mummy,tayi tsaki mai karfi ta cigaba da wayar da takeyi,sadik yace anty ke da wa k**e tsaki kuma,tace ni da wadannan kitifaffun mana,wai daukar wannan yar kauyen s**ayi s**a yo mata shopping,jalila harda rungumeta saboda munafurci,yayi tsaki yace duk zasu gane kurensu anty,ina nan dawowa nan kusa zan warware duk kullin su,ni dai dan Allah ki taimakeni ki fadamin numbr da zan sami sanah,wallahi ina cikin tsananin damuwa.Tayi murmushin mugunta tace abba kayi hakuri da maganar sanah,ni banason tashin hankali,karka kara kirana ma bare ayi tunanin ni ke zuga ka,cikin damuwa yace haba anty,so k**eyi in mutu ko kuma wani ciwo ya k**ani,wallahi na kasa maida hankalina a karatu,kirjina zafi yake min,meyasa sanah zata hukunta ni akan laifin da bansan dashi ba.Anty amarya zuciyarta wasai dan taga alamun daga zuciyarshi yake fadin wadannan kalaman,a hankali tace dukkanku hakuri zakuyi,dan itama sanah tana can bata ko iya cin abinci,Cikin damuwa yace can ina anty?tace ta tafi ai,muryarta ta dan fara rawa tace yau tun safe yaya tayita zaginta akan yarinyar nan,zagi sosai tayi mata har jalila na sa baki,Sadik ya dafe kanshi yama rasa me zece,shurun da anty taji ne yasa tace kana jina abba,uhmm kawai yace mata,tace kayi hakuri kayi ma yaya biyayya,ka cire---sallamar nurain ce ta katse mata maganar,tayi saurin kashe wayar s**a gaisa cikin sakin fuska,sai da yayi gaba tabi bayanshi da harara,al'adar anty amarya kenan kowa a gidan haka take mishi sai kun gaisa ko kun gama magana da ita cikin sakin fuska sai tabi bayanka da harara,ta tsani yaran gidan da mahaifiyarsu amma saboda tsabar iya bariki da kissa babu wanda yake ganewa dan nunawa takeyi tafi son su akan mahaifansu,wannan dalilin yasa daddy yake girmamata saboda tana nuna ma ya'yanshi da matarshi so da kulawa ta karya,ta dade tana neman dalilin da zai haddasa fada a gidan sai yanzu ta samu wannan damar daga gurin sakarai sadik.....

ZULAIHAT ●15  BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.Washe gari tun kafin asuba zulaihat ta farka saboda ta riga ta saba lokac...
26/06/2025

ZULAIHAT ●15
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.

Washe gari tun kafin asuba zulaihat ta farka saboda ta riga ta saba lokacin nayi bacci zai kauracewa idonta,ta dinga bin dakin da aka kaita ta kwana da kallo kaya barkatai dan tun da aka shigo da ita take kare ma dakin kallo barin toilet din da yaji kayan gyara.
Tashi tayi a hankali ta shiga bayin tayi tsarki ta kunna ruwa k**ar yadda jalila ta nuna mata tayi alwala,tsayawa tayi gaban mudubin bayin tana kare ma kanta kallo,sai da ta dan dade sannan ta fito ta shimfida dadduma tayi nafila kafin a kira sallar asuba,karantun kur'ani ta dinga yi da"ka",batare da ta duba kur'ani ba.Har aka kira sallah tana karatu tana idarwa ta mike tayi sallah,ta zauna tana addu'oi tana tuno rayuwarta ta baya,ko yanzu me goggo takeyi tasan tana can tana aikin waina,haka ta dinga tunanin su goggo da salaha da babanta,ta share kwallar da ta digo mata a idonta ta karasa adduointa ta nade daddumar ta maida ita mazauninta,Kofar dakin taji an bude ta waigo s**a hada ido da mummy,ta karaso ciki itama da hijab da carbi a hannunta tana murmushi,
zulaihat ta durkusa da sauri tace ina kwana, mummy ta d**ota tace lafiya lau zulaihat ya kwanan bakon guri,zulaihat ta sunne kanta tace lafiya lau,mummy tace to alhamdulillahi ki saki jikinki kema yar gida ce,banason wannan dari-darin da k**eyi,da ke da laila da jalila duk daya kuke a gurina,saboda haka ki daukeni matsayin uwa kinji,Zulaihat tace to in sha Allah,mummy tace yauwa diyata,bari inje daki kema ki kwanta ki huta kafin a kawo miki abin kari,zulaihat tace to.
Amma babu wani aikin da zanyi,mummy tace a'a je ki kwanta ki huta kinji,zulaihat ta gyada kanta ta koma ta zauna bakin gado.Gurin karfe 9am jalila ta turo kofar dakin, lokacin zulaihat na tsaye tana goge jiki,ta juyo da sauri zata tsuguna jalila ta hxade rai tace tashi-tashi wai so k**eyi kija min bala'i ne,na fada miki karki kara tsuguna min bakiji ba ko,ki rufamin asiri mu dinga gaisawa daga tsaye,,kuma ki saki jikinki kinji?
Zulaihat tace to,jalila tace yauwa,yanzu ki shirya ki fito mu karya ta ajiye mata doguwar riga a kan gado ta fita,zulaihat ta duba rigar taga katuwa ce irin ta jiya,har kasa take kai mata,ta koma gaban madubi,mai kadai ta shafa ta dauki rigar ta saka ta rufe kanta da gyalen ta sakko falon,a bangaren dining taga mummy da jalila suna zaune suna hira, karasawa tayi ta tsuguna ta kara gaida mummy,mummy tayi murmushi tace ai mun gaisa zulaihat tashi ki zauna anan,ta nuna mata kujerar kusa da ita,zulaihat ta zauna cikin jin kunya tana ta sinne kai,jalila tayi serven dinsu mummy da kanta ta hada ma zulaihat tea...
mai kauri ta tura gabanta tace maza ki shanye duka,zulaihat tace to,da kyar kunya ta barta ta fara cin dankali da sauce din hanta,a tare s**a gama karyawa dukkansu,mummy ta koma cikin falon ta zauna,zulaihat ta taya jalila kai kaya tsaftataccen kitchen din da k**ar ba anan ake girki ba.Fatsin ce tsaye a ciki tana wanke-wanke,zulaihat ta karasa kusa da fatsin tace kawo in tayaki,fatsin ta wage baki tace a'a jeki abinki ai na kusa gamawa,zata kara magana jalila taja hannunta tace zo mu tafi ciki mummy zatayi fada in taga kina aiki,Falor s**a wuce zulaihat ta rabe gefen kujera,mummy tayi murmushi a ranta tace da sannu zaki saki jiki.Sai da s**a dan dade sannan mummy tace zulaihat ajinki nawa a school,zulaihat tace jss(3) nake zan shiga ss.Mummy tace wace makaranta kikayi? ta kara sunkuyar da kanta tace nayi I.G.E.A unguwar rimi dana gama malam salim ya samo min capital school,mummy tace good,kina sha'awar cigaba daga ss1 din?jalila tayi dariya tace haba mummy me zai hana tayi sha'awa,ai kawai gara in anyi resuming ta dinga zuwa ko,mummy zatayi magana shewar da taji ta katseta,daga kanta tayi taga sanah janye da trolley anty amarya rike da jaka,har s**a karaso cikin falon basu kalli inda su mummy suke ba sai hirarsu sukeyi suna dariya,sai da s**a zo daf dasu anty amarya tayi murmushin rainin wayau tace yaya ina kwana, mummy da mamaki ya cika ta tace lafiya lau,sanah ta kara gyara dankwalinta tana kallon zulaihat tana kas-kas da cingam,ina kwana zulaihat ta fadi hade da kara tankwashe kafa,s**a mata kallon uku saura kwata,sannan sanah ta kwashe da dariya harda rike ciki,anty amarya ta dake cikin kissa tace banason iskanci wuce mota gani nan,ran mummy ya baci sosai da abinda sanah tayi mata dan ko gaishe ta batayi ba,anty amarya tace yaya bari in kai sanah gidan aneesah,mummy tace to a dawo lafiya,bata jira jin abinda zata ce ba ta kalli jalila tace tashi kuje gurin laila in ta gama kuzo ku tafi shopping din,jalila tace to mummy s**a mike suke wuce side din laila, mummy ta mike tayi hanyar sama ta bar anty amarya tsaye tana hararar bayanta,sai da ta gaji dan kanta tayi kwafa ta wuce waje tana sakar zuci...

●● ZULAIHAT ●● 14BY comr.Abdulmalik lawal MalumfashiA hankali yace to anty amma dan Allah kuyi hakuri,tace babu komai ka...
21/06/2025

●● ZULAIHAT ●● 14
BY comr.Abdulmalik lawal Malumfashi
A hankali yace to anty amma dan Allah kuyi hakuri,tace babu komai kaima Allah ya baka hakurin juriyar rashin sanah dan tausayi kuke bani dukkanku,gata nan banda kuka babu abinda takeyi.kuka ne kadai sadik baiyi ba,yace bazan iya rabuwa da ita ba anty,ko me za'ayi sai dai ayi wallahi dan sanah ta zama wani bangare a zuciyata dan haka ki ma daina wannan maganar,anty amarya tace dole kayi hakuri da ita ab-- ya katseta da sauri yace anty bani sanah please!,tayi murmushi dan tasan sanah ta diga mishi dafinta mai wuyar goguwa lallai ta samu damar aiwatar da kudirinta ta hanyar sadik,ta kwantar da murya tace bazai yiwu kayi magana da ita ba kayi hakuri kawai Allah ya hada kowa da rabonshi.
Tayi saurin kashe wayar tana murmushin mugunta,ta kashe wayar gaba dayanta,ta kalli sanah tace mun k**a sadik sanah,tabbas zai bijire ma mahaifiyar shi,ni kuma zanyi ta hura wuta ta a can kasa tsakanin dukansu ukun,daddy,mummy da shi sadik,wannan karan sai nayi nasara akanta dan haka gobe ki shirya ki tafi kuma karki kara daukar wayarshi.ke kima canza layi nasan bazai jure ba zai biyoki,ke kuma sai kisan yadda zakiyi ki rikita shi ya dawo ya saki waccen sauran yunwar.kinga anan komai zai dagule sai insan yadda zanyi in jawo abba jikina ta yadda zamu cin ma burin mu,sanah ta share hawayenta tayi murmushin jindadi zuciyarta tayi sanyi dan bata jin zata iya rayuwa ba tare da sadik ba.....
Sadik juyi kawai yakeyi wani abu ya tokare mishi makogoranshi,kuka kawai yakeson yi amma ya kasa,meyasa mummy zatayi mishi haka,wace irin mace mummy ta aura mishi?Tambayoyin da ya dinga yi kenan ya kasa samun amsoshinsu,yayi huci ya daga murya yace gaskiya mummy sai dai kiyi hakuri amma bazan iya zama da macen da bana so ba,shi a tsarinshi yafi son mace wayayya mai aji amma shi sam bazai iya zama da irin macen da mummy ke kwaso musu ba.Yayi tsaki ya kara kiran layin sanah karo na na ashirin da uku ya kara jinta a kashe,ya wurgar da wayar ta fadi ta fashe ya buga hannunshi a bango yanajin wani irin zafi a ranshi,bazan iya jure wannan punishment dinba bazan iya baaaa!!
Dole ya nemi hutu ya dawo gida yayi solving problems dinshi,dole ya ganar da mummy kowa yanada yancin yin abinda ya keso,ya wuce bayi a fusace ya sakar ma kanshi ruwa yanajin tsanar duka yan gidansu saboda suna neman rabashi da ruhinshi, bazai kara nemansu ba sai dai kawai su ganshi....
Lailah tsaye gaban mudubi tana tsefewa ZULAIHAT kanta da yayi mugun datti,tanayi tana goge hannunta saboda dauďar tayi yawa,tace ke kuwa yaushe rabonki da tsifa kinga kanki yanda yayi datti ya cukurkuďe, zulaihat tayi murmushi cikin kunya tace hmmm kawai,laila na gama mata tsifa ta taje tayi mata parking dinshi a tsakiyar kai,laila tace gaki da gashi amma saboda rashin gyara ya dunkule guri ďaya,shi kanshi ya galabaita ta fadi tana dariya,zulaihat tayi murmushi a ranta tace inata kaina wake ta gashin da na manta rabona da budeshi,anty laila tace tashi ki cire uniform din nan muje in nuna miki komai na bayi sai kiyi wanka a kaiki saloon,ta mike tace to,sun kusa da bayin jalila ta shigo da sallama, anty laila ta amsa tace jalee ina kuka shiga ne,jalila ta ajiye doguwar rigar da mummy ta bata bayan ta gama mata tatas kuma tace tazo gurinsu lailan ta dinga Jan zulaihat a jiki,ta kalli anty laila tace muna garden ne,tayi murmushi tace amaryar yaya abba sannu,zulaihat ta tsuguna tace ina wuni,jalila ta kwashe da dariya tace tashi ni ba ruwana kar ki kara tsuguna min kisa mummy ta yi punishing dina da fushinta,laila tayi dariya tace ai fa,ta ďago zulaihat s**a wuce bayi.
Jalila ta rike baki tana mamakin mummy, yarinyar tana da kyau amma tayi karama da yawa,yadda yaya abba keji da kanshi,yan mata masu aji ke kawo kansu ya kare a wannan kucakar,lallai akwai bala'i in ya dawo,ta kwantar da kanta kan kujera......

18/06/2025

CONTINUETION OF PAGE 13.
( ZULAIHAT)
yanzun nan zan kira mummy ta warware auren da ta dauko ma kanta,da sauri anty amarya ta katse shi cikin kwarewa a iya bariki tace karkayi haka,ka nuna musu bakasan zancen ba, in ba su s**a tare ka dashi ba, in ba haka ba ni zaka jawa masifa kasan banason duk abinda zai bata ran yaya ta karasa fadi tana kanne ma sanah ido,dan tasan sadeeq ya shiga tarkonta....

●● ZULAIHAT ●● 13  BY COMR.A/MALIK LAWAL M/FASHI.Zulaihat na zaune cikin mota a takure,anty laila na dan janta da hira j...
18/06/2025

●● ZULAIHAT ●● 13
BY COMR.A/MALIK LAWAL M/FASHI.
Zulaihat na zaune cikin mota a takure,anty laila na dan janta da hira jefi-jefi,sai dai tayi murmushi kadan,amma a tsorace take sosai saboda rashin sanin inda zasu,in ta tuno malam saleem yasan su sai hankalinta ya dan kwanta,Mummy ta kalli laila tace yamma tayi laila da kunje shopping kin siyo mata duk abun da bata dashi amma gobe da wuri sai ku fita ko,cikin girmamawa laila tace Allah ya kaimu mummy,Kallon unguwar zulaihat takeyi tsoronta ya kara zurfi saboda bude wani tankamemen gate da akayi tun daga waje taketa kalle-kalle,hankalinta a tashe sojoji s**a bude musu kofa suna sara musu, idon zulaihat ya ciko da kwalla anty laila tace fito muje mana,ta fito a hankali s**a jera suna tafiya har cikin gida,sanyin kamshi ne ya daki hancin zulaihat da aka bude kofar, anty laila ta kamota s**a bi bayan mummy s**a shiga da sallama,twins s**a rugo da gudu s**a dane jikin mummy,sai da s**ai bacci a gefen anty amarya,mummy ta saukesu tace nagaji dayawa ku bari in huta ko sweeries,s**a daga kansu s**a koma jikin anty laila suna bata labarai na shirme.
Anty amarya ta kalli mummy da ta zauna tana maida numfashi tace kun dade yaya,da har zan bi sahu ta fadi cikin zolaya,laila s**a karasa cikin falon zulaihat ta tsuguna ta gaida anty amarya,ta amsa tana murmushi tace wannan yar kyakyawar fa laila a ina kuka samota,mummy tayi murmushi ta kalli laila tace kuje ciki laila,ki kaita ďaki daya a bangarena kisata tayi wanka,anty laila tace mummy wai da mu tafi side dina in tayi wanka sai taci abinci anjima sai in kawota dakinki,mummy tace to ba laifi duk yadda kikayi Allah yayi maki albarka,tace ameen taja zulaihat s**a wuce bangarenta tare da twins.
Mummy ta kalli anty amarya tace yarinya na samo a gurin sauka,yarinya marainiya kuma mai hankali,gata abin tausayi,ta kwashe duk labarin zulaihat wanda taji ta fada mata,anty amarya ta dinga gyada kai cikin tausayi tace Allah sarki har naji tausayinta,mummy tace kedai bari yarinyar ta shiga raina lokaci guda shiyasa na nema wa abba aurenta saboda nutsuwarta kuma an bashi har an daura auren,anty amarya dake zaune ba hatta jalila da sanah da s**a dawo daga lambu lokacin sai da s**a girgiza.
Jalila ta kalli sanah da idonta yayi ja sannan ta zagayo ta gaban mummy,tace mummy wane abban? mummy ta harareta tace ina da wani abba da ya wuce sadeeq ne.
sanah ta ruga daki da gudu zuciyarta na tsananin bugawa gaba daya ta nemi kuka ta rasa.Anty amarya tayi kokari matuka ganin ta boye bacin ranta amma ta kasa,saboda sau biyu kenan mummy tanayi mata haka,tun akan nurain da taso kanwarta Aneesah ta aura har sun gama magana da daddy,kawai washe gari mummy taje ta auro mishi yar aminiyarta,anty amarya ta kalli mummy ta kirkiro yake tace Allah ya sanya alkhairi.
Mummy tayi murmushi tace ameen.A fili amma a zuciyarta tace sai dai ranki yayita baci,ta mike tace bari in dan watsa ruwa bata jira jin amsar ta ba ta wuce hanyar sama tana kwala ma jalila da tabi sanah daki kira,jalila ta fito da gudu tabi mummy samah.
Anty amarya na zaune a dakinta tana rarrashin sanah dake kuka k**ar ranta zai fita,dan mummy ta rikirkita mata plans dinta,
wayarta dake gefe tanata faman kuka tasan sadeeq ne amma ko kallon wayar batayi ba, kiran ya ishi anty amarya ta dauki wayar.
'"Hello!" tace babu dariya a fuskarta,daga daya bangaren jikin sadeeq har rawa yakeyi ya dauka sanah ce ta dauka,yace sweet baby menayi haka kika zabi ki yi min irin wannan ukubar,kinsan in banji mur--- anty amarya ta katse shi da cewa ba ita bace abba nice,yayi murmushin jin kunya yace anty ina wuni, lafiya kadai tace mishi,yace anty sanah bata da lafiya ne,cikin kissa anty amarya tace lafiyarta kalau,ka saurareni da kyau abba, daga yau karka kara kiran layin sanah,kayi biyayya ga zabin mahaifiyarka,ka bar sanah itama Allah ya hada ta da mai sonta,cikin kidimewa yace anty ban gane abinda k**e nufi ba,ta rage muryarta ta fara ďan kukan munafurci tace abba bansan me yasa yaya bata kaunata ba,duk irin biyayyar da nake mata bata gani.A kullum burina in hada zuria daku amma yaya sam bata kaunar hakan,anyi na aneesah ya wuce ban damu ba,saboda shi dama nurain bai ce yana sonta ba,amma yanzu kowa yasan irin soyayyar da kukeyi da sanah har muna fatan kuyi aure shine yaya tayi ma sanah wulakanci sosai akanka har karshe taje ta auro maka wata yarinya yar talakawa wanda basu gaji arziki ba,irin yaran da burinsu su aureka ka mutu suci dukiya,ta kara fashewa da kuka tace Allah ya sani inason jinin yaya Aisha da jini na,saboda ban haihu a cikinku ba shiyasa nakeson wani ya auri jinina in ya haihu ko na mutu baza'a manta dani ba,sadeeq ya kara rudewa yace anty dan Allah kiyi shuru waye ya fada miki wannan maganar,ya za'ayi ayi min aure ba tare da sanina ba,
anty amarya tace wallahi da gaske ne abba, amma kayi hakuri kayi ma mahai--- karki ce inyi mata biyayya anty ya fadi cikin daga murya k**ar zautacce,yace wallahi bazanyi biyayya akan abinda zai cutar dani ba.
yanzun nan zan kira mummy ta warware aur

Address

No22. Galadima Dudi Road Kofar Kudu Unguwar Liman Malumfashi
Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Comr.Abdulmalik lawal beguwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share