
27/07/2025
◆◆ ZULAIHAT◆◆ 20
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI
Zaune suke kewaye da mummy a Falor bayan isha'i,faruk na zaune yana latsa waya,jalila da zulaihat suna duba wani littafin adduo'i suna musu akanshi,Anty amarya ta fito cikin daguwar riga mai kyau da tsari,ta gabansu tazo ta wuce duk s**a gaisheta daya bayan daya,ta amsa tana yatsina mummy ko kallon inda take batayi ba,fridge din falor ta bude ta dakko juice ta koma daki,tana jin hon ďin motar daddy tayi maza ta mike ta kara gyara jikinta ta feshe jikinta da ni'imtaccen turare,sai da taji ya shigo sannan ta fito tana tafiyar hawainiya,ta karaso cikin falon ta dan durkusa tace sannu yaya,mummy da mamaki ya isheta ko kallon inda take batayi ba,daddy ya lura tsaf da mummy sannan yabi dukka yaran da kallo dan baiji sun gaisheta ba,haba nan da nan ranshi ya baci sosai ya kalli mummy da ta haďe girar sama da ta kasa yace Aisha bakiji ana gaisheki bane,mummy tace banji ba ta cigaba da kallon tv,daddy ya kalli faruk yace kai dan ubanka baka iya gaisuwa bane,cikin rashin fahimta yace dad-- bai bari ya karasa ba ya shiga surfa musu ruwan bala'i anty amarya na gefenshi tana kukan munafurci tana bashi hakuri,
ya kalli zulaihat da kanta ke sukunye yace harda ke zuwan jiya har an koya miki rashin kunya an nuna miki karki daraja matata to wallahi babu wanda ya isa ya taka min mata ina kallo haka ya dinga masifa mummy bata kalli inda yake ba bare tasan abinda yake fadi,
zagin da taji anty amarya tayi ma zulaihat ne yasata mikewa a fusace,kuma dama tayi hakan ne dan ta harzuka mummy,Cikin fushi mummy ta janyo zulaihat dake rakube a kusa da jalila duk kuka sukeyi,tace Hadiza kikace mata yar matsiyata?
kinsan waye matsiyaci?to ki bude kunnenki dakyau kijini,
matsiyaci shine wanda duk abinda ake bashi baya isar shi sai ya hada dana haram,matsayaci shine wanda yake siyar da mutuncinshi dan ya samu kudi a kirashi da mai arziki,matsiyaci shine mai arzikin dake nuna halin tsiya k**ar yadda k**eyi.
kuma yanada daga cikin siffofin matsiyaci mutum ya zama munafuki algungumi k**ar yadda k**e,sai kiyi alkalanci tsakanin ke da ita waye matsiyaci?
kinga wannan yarinyar,ta fi min ke da duk wani wanda ya rabeki,haushi k**eji saboda na aurawa abba ita ko,to bari kiji ko bayan raina jinina bazai taba haduwa da jinin fasikai irin---- wawan marin da daddy ya dauketa dashi ne ya hanata karasa maganar da takeyi,faruk ya mike da sauri jikinshi na rawa ya fita daga gidan gaba daya idonshi jawur,daddy yace a gabana k**e fifita wata banza akan matata,a gabana k**e kiran matata fasika,lallai Aisha kin cika marar mutunci me manta alkhairi, duk irin biyayyar da hadiza take miki baki gani,yanzu dama akan wannan yarinyar gidana yake neman k**awa da wuta, wallahi badan nasan darajar aure ba da a yau sai yarinyar nan ta bar min gidana,amma kisa a ranki,duk ranar da abba ya dawo yace baya son yarinyar nan,wallahi tallahi zan goya mishi baya dari bisa dari ya auri wacce yakeso.
Dan kinga na kyaleki kina yadda k**eso da ya'yana to komai yazo karshe,ya cigaba da masifarshi mummy dake tsaye rike da kunci hawaye na zuba akansu ta juya ta barshi a gurin yanata masifa,daki s**a wuce ita da jalila da zulaihat dukkansu kuka sukeyi.
Daddy ya zauna bayan yayi masifar mai isarshi muryarshi har ta fara dishewa saboda bai iya masifar ba,ya shiga rarrashin anty amarya dake kuka sosai,yace ya isa hadiza,cikin kuka ta tureshi tace me yasa zaka mareta?
wallahi zafin marin a jikina najishi,wata rana zata gane kuskurenta tasan ni mai kaunarta ce,amma yanxu ka kara goga min bakin jini,yaya ta kasa gane irin son da nake mata,amma da sannu zata gane.""ta kara rushewa da kuka.''yiii-yii....wayyo..wayyo......
ya dinga rarrashinta yanajin tausayinta a zuciyarshi dan yasan tana kaunarsu dukkansu har cikin ranta,to me ya canza Aisha ta tsaneta lokaci daya,me ya canzata take neman rushe farin cikin gidanshi magana yakeyi a zuci baisan ta fito ba.Anty amarya tayi saurin mikewa tace Zulaihat.Shigowar Zulaihat gidan nan yana neman rusa da farin cikin daya ginu lokaci mai tsawo.Irin yaran nan burinsu su auri mutum ya mutu suci gado amma yaya ta kasa ganewa,ni tausayi ma take bani saboda makashinta yana jikinta,daddy ya gyada kanshi ya daura duk akalar tunaninshi akan Zulaihat baiwar Allah.
(kissa tafi magani sunan wani littafi).