26/06/2025
ZULAIHAT ●15
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.
Washe gari tun kafin asuba zulaihat ta farka saboda ta riga ta saba lokacin nayi bacci zai kauracewa idonta,ta dinga bin dakin da aka kaita ta kwana da kallo kaya barkatai dan tun da aka shigo da ita take kare ma dakin kallo barin toilet din da yaji kayan gyara.
Tashi tayi a hankali ta shiga bayin tayi tsarki ta kunna ruwa k**ar yadda jalila ta nuna mata tayi alwala,tsayawa tayi gaban mudubin bayin tana kare ma kanta kallo,sai da ta dan dade sannan ta fito ta shimfida dadduma tayi nafila kafin a kira sallar asuba,karantun kur'ani ta dinga yi da"ka",batare da ta duba kur'ani ba.Har aka kira sallah tana karatu tana idarwa ta mike tayi sallah,ta zauna tana addu'oi tana tuno rayuwarta ta baya,ko yanzu me goggo takeyi tasan tana can tana aikin waina,haka ta dinga tunanin su goggo da salaha da babanta,ta share kwallar da ta digo mata a idonta ta karasa adduointa ta nade daddumar ta maida ita mazauninta,Kofar dakin taji an bude ta waigo s**a hada ido da mummy,ta karaso ciki itama da hijab da carbi a hannunta tana murmushi,
zulaihat ta durkusa da sauri tace ina kwana, mummy ta d**ota tace lafiya lau zulaihat ya kwanan bakon guri,zulaihat ta sunne kanta tace lafiya lau,mummy tace to alhamdulillahi ki saki jikinki kema yar gida ce,banason wannan dari-darin da k**eyi,da ke da laila da jalila duk daya kuke a gurina,saboda haka ki daukeni matsayin uwa kinji,Zulaihat tace to in sha Allah,mummy tace yauwa diyata,bari inje daki kema ki kwanta ki huta kafin a kawo miki abin kari,zulaihat tace to.
Amma babu wani aikin da zanyi,mummy tace a'a je ki kwanta ki huta kinji,zulaihat ta gyada kanta ta koma ta zauna bakin gado.Gurin karfe 9am jalila ta turo kofar dakin, lokacin zulaihat na tsaye tana goge jiki,ta juyo da sauri zata tsuguna jalila ta hxade rai tace tashi-tashi wai so k**eyi kija min bala'i ne,na fada miki karki kara tsuguna min bakiji ba ko,ki rufamin asiri mu dinga gaisawa daga tsaye,,kuma ki saki jikinki kinji?
Zulaihat tace to,jalila tace yauwa,yanzu ki shirya ki fito mu karya ta ajiye mata doguwar riga a kan gado ta fita,zulaihat ta duba rigar taga katuwa ce irin ta jiya,har kasa take kai mata,ta koma gaban madubi,mai kadai ta shafa ta dauki rigar ta saka ta rufe kanta da gyalen ta sakko falon,a bangaren dining taga mummy da jalila suna zaune suna hira, karasawa tayi ta tsuguna ta kara gaida mummy,mummy tayi murmushi tace ai mun gaisa zulaihat tashi ki zauna anan,ta nuna mata kujerar kusa da ita,zulaihat ta zauna cikin jin kunya tana ta sinne kai,jalila tayi serven dinsu mummy da kanta ta hada ma zulaihat tea...
mai kauri ta tura gabanta tace maza ki shanye duka,zulaihat tace to,da kyar kunya ta barta ta fara cin dankali da sauce din hanta,a tare s**a gama karyawa dukkansu,mummy ta koma cikin falon ta zauna,zulaihat ta taya jalila kai kaya tsaftataccen kitchen din da k**ar ba anan ake girki ba.Fatsin ce tsaye a ciki tana wanke-wanke,zulaihat ta karasa kusa da fatsin tace kawo in tayaki,fatsin ta wage baki tace a'a jeki abinki ai na kusa gamawa,zata kara magana jalila taja hannunta tace zo mu tafi ciki mummy zatayi fada in taga kina aiki,Falor s**a wuce zulaihat ta rabe gefen kujera,mummy tayi murmushi a ranta tace da sannu zaki saki jiki.Sai da s**a dan dade sannan mummy tace zulaihat ajinki nawa a school,zulaihat tace jss(3) nake zan shiga ss.Mummy tace wace makaranta kikayi? ta kara sunkuyar da kanta tace nayi I.G.E.A unguwar rimi dana gama malam salim ya samo min capital school,mummy tace good,kina sha'awar cigaba daga ss1 din?jalila tayi dariya tace haba mummy me zai hana tayi sha'awa,ai kawai gara in anyi resuming ta dinga zuwa ko,mummy zatayi magana shewar da taji ta katseta,daga kanta tayi taga sanah janye da trolley anty amarya rike da jaka,har s**a karaso cikin falon basu kalli inda su mummy suke ba sai hirarsu sukeyi suna dariya,sai da s**a zo daf dasu anty amarya tayi murmushin rainin wayau tace yaya ina kwana, mummy da mamaki ya cika ta tace lafiya lau,sanah ta kara gyara dankwalinta tana kallon zulaihat tana kas-kas da cingam,ina kwana zulaihat ta fadi hade da kara tankwashe kafa,s**a mata kallon uku saura kwata,sannan sanah ta kwashe da dariya harda rike ciki,anty amarya ta dake cikin kissa tace banason iskanci wuce mota gani nan,ran mummy ya baci sosai da abinda sanah tayi mata dan ko gaishe ta batayi ba,anty amarya tace yaya bari in kai sanah gidan aneesah,mummy tace to a dawo lafiya,bata jira jin abinda zata ce ba ta kalli jalila tace tashi kuje gurin laila in ta gama kuzo ku tafi shopping din,jalila tace to mummy s**a mike suke wuce side din laila, mummy ta mike tayi hanyar sama ta bar anty amarya tsaye tana hararar bayanta,sai da ta gaji dan kanta tayi kwafa ta wuce waje tana sakar zuci...