Comr.Abdulmalik lawal beguwa

Comr.Abdulmalik lawal beguwa My name is Abdulmalik lawal Mahmud,I was born in the of 1990,at malumfashi local government katsina state of Nigeria.

30/11/2025

Allahu Akbar Wal-Hamdu lillah wa Subhanallah, ko kuma Subhanallah Wal hamdu lillah wa La'ilaha illal Lahu Wallahu Akbar (awata ruwayar).

★ Imam Tirmizy ne ya ruwaito wannan hadisin, acikin Jami'ut Tirmizy juzu'i na 2 shafi na 509.
Awajen Imamut Tirmizy yake cewa "An ruwaito hadisai da dama game da SALATUT TASBEEHI amma yawancin hadisan basu inganta ba. (Akwai rauni awajen masu ruwayar).

★ IMAM ABU-DAWUD shima ya ruwaito hadisin ta wata hanyar daban (wacce ba irinta Tirmizy ba. kuma Malamai sun HASSANA hadisin.Aduba cikin SUNANU nasa, juzu'i na 2 shafi na 96, hadisi na 1,297.

★ IMAMUL HAKIM ya ruwaito irin wannan hadisin ta hanyar ABDULLAHI BN UMAR BN ALKHATTAB (ra). Kuma yace WANNAN HADISIN YA INGANTA. BABU WATA QURA-QURA ACIKIN ISNADINSA.Daga cikin Hujjojin da suke tabbatar da INGANCIN HADISIN, shine yawaitar Sahabbai da Tabi'ai wadanda suke yin wannan Sallar, kuma suke koyar da ita ga Almajiransu.ABDULLAHI IBNUL MUBARAK (RA) ya kasance yana yin wannan sallar kuma yana koyar da ita ga Almajiransa.
Kuma dukkan wadanda s**a Ruwaito wannan Sallar daga Ibnul Mubarak, Mutane ne Ingantattu. kuma kowa yasan cewar Ibnul Mubarak ba zai koyar da duk abinda bai Inganta ba.
(Aduba cikin MUSTADRAKUL HAKIM ALA SAHIHAYNI juzu'i na daya, shafi na 464).
★ IMAM IBNU MAAJAH (rah) shima ya ware BABI GUDA ACIKIN LITTAFIN HADISINSA. wanda acikinsa yayi magana akan Salatut Tasbeehi tare da kawowa hadisai ingantattun daban daban.(Aduba cikin Sunanu Ibni Maajah juzu'i na 1 shafi na 442, hadisi mai lamba 1,430)
★ IMAM ALBAIHAQEE (rah) shima bayan ya kakkawo hadisan da s**ayi magana akan SALATUT TASBEEHI yace : "Kasancewar Salihan bayin Allah irinsu Ibnul Mubarak suna yinta, kuma an ruwaito ta daga garesu, Shima hujjah ne akan cewa hadisin Marfu'i ne kuma ya inganta.
(aduba cikin SHU'ABUL IMAN juzu'i na 1 shafi na 427).IBNUL MUNDHIRY (RAH) shima ya ruwaito wannan hadisin sannan yace An ruwaito shi ta hanyoyi Sahihai masu yawa daga Sahabbai daban daban.Kuma Malaman Hadisi da dama sun hanyoyin.(aduba cikin ATTARGHEEB WAT TARHEEB juzu'i na 1 shafi na 267).
Albaniy yayi kokarin raunata wata daga cikin Isnadan hadisin, yace wai akwai wani Majhuli acikin isnadin. Amma Malamai da dama suna sun mayar masa da maganarsa.
★ IMAM SUYUTY ya kawo sunayen Manyan HUFFAZU (maluma MAHADDATAN hadisi) sama da guda 20 wadanda s**a inganta Hadisan SALATUT TASBEEHI. acikinsu akwai:
1. HAFIZ ABU SA'EED AS-SAM'ANY.
2. HAFIZ KHATEEB ALBAGHDADY.
3. HAFIZ IBNU MUNDAH.
4. HAFIZ IBNUS SALAH.
5. HAFIZ ABU MUSAL MADANY.
6. HAFIZ ZARKHASHY.
(Aduba cikin LA'ALI'UL MASNU'AH juzu'i na 2 shafi na 42 zuwa na 45).A takaice dai SALATUT TASBEEHI ibadah ce mai falala wacce ruwayarta ta inganta daga Manzon Allah ﷺ.
©Comr.Abdulmalik lawal malumfashi

30/11/2025

SALATUT TASBEEHI

Assalamu 'alaikum 'yan uwa Musulmi. Tun Kamar Watanni uku da s**a gabata wasu 'yan uwa sake ta aikowa da tambayoyinsu a game da Sallar nan mai falala wacce ake kira SALATUT TASBEEHI.

Wadansu suna yin tambaya ne game da ita kanta sallar. wato yadda ake yinta. wadansu Mutanen Kumar suna tambaya ne akan INGANCIN HADISIN DA YAZO DA BAYANINTA.To yanzu Insha Allahu zanyi bayani akan yadda ake yinta, sannan Kuma inyi magana akan hadisan da s**a zo da banyaninta.

"Watarana Manzon Allah ﷺ yace ma Baffansa Sayyiduna 'Abbas bn Abdil-Muttalib (rta):
'Ya Baffa!! Bari inyi maka zumunci! Bari inyi maka kyauta!! Bari in amfaneka"

Sai Abbas (radhiyal-Lahu anhu) yace "Kwarai kuwa Ya Ma'aikin Allah".Sai Manzon Allah ﷺ yaci gaba da ce masa:
"Baffa kayi sallah raka'a 4. acikin kowacce raka'a ka karanta Fatiha da surah.

Bayan ka karanta surah sai kayi TASBEEHI guda goma sha-biyar (15) kafin kayi ruku'u.
Idan kayi ruku'u zaka maimaita (Tasbeehin) sau goma (10). Idan ka d**o kanka (daga ruku'un) ma haka zakayi tasbeehin guda goma (10).

Sannan ka tafi Sujjadah. acikin Sujjadah zakayi tasbeehin guda goma (10). Idan ka d**o daga Sujjadar ma haka zakayi tasbeehin sau goma.
Sannan ka sake yin Sujjadar. ita ma acikinta kayi tasbeehin sau 10. idan ka d**o kanka daga wannan sujjadar (sujada ta 2) zaka sake yin tasbeehin guda 10 kafin ka mike tsaye.

Tasbeehi 75 kenan acikin kowacce raka'a, kuma 300 kenan acikin raka'a 4 gaba daya.
Ko zunubanka sun kai yawan adadin yashin da yake Aalij, to Allah za gafarta maka su."
Sai Sayyiduna Abbas (ra) yace "YA RASULALLAHI! waye zai iya aiwatar da irin wannan sallar akullum!"

Sai Manzon Allah (saww) yace "TO IDAN BA ZA IYA YI KULLUM BA, SAI KA RIKA YINTA DUK JUMA'A (wato duk mako guda kenan).
Idan ba zaka iya yi duk mako ba, to ka rikayi sau 'daya duk wata guda".
Bai gushe ba yana magana har sai da yace :"KAYI TA KODA SAU 1 NE ACIKIN SHEKARA GUDA".

wannan motar Yakama kasar Nigeria ta mallaka
06/11/2025

wannan motar Yakama kasar Nigeria ta mallaka

24/10/2025

The Kind Little Boy

Once upon a time, there was a little boy named Musa. He lived in a small village with his parents. Every morning, Musa walked to school through a path full of trees and flowers.

One day, he saw a little bird with a broken wing lying on the ground. Musa felt sorry for it. He gently picked up the bird and took it home. Every day after school, he fed the bird and cared for it until it could fly again.

When the bird was strong, Musa took it outside and said, “You can go home now.” The bird flew around him happily and sang a sweet song before flying away.

From that day, the bird always came to Musa’s window every morning to sing for him. Musa smiled and felt happy knowing kindness always comes back. 🌼

10/10/2025

WhatsApp Group Invite

10/10/2025

MATSALAR ZARGI A TSAKANIN MA’AURATA

Zargi wata cuta ce da take lalata soyayya da kwanciyar hankali a cikin aure. Idan mace ko namiji s**a fara zargin juna ba tare da hujja ba, to wannan yana iya zama matakin farko na rugujewar zaman lafiya.

Me ke janyo zargi?

Akwai dalilai da dama da ke haifar da zargi a cikin aure, ga wasu daga ciki:

1. Rashin amincewa da juna – Idan babu gaskiya a tsakaninku, duk wata magana ko tafiya sai ta zama abin shakku.

2. Tarihin rashin gaskiya – Idan ɗaya daga cikin ma’aurata ya taba cin amanar ɗaya, sai ya zama da wuya a sake samun kwanciyar hankali.

3. Saurin yanke hukunci – Wani lokaci mutum yakan yanke hukunci ba tare da jin bayanin gaskiya ba.

4. Sako ko kiran waya – Karamin abu kamar sakon waya, idan ba’a bayyana ba, yana iya zama tushen zargi.

5. Shawarwari daga abokai marasa tunani – Wasu abokai suna saka wuta a cikin aure ta hanyar kawo magana marar tushe.

Illolin zargi

Zargi yana da illa masu yawa:

Rashin natsuwa – Idan kullum kana tunanin abokin rayuwarka yana da wani sirri, to hankalinka ba zai taɓa kwanciya ba.

Rashin yarda – Zargi yana kashe amincewa, wanda shi ne ginshiƙin soyayya.

Ƙiyayya da rashin jin daɗi – Zargi na janyo tsanar juna da gajiya da zama tare.

Rushewar aure – Idan zargi ya kai matakin gardama da rashin mutuntawa, aure na iya karewa.

Yadda za a guji zargi

1. Kuyi magana cikin gaskiya – Ku riƙa faɗa wa juna komai cikin gaskiya.

2. Ku yarda da juna – Yarda ita ce ginin soyayya mai ɗorewa.

3. Kada ku boye sirri – Boye-boyen abubuwa na iya haifar da zargi.

4. Kada ku saurari magana daga waje – Koyi da yin bincike kafin yanke hukunci.

5. Ku kasance masu haƙuri – Haƙuri yana hana manyan matsaloli su zama faɗa.

Kammalawa

Zargi ba hujja ba ne, kuma ba ya kawo mafita. Idan akwai shakku, magana da fahimta ce mafita, ba zargi ba. Ku koya yin dogaro da juna, domin soyayya ba ta iya rayuwa cikin rashin amincewa.

ALHAMDULILLAHIAyau jama'an wannan unguwar KOFAR KUDU/Unguwar liman suna masu nuna farin cikin da yimaka addu'a sakamakon...
27/08/2025

ALHAMDULILLAHI
Ayau jama'an wannan unguwar KOFAR KUDU/Unguwar liman suna masu nuna farin cikin da yimaka addu'a sakamakon kokarin da kakeyi na shige da fice Dan ganin dacewa da samo ma wannan unguwa solar lights har guda (10).
Wannan kowa yasani cewa somun tabine kafin nan gaba kadan.Sauran unguwannin suma duk zasu samu nasu cikin ikon Allah.
Yayi Alkawari insha Allahu zuwa jimawa kadan sauran unguwannin da kuma lunguna da duk muke dasu acikin wadannan unguwannin za yayi kokarin samo masu nasu.
Da wannan damar mutanan wannan yanki suke yimaka godiya da kuma addu'a.
Ubangiji Allah ya jikan iyayenka da gafara,ya haskaka rayuwaka arzikin manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam.
Muna godiya.

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 20         BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHIZaune suke kewaye da mummy a Falor bayan isha'i,faruk na zaune ...
27/07/2025

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 20
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI
Zaune suke kewaye da mummy a Falor bayan isha'i,faruk na zaune yana latsa waya,jalila da zulaihat suna duba wani littafin adduo'i suna musu akanshi,Anty amarya ta fito cikin daguwar riga mai kyau da tsari,ta gabansu tazo ta wuce duk s**a gaisheta daya bayan daya,ta amsa tana yatsina mummy ko kallon inda take batayi ba,fridge din falor ta bude ta dakko juice ta koma daki,tana jin hon ďin motar daddy tayi maza ta mike ta kara gyara jikinta ta feshe jikinta da ni'imtaccen turare,sai da taji ya shigo sannan ta fito tana tafiyar hawainiya,ta karaso cikin falon ta dan durkusa tace sannu yaya,mummy da mamaki ya isheta ko kallon inda take batayi ba,daddy ya lura tsaf da mummy sannan yabi dukka yaran da kallo dan baiji sun gaisheta ba,haba nan da nan ranshi ya baci sosai ya kalli mummy da ta haďe girar sama da ta kasa yace Aisha bakiji ana gaisheki bane,mummy tace banji ba ta cigaba da kallon tv,daddy ya kalli faruk yace kai dan ubanka baka iya gaisuwa bane,cikin rashin fahimta yace dad-- bai bari ya karasa ba ya shiga surfa musu ruwan bala'i anty amarya na gefenshi tana kukan munafurci tana bashi hakuri,
ya kalli zulaihat da kanta ke sukunye yace harda ke zuwan jiya har an koya miki rashin kunya an nuna miki karki daraja matata to wallahi babu wanda ya isa ya taka min mata ina kallo haka ya dinga masifa mummy bata kalli inda yake ba bare tasan abinda yake fadi,
zagin da taji anty amarya tayi ma zulaihat ne yasata mikewa a fusace,kuma dama tayi hakan ne dan ta harzuka mummy,Cikin fushi mummy ta janyo zulaihat dake rakube a kusa da jalila duk kuka sukeyi,tace Hadiza kikace mata yar matsiyata?
kinsan waye matsiyaci?to ki bude kunnenki dakyau kijini,
matsiyaci shine wanda duk abinda ake bashi baya isar shi sai ya hada dana haram,matsayaci shine wanda yake siyar da mutuncinshi dan ya samu kudi a kirashi da mai arziki,matsiyaci shine mai arzikin dake nuna halin tsiya kamar yadda k**eyi.
kuma yanada daga cikin siffofin matsiyaci mutum ya zama munafuki algungumi kamar yadda k**e,sai kiyi alkalanci tsakanin ke da ita waye matsiyaci?
kinga wannan yarinyar,ta fi min ke da duk wani wanda ya rabeki,haushi k**eji saboda na aurawa abba ita ko,to bari kiji ko bayan raina jinina bazai taba haduwa da jinin fasikai irin---- wawan marin da daddy ya dauketa dashi ne ya hanata karasa maganar da takeyi,faruk ya mike da sauri jikinshi na rawa ya fita daga gidan gaba daya idonshi jawur,daddy yace a gabana k**e fifita wata banza akan matata,a gabana k**e kiran matata fasika,lallai Aisha kin cika marar mutunci me manta alkhairi, duk irin biyayyar da hadiza take miki baki gani,yanzu dama akan wannan yarinyar gidana yake neman kamawa da wuta, wallahi badan nasan darajar aure ba da a yau sai yarinyar nan ta bar min gidana,amma kisa a ranki,duk ranar da abba ya dawo yace baya son yarinyar nan,wallahi tallahi zan goya mishi baya dari bisa dari ya auri wacce yakeso.
Dan kinga na kyaleki kina yadda k**eso da ya'yana to komai yazo karshe,ya cigaba da masifarshi mummy dake tsaye rike da kunci hawaye na zuba akansu ta juya ta barshi a gurin yanata masifa,daki s**a wuce ita da jalila da zulaihat dukkansu kuka sukeyi.
Daddy ya zauna bayan yayi masifar mai isarshi muryarshi har ta fara dishewa saboda bai iya masifar ba,ya shiga rarrashin anty amarya dake kuka sosai,yace ya isa hadiza,cikin kuka ta tureshi tace me yasa zaka mareta?
wallahi zafin marin a jikina najishi,wata rana zata gane kuskurenta tasan ni mai kaunarta ce,amma yanxu ka kara goga min bakin jini,yaya ta kasa gane irin son da nake mata,amma da sannu zata gane.""ta kara rushewa da kuka.''yiii-yii....wayyo..wayyo......
ya dinga rarrashinta yanajin tausayinta a zuciyarshi dan yasan tana kaunarsu dukkansu har cikin ranta,to me ya canza Aisha ta tsaneta lokaci daya,me ya canzata take neman rushe farin cikin gidanshi magana yakeyi a zuci baisan ta fito ba.Anty amarya tayi saurin mikewa tace Zulaihat.Shigowar Zulaihat gidan nan yana neman rusa da farin cikin daya ginu lokaci mai tsawo.Irin yaran nan burinsu su auri mutum ya mutu suci gado amma yaya ta kasa ganewa,ni tausayi ma take bani saboda makashinta yana jikinta,daddy ya gyada kanshi ya daura duk akalar tunaninshi akan Zulaihat baiwar Allah.
(kissa tafi magani sunan wani littafi).

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 19       BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHIDakinshi ya wuce ya kwanta yana ta juyi, Astaghfirullah...Astagfi...
27/07/2025

◆◆ ZULAIHAT◆◆ 19
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI
Dakinshi ya wuce ya kwanta yana ta juyi, Astaghfirullah...
Astagfirullah......Astagfirullah......
Kalmar da ya dinga fadi kenan a bayyane,saboda farat daya zuciyarshi ta kamu da son macen da ta haramta a gareshi har abada,ya dinga godiya ga Allah da yasa ya sani da wuri,tabbas kallo ďaya yayi mata yaji wani abu game da ita,a kallon da yayi mata na biyu zuciyarshi ta fara kitsa mishi wani sabon al'amari mai wuyar faďuwa. Hannunshi ya daga sama yace Allah na gode maka daka sanar dani wacece ita a kallon da nayi mata na uku,Ya lumshe idonshi a hankali yana neman tsari daga sharrin shaidan dan yasan duk aikinshi ne wannan,cikin ikon Allah har bacci yayi gaba dashi....
Kuka sosai anty amarya keyi a gaban daddy,duk wanda ya ganta a wannan lokacin zai dauka daga can cikin zuciyarta take kukan,hankalin daddy ya tashi matuka,yace subhanallahi hadiza lafiya me ya faru,cikin muryar kuka tace babu komai,da sauri yace kamar yaya babu komai,fada min abinda ke faruwa mana,ta kara narke murya tace banason ace na fara kawo kara,duk abinda akeyi min a cikin gidan nan ina shanye wa na dauki yaya tamkar ita ta haifeni shiyasa kome zatayi min bana daukarshi da zafi,amma bazan jure gaba da ita ba.
Ina matukar shan wahala saboda rashin kulani da bata yi kwata-kwata bata amsa gaisuwata,haka ta hana su jalila gaisheni,yau kwanan faruk hudu a gidan nan ko sau daya bai je inda nake ba bare yayi tunanin gaisheni, dan Allah ka bata hakuri in nayi ma wani laifi ta karasa fadi tana sheshshekar kuka kamar da gaske,ran daddy ya baci sosai yace ita Aishan ce bata kulaki,anty amarya ta gyada kai tana share hawaye,yace me kikayi mata to,cikin sanyin murya tace babu abinda na mata,daddy ya mike a fusace zai fita tayi maza ta riko shi,tace kayi hakuri daddy bazan juri inga kana ma yaya fada ba dan Allah karka mata magana zata ce kararta na kawo gurinka kuma zai kara zame mana matsala, nidai inason ka lura da kanka idan kaga yadda muke tafiyar da alamuran mu sai kayi mata magana,amna yanzu in ka sameta ai komai baci zaiyi.
Daddy yayi ajiyar zuciya yace wallahi da kin barni naje na sameta,suma su faruk din sai naci mutuncinsu,anty amarya tace kayi hakuri yara ne,kuma ni duk abinda zasu min bazan taba rikeshi ba saboda son da nake musu ko da dan da na haifa banajin zan iya mishi irinshi,ta dangwabe a jikinshi tace ina matukar kaunar jininka fiye da yadda nakeson kaina ma,dadi daddy yaji har cikin ranshi ya rungumota sosai yana rarrashinta nan ta kasheshi da kissarta mai zafi wacce take ma mummy zagon kasa da ita...

◆◆ ZULAIHAT ◆◆ 18 BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.Laila ce ta fara ganinshi ta fadada fara'arta tace faruk yaushe ka da...
08/07/2025

◆◆ ZULAIHAT ◆◆ 18
BY COMR.A/MALIK LAWAL MALUMFASHI.
Laila ce ta fara ganinshi ta fadada fara'arta tace faruk yaushe ka dawo,yace yanzun nan anty ya rankwashi kan jalila dake shan fruit salad yace acici,ta ajiye cokalin din ta rungumeshi tace yaya faruk oyoyo,shine baka fada azo a dauke ka ba,ya harareta yace sai kace wani yaro,anty ina mummina,anty laila tace suna school nasan yanzu zaka gansu,sannu dan autan mijin yau kai zanyi yayi fadi duk abinda kakeso in kawo maka,yayi dariya yace I trust u anty ki kawo min kome kuka dafa,jalila cikin murna tace to Dan uwa,ta kwaso ragowar kayan da basu jera a dining ba ta jera,sannan ta zuba mishi abinci tana mishi hira dan taji dadin dawowarshi,yace to parrot barni in ci abinci,ta turo baki tace kai yaya dan ma kaga ina murna ka dawo shine kake min wulakanci ko,yace sorry sister surutunki ne yayi yawa,tace to shikenan da naso in baka labarai amma na fasa,yace yi hakuri kanwata zauna ki tayani cin abinci in mun gama sai ki bani ko,ta zauna ta zuba abinci s**a ci tare tana mishi hira..Zulaihat na daki tsoro ya hanata fitowa duk tunaninta shine wanda aka daura mata aure dashi,afrah ce ta shigo dakin ta tsaya gabanta tace anty zage min zip mummy tana sallah kuma anty jalila tace bazata zage min ba saboda naki bata ice cream din da daddyn aida ya siyo man.
zulaihat ta janyota ta zage mata zip tace me yasa kika hanata rowa babu kyau,afrah tace ba kowa yasha nashi muna bacci ba;ni bazan bata nawa ba,zulaihat tace to muje in miki wanka sai ki kira amrah ma in mata ko,afrah tace ai anty jalila ta mata saboda ita ta bata nata,zulaihat tayi dariya tace to muje in miki, s**a shiga bayin ta mata wanka s**a fito ta shafa mata mai,tace je ki dakko kayanki in sa miki,ta fita da gudu taje daki ta dakko kayanta da mummy ta fito musu dashi,tayima jalila dake ma amrah kwalliya gwalo ta ruga da gudu jalila tabi bayanta itama da gudu,ihuuu!!! afrah ta dinga yi saboda jalila ta kusa kamota,a tare zulaihat da faruk s**a fito a firgice sun dauka wani abun ne ya sameta,jikin zulaihat afrah ta fada tana maida numfashi tana dariya,jalila ta karaso ta daga hannu zata kai mata duka,faruk dake tsaye yana kallon zulaihat ya daka mata tsawa,yace baki da hankali ne,me ta miki,jalila tace wallahi yaya yarinyar nan ta raina ni,da ta miki me ya fadi yana kallonta,afrah tayi saurin guduwa bayanshi tace (yaya umar sunan da mummy ke kiranshi suma haka suke kiranshi ita da amrah)babu abinda na mata wai dan tace insammata ice cream naki shine taki min wanka kuma ta biyoni zata duke ni,jalila tace wallahi karya take min gwalo fa ta min ni sa'arta ce da zata min gwalo,faruk yace kusan sa'arta dince ke tunda bakinki ya iya kwadayin abun yara komai kika gani sai kinsha,ta turo baki kamar zatayi kuka tace wallahi yau Allah ne kadai zai kwaceki,afrah ta kara mata gwalo tana dariya,jalila tace yaya kana ganin abinda takemin ko wallahi yau sai naji ma yarinyar nan ciwo,ta wuce daki ranta a bace,zulaihat ta dauki kayan afrah tace zo muje in shiryaki,afrah ta rugo gurin zulaihat s**a wuce daki s**a bar faruk baki sake yana kallonta,wai wacece wannan, ya fadi a fili,yarinyar is so cute,ya daga kafadunshi ya juya daki yana siffanta yanayin zulaihat a zuciyarshi..
Da safe bayan ya dawo sallar asuba ya shiga dakin mummy,zaune ya samesu tare da zulaihat tana kara ma mummy karatu,gefensu ya zauna yana sauraron kira'arta yana bin karatun idonshi a lumshe,sai da s**a idar sannan ya bude idonshi ya kalli zulaihat da ke kwashe qur'anai,ta sunkuya tace ina kwana,yace lafiya lau malama,ta ajiye qur'anan gurin da suke ta fita,ya dawo kusa da mummy yace ina kwana mummy,tace lafiya lau umar ya gajiyar hanya,yace tabi lafiya mummy,nan s**a fara hirar school dinshi,har gurin karfe takwas suna hira,har ya tashi zai tafi ya dawo yace wai mummy a ina kika samo wannan kyakykyawar malamar,mummy tayi dariya tace malama ce amma tá gida,ya zauna yace ban gane ba,tace Amaryar Abba ce,gaban faruk ya fadi sosai yace wane abban,mummy tace na nan gidan yayanka,abinda yasa bamu fada muku ba saboda muna son muyi muku surprise,ko shi abban bai sani ba,faruk yayi ajiyar zuciya yace gaskiya yaya abba ya dace sosai,Allah ya basu zaman lafiya,mummy ta bude murya cikin farin ciki tace ameen umar,yayi murmushi ya tashi ya fita jikinshi a sanyaye..............

08/07/2025

Address

No22. Galadima Dudi Road Kofar Kudu Unguwar Liman Malumfashi
Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Comr.Abdulmalik lawal beguwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share