Hausa Forum

Hausa Forum HausaForum.com.ng Kanun Labarai, Kuyi Following Domin Samun Nagartattun Labarai a koda yaushe

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin TalauciBayan tsawon shekaru na aiki tukuru, kasar Sin...
04/06/2026

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Bayan tsawon shekaru na aiki tukuru, kasar Sin ta cimma nasarar kawar da matsanancin talauci tsakanin al’ummunta. Ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar ta kammala dukkanin ayyuka masu nasaba da wannan aiki, ciki har da karfafa nasarori, da fadada matakan yaki da talauci yadda ya k**ata, yayin da take kara ingiza farfado da yankunan karkara, da aiwatar da matakan dakile sake tsundumar al’ummun da s**a riga s**a tsira daga kangin fatara.

Alhazan Kebbi rukunin farko sun dawo gidaRukunin farko na Alhazan Jihar Kebbi na Hajjin shekarar 2026 sun sauka a Filin ...
04/06/2026

Alhazan Kebbi rukunin farko sun dawo gida

Rukunin farko na Alhazan Jihar Kebbi na Hajjin shekarar 2026 sun sauka a Filin Jirgin Sama na Kasa da Kasa na Sir Ahmadu Bello da ke Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

Rukunin farko na Alhazan Kebbi 426 sun dawo gida – HAUSA FORUM Rukunin farko na alhazan Jihar Kebbi su 426 da s**a sauke...
04/06/2026

Rukunin farko na Alhazan Kebbi 426 sun dawo gida – HAUSA FORUM

Rukunin farko na alhazan Jihar Kebbi su 426 da s**a sauke farali a Hajjin shekarar 2026 sun iso Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Sir Ahmadu Bello da ke Birnin Kebbi a ranar Alhamis.

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na ZamanantarwaShin kun taba ganin yadda hamada ta zama wuri mai cike da bish...
04/06/2026

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Shin kun taba ganin yadda hamada ta zama wuri mai cike da bishiyoyi, yankuna daban daban sun hada juna a maimako warewa, kana hanyoyi sun hada juna a maimakon masu laka? Wannan ba sihiri ba ne, canji ne na gaske da aka samu a tsawon shekaru fiye da 10 da s**a gabata yayin da kasar Sin take kokarin raya kanta.

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da MararabaAn rufe wasu makarantu a yankunan Nyanya da ke Abuja da...
04/06/2026

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

An rufe wasu makarantu a yankunan Nyanya da ke Abuja da kuma Mararaba da ke Jihar Nasarawa a ranar Alhamis, bayan samun rahoton barazanar tsaro da ya jawo fargaba tsakanin iyaye da hukumomin makarantu.

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na UkuYanzu haka ana gudanar da taron masana ilmin harkokin ka...
04/06/2026

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Yanzu haka ana gudanar da taron masana ilmin harkokin kasar Sin na duniya karo na uku, a birnin Dunghuang na lardin Gansu, da ke arewa maso yammacin kasar Sin, inda wakilai sama da 300, da s**a fito daga kasashe kusan 70, suke musaya a kan batutuwan da s**a hada da musayar wayewar kai tsakanin Sin da sauran kasashen duniya.

An k**a wanda ya yi wa mahaifinsa dukan mutuwa a OndoRundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta k**a wani mutum mai shekara 38...
04/06/2026

An k**a wanda ya yi wa mahaifinsa dukan mutuwa a Ondo

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta k**a wani mutum mai shekara 38, Nsikak Kingsley saboda zargin dukan mahaifinsa.

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa DaidaitoKakakin ma’aikatar...
04/06/2026

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Mao Ning ta bayyana cewa hadin gwiwar tattalin arziki da ciniki tsakanin Sin da Tarayyar Turai, ya samo asali ne daga burin cimma muradun bai daya, kuma jigonsa shi ne samar da fa’ida a fannin gogayyar kasuwa.

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester CityƘungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta kusa da kammala yarjejeniya...
04/06/2026

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta kusa da kammala yarjejeniyar ɗaukar matashin ɗan wasan Leicester City, Jeremy Monga.

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin BeijingOfishin yada labarai na majalisar g...
04/06/2026

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya gudanar da taron “tattaunawar magadan garuruwa na duniya na 2026” a birnin Beijing, daga ranar 2 zuwa 3 ga watan nan na Yuni. Magadan garuruwa da wakilan birane fiye da 30 daga kasashe 6 na Afirka, da s**a hada da Morocco, Seychelles, Tunisia, Senegal da sauransu, tare da wasu wakilan kungiyar hadin kan birane na yawon bude ido ta duniya (WTCF), sun halarci taron.

Address

Modern Market Maru
Maru
10001

Telephone

+2347033515371

Website

https://youtube.com/@hausaforumnew?si=7YduslH7gDv1QdoT, https://www.instagram.com/hausa_f

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Forum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share