04/06/2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Bayan tsawon shekaru na aiki tukuru, kasar Sin ta cimma nasarar kawar da matsanancin talauci tsakanin al’ummunta. Ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar ta kammala dukkanin ayyuka masu nasaba da wannan aiki, ciki har da karfafa nasarori, da fadada matakan yaki da talauci yadda ya k**ata, yayin da take kara ingiza farfado da yankunan karkara, da aiwatar da matakan dakile sake tsundumar al’ummun da s**a riga s**a tsira daga kangin fatara.