Hausa Forum

Hausa Forum HausaForum.com.ng Kanun Labarai, Kuyi Following Domin Samun Nagartattun Labarai a koda yaushe

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya nuna damuwa kan furucin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya ...
02/11/2025

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya nuna damuwa kan furucin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi kan zargin ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Nijeriya. A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, Kwankwaso ya ce ya lura da yadda Trump ke ta yin furuci masu tsauri kan Nijeriya, musamman bayan sanya ƙasar cikin jerin “...

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya nuna damuwa kan furucin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi kan zargin ana yi wa Kiristoci

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki matakin gag...
02/11/2025

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki matakin gaggawa kan shugaban Amurka, Donald Trump, bayan barazanar da ya yi na kawo hari Nijeriya. A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Lahadi, Sheikh Gumi ya bayyana barazanar Trump a matsayin wulaƙanci ga ikon Nijeriya, yana mai cewa bai dace wata ƙasa mai cikakken ‘yanci ta zama abin tsoratarwa da irin wannan furuci ba....

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki matakin gaggawa kan shugaban Amurka, Donald

Allah Ya yi wa fitaccen jarumin Kannywood, Mato Na Mato, wanda aka fi sani da Malam Nata’ala a cikin shirin Dadin Kowa r...
02/11/2025

Allah Ya yi wa fitaccen jarumin Kannywood, Mato Na Mato, wanda aka fi sani da Malam Nata’ala a cikin shirin Dadin Kowa rasuwa. Wannan na cikin wani saƙo da fitacciyar marubuciya, Fauziyya D. Sulaiman ta wallafa a shafinta na Facebook a daren ranar Lahadi.

Kamar wannan: Kamar Loading ... Mai dangantaka Source link

Jarumin ya rasu bayan fama da ciwon daji.

Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke J...
02/11/2025

Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke Jihar Yobe. Rundunar ’yan sanda ta Jihar, ta tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Asabar. A cewar sanarwar, Abba Hassan, wanda asalinsa ɗa Jihar Borno ne, ya gudu daga gidan yarin a ranar 31 ga watan Oktoba, bayan kotu ta yanke masa hukuncin kisa....

Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke Jihar Yobe.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon taya murnar bude babban gidan tarihi na kasar Masar ga shugaba Abdel-Fattah...
02/11/2025

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon taya murnar bude babban gidan tarihi na kasar Masar ga shugaba Abdel-Fattah al-Sisi. Cikin sakon nasa na jiya Asabar, shugaba Xi ya ce “Albarkacin bude babban gidan tarihin na Masar, ina fatan mika sahihin sakon taya murna ga shugaba Abdel-Fattah al-Sisi da al’ummun kasar. Na yi imanin cewa babban gidan tarihin na Masar zai bar wata muhimmiyar alama a tarihin al’adun Masar, tare da taka rawar gani wajen karewa, da kuma gadar da dadaddiyar wayewar kan kasar”....

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon taya murnar bude babban gidan tarihi na kasar Masar ga shugaba Abdel-Fattah al-Sisi. Cikin sakon nasa na jiya Asabar, shugaba Xi ya ce “Albarkacin bude babban gidan tarihin na Masar, ina fatan mika sahihin sakon taya murna ga shugaba Abdel-Fattah al-Sis...

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya ɗauki mataki mai tsauri a k...
02/11/2025

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya ɗauki mataki mai tsauri a kan Shugaban Amurka, Donald Trump, game da barazanar da ya yi na amfani da ƙarfin soja a kan Najeriya. Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Lahadi, malamin ya bayyana cewa irin wannan magana ta Trump cin mutunci ce ga ’yancin Najeriya....

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shawarci Shugaba Bola Tinubu da ya ɗauki mataki mai tsauri a kan Shugaban Amurka, Donald Trump, game da barazanar da ya yi na amfani da ƙarfin soja a kan Najeriya.

02/11/2025

Adadin mutanen da ake zartar wa hukuncin kisa na karuwa a duniya duk da cewa kasashe da yawa sun daina amfani da kisa a matsayin hukuncin manyan laifuka. A watan Janairun 2024 ne aka yanke wa wani dan Amurka hukuncin kisa ta hanyar amfani da iskar gas, karo na farko da aka yi amfani da irin wannan tsari. Sannan aka yanke wa wani dan Japan hukuncin kisa saboda wutar da ya cinna wadda ta yi ajalin mutum 36....

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kwarya-kwaryar taron shugabannin APEC karo na 32, da ziyarar da shugaba...
02/11/2025

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kwarya-kwaryar taron shugabannin APEC karo na 32, da ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar a kasar Koriya ta Kudu, sun bude babin yaukaka hadin gwiwar yankin Asiya da Fasifik, kuma hakan ya shaida nauyin dake wuyan Sin na babbar kasa a duniya. Wang Yi, ya yi tsokacin ne a Lahadin nan, yayin taron manema labarai dangane da ziyarar da shugaban na Sin ya gudanar a Koriya ta Kudu....

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kwarya-kwaryar taron shugabannin APEC karo na 32, da ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar a kasar Koriya ta Kudu, sun bude babin yaukaka hadin gwiwar yankin Asiya da Fasifik, kuma hakan ya shaida nauyin dake wuyan Sin na babbar kasa a d...

Assalamu alaikum masu karatu, barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin shirin na mu mai farin jini da albark...
02/11/2025

Assalamu alaikum masu karatu, barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin shirin na mu mai farin jini da albarka na Girki Adon Mata. A yau shafin na mu zai koya muku yadda ake hada Fab Biskit: Abubuwan bukata: Fulawa 2 Kofi, S**ari–½ Kofi, Buta ½ Kofi, Kwai Daya, Bakin Fauda karamin cokali, Madara ta gari ko ta ruwa babban cokali 2, Filaibo (Banilla ko sururuberi ½ ), Gishiri kadan…...

A yau shafin na mu zai koya muku yadda ake hada Fab Biskit:

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sake fuskantar wani mummunan sakamako bayan ta sha kashi a hannun Enyimba Unite...
02/11/2025

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sake fuskantar wani mummunan sakamako bayan ta sha kashi a hannun Enyimba United a wasan mako na 11 na gasar NPFL, wanda aka buga a filin wasa na Enyimba International Stadium da ke birnin Aba, jihar Abia. Ɗan wasan Enyimba, Bassey John, ne ya fara zura ƙwallo a ragar Pillars a minti na 27, kafin Edidiong ya ƙara ta biyu mintuna kaɗan kafin a tafi hutun rabin lokaci....

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sake fuskantar wani mummunan sakamako bayan ta sha kashi a hannun Enyimba United a wasan mako na 11 na gasar NPFL,

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Wolverhampton Wanderers ta kori kocinta Vitor Pereira a yau Lahadi, 2 ga watan Nuwamba, bayan d...
02/11/2025

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Wolverhampton Wanderers ta kori kocinta Vitor Pereira a yau Lahadi, 2 ga watan Nuwamba, bayan da ƙungiyar ta kasa samun nasara a wasanni goma na farko a gasar Firimiya ta bana. Pereira ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru uku a watan Satumba, bayan ya taimaka wajen tabbatar da cewa Wolves ba ta faɗa zuwa gasar Championship a kakar da ta gabata ba…...

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Wolverhampton Wanderers ta kori kocinta Vitor Pereira a yau Lahadi, 2 ga watan Nuwamba, bayan da ƙungiyar ta kasa samun nasara a

Rahotanni daga sassa daban-daban na kasa sun nuna cewa yawancin mataimakan gwamnoni a wannan zamanin siyasa ba sa cikin ...
02/11/2025

Rahotanni daga sassa daban-daban na kasa sun nuna cewa yawancin mataimakan gwamnoni a wannan zamanin siyasa ba sa cikin jerin wadanda ake ganin za su gaji gwamnoni, bisa yanayin siyasar jihohi. Wakilanmu a fadin kasa sun tattara bayanai cewa yayin da gwamnoni masu wa’adin biyu ke shirin mika mulki ga magada, babu wanda ke nuna alamar goyon bayan mataimakinsa ya gaje shi....

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, zai kammala wa’adinsa na biyu a shekarar 2027, amma babu wata alamar cewa mataimakinsa, Mista Kayode Alabi, zai

Address

Maru, Nasarawa, Nasarawa

10001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Forum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share