Kainuwa Dashen Allah TV

Kainuwa Dashen Allah TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Kainuwa Dashen Allah TV, Minna.
(1)

25/09/2025

MU YAWAITA SALATI A GARESHI (S.A.W) ❤️

"Wannan shine daren juma'a, dare ne da ake son yawaita yin salati ga Manzon Allah sallallahu alaihi wasallama a daren sa da kuma ranar Juma'a"

"Kada mu yi ƙasa a guiwa wajen yawaita yi masa salati a bisa cancantarsa da hakan, domin lallai duk wanda ya yi salati ɗaya a gareshi, shima Allah zai yi masa guda goma madadinsa"

"Kuma lallai ka sani! Tabbas babu wani Musulmin da zai yawaita salati ga Annabi Muhammad sallallahu alaihi wasallama, face sai Allah Ya haskaka zuciyarsa, kuma ya gafarta masa zunubansa, kuma ya yalwata ƙirjinsa, sannan kuma ya sauƙaƙa masa dukkanin lamuransa, to ku yawaita salati a gareshi, tsammaninku Allah Ya sanya ku daga cikin tafarkin daidai, kuma Ya gafarta muku zunubanku"

اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ٠

اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ٠

25/09/2025

Huzaifah Ibn Asid al-Ghifari (رضي الله عنه) said:

“The Prophet ﷺ came to us while we were talking, and he asked: ‘What are you talking about?’ They said: ‘We are discussing the Hour.’ He ﷺ said: ‘The Hour will not come until you see ten signs before it.’ Then he mentioned: the smoke, the Dajjal (Antichrist), the Beast, the rising of the sun from the west, the descent of Isa ibn Maryam (Jesus son of Mary, peace be upon him), Gog and Magog (Yajuj & Majuj), three sinkings of the earth — one in the east, one in the west, and one in the Arabian Peninsula — and the last of them is a fire which will emerge from Yemen and drive the people to their place of gathering.”

— Sahih Muslim, Book of Fitan, 2901

24/09/2025

HASSADA BABBAR CUTA CE !!!

Hassada ba wai kawai rashin jin daɗin ganin wani da ni’ima ba ce, a’a cuta ce ta zuciya wacce ke ƙona rayuwar mai ita kafin ta taɓa wanda ake yi wa.

Abinda ya sa Hassada ta zama babbar cuta kuwa tana cinye ayyukan alheri kamar yadda wuta ke cinye itace, hakanan tana sanya zuciya ta cika da baƙin-ciki da ƙiyayya da damuwa. Kuma tana nuna rashin gamsuwa da rabon da Allah ya raba ya bawa bayinsa, sau da yawa tana kai mutum ga laifi kamar giba (gulma) da ƙarya, ko ma cutarwa.

Hassada ba ta rage wa wanda ake yi wa hassadar akan wani ni’ima da Allah ya azurta shi da shi, amma tana lalata mai ita. Don haka, mu nemi tsarkin zuciya da albarkar soyayya da fatan alheri ga juna.

24/09/2025

Ga Cikakken bayanin da ake Ta cece kuce Akai na Sheikh Lawan Abubakar Shu'aib Triumph Hafizahullah

23/09/2025

The Cure For The Heart♥️

‎The following five things cure the heart:

‎1. The company of the pious.
‎2. Recitation of the Qur'ān.
‎3. Keeping the stomach empty (fasting frequently).
‎4. Standing in Salah during the night (Qiyamullail).
‎5. Weeping in front of Allah before dawn.

{التحضيري ليوم القيامة ٣٨}

22/09/2025

BA MAKAWA KOWA ZAI MUTU

Allah Madaukaki Ya Ce:

"أَيْنَمَا تَكُونُوا يُدْرِككُّمُ الْمَوْتُ"
سورة النساء: 78

"Duk a inda kuka kasance, mutuwa za ta riske ku..."

Ibnu Katheer (Rahimahullah) ya ce:

Duk inda kuka kasance mutuwa za ta zo ta riskeku, saboda haka ku kasance a kan da'a ma Allah kuma kamar yanda Allah ya umarceku, domin shine alkhairi a gareku, saboda ita dai mutuwa dole ce kuma babu halin guduwa mata, sa'annan zuwa ga Allah ne makoma take, duk wanda ya kasance mai biyayya ne gareshi sai Ya saka masa da mafificin sakamako, Ya bashi mafi cikan lada.

21/09/2025

AYATUL KURSIY

Shaykh Abdul-Azeez Bin Baaz (رحمه الله) ya ce: "Karanta Ayatul Kursiy a yayin kwanciya barci yana daga cikin sabubban samun tsira daga Sihiri da Shaiɗan".

نور على الدرب ٢٩٦/٣

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلْحَىُّ ٱلْقَيُّومُ ۚ لَا تَأْخُذُهُۥ سِنَةٌ وَلَا نَوْمٌ ۚ لَّهُۥ مَا فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِى ٱلْأَرْضِ ۗ مَن ذَا ٱلَّذِى يَشْفَعُ عِندَهُۥٓ إِلَّا بِإِذْنِهِۦ ۚ يَعْلَمُ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُمْ ۖ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَىْءٍۢ مِّنْ عِلْمِهِۦٓ إِلَّا بِمَا شَآءَ ۚ وَسِعَ كُرْسِيُّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ ۖ وَلَا يَـُٔودُهُۥ حِفْظُهُمَا ۚ وَهُوَ ٱلْعَلِىُّ ٱلْعَظِيمُ

21/09/2025

✓Menene Adalci Na Qarin Aure Da Ake Nufi??

20/09/2025

Don’t pay attention to those who downplay the power of duʿāʾ for Gaza 🇵🇸— it is something immense. At the same time, don’t be misled by those who think making duʿāʾ means we can neglect all other responsibilities.
Gaza is going through unbearable pain. Gaza needs our duʿāʾ, our wealth, and every support we can give.

The steadfastness of the Muslims in Gaza is the main barrier against the schemes and plots of the Zionists across the entire region. They defend Gaza, al-Masjid al-Aqsa, Sham (Syria), and the whole area.
If their ranks were to break, you would witness how quickly the Zionists would carry out the rest of their plans in the region.
Truly, their steadfastness to this day is a sign of Allah’s support for His servants, and they stand as a proof against the Ummah. Perhaps Allah will grant them the reward of reviving the entire Ummah through their resilience and perseverance.

20/09/2025

ZIKIRIN SAFIYA DA MARAICE

"Kada ka rafkana daga zikirori a rayuwarka, musamman ma irin zikirorin safiya da maraice, da makamantansu, domin haƙiƙa shaiɗan yakan yi galaba kan duk wanda yake gafala daga yin addu'o’i a rayuwarsa"

"Yo sau nawa wata musiba take shirin afkuwa gareka amma a dalilin addu'o’in da ka kasance kana yi yau da kullum sai Allah Ta'ala ya karkatar da wannan musibar izuwa wani gurin, sau nawa wani bala'in yake tunkaroka amma dalilin zikirorin da ka kasance kana yi sai Allah ya taƙaita wannan bala'i ya sauka a kan kayanka a maimakon ya sauka a karan-kanka"

"Haƙiƙa akwai falala a cikin yin zikirori a rayuwa, domin haƙiƙa shi zikiri kariya ne kuma garkuwa ne ga bawa, sannan kuma haƙiƙa Allah yana bawa bawansa lada idan ya kasance yana kiyaye yin zikiri musamman irin zikirin da ya tabbata a sunnah"

❝Duk wanda ya ce “Subhanallahi Wa Bi Hamdihi” سبحان الله وبحمده sau ɗari a rana (100x), za a kankare masa zunubansa koda kuwa sun kai misalin yawan kumfar teku❞

20/09/2025

•SAI AN TANTANCE TARIHI
•Akwai Memory Card 32gb Cike Da Karatuttukan Mallam Albani Zaria (R.H)Na Siyarwa N5k, Duk Mai Buqata Ya Rubuta Albani Memory Card Ta Whatsapp Ta Wannan Lambar +2347068656605.

18/09/2025

Kadan Daga Cikin Arziqin Duniya

1.Hankali
2.'Yanci
3.Lafiya
4.Rai
5.Lafiyar Gabbai
6.Zaman Lafiya

👉🏾Kainuwa TV

Address

Minna

Telephone

07068656605

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kainuwa Dashen Allah TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share