30/05/2026
Rahotanni sun bayyana cewa wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun yi garkuwa da tsohon Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Sojin Najeriya, Rabe Abubakar, tare da matarsa a yankin Matazu da ke Jihar Katsina.
An ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar yayin da tsohon jami'in sojan da matarsa ke kan hanyarsu ta zuwa birnin Katsina, inda maharan s**a tare motarsu s**a yi awon gaba da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa direban motar ya samu raunin harbin bindiga lokacin harin, amma ya yi nasarar tserewa daga hannun maharan.
Haka kuma an gano motar tsohon jami'in sojan, wata jan motar Peugeot 504, wadda aka kai ofishin rundunar 'yan sanda na Matazu.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina da kuma hedkwatar rundunar sojojin Najeriya ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da sace tsohon janar ɗin da matarsa ba.
Sai dai rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro sun fara bincike da ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.
Lamarin ya sake jawo damuwa kan matsalar tsaro da hare-haren ’yan bindiga da ke ci gaba da addabar wasu yankuna na Arewa maso Yammacin Najeriya, musamman a Jihar Katsina.