PAKKA FM Radio

PAKKA FM Radio Latest News and Updates

Wani mutumin kasar Ghana mai suna Wilson Gbli Nartey daga Ningo ya more rayuwarsa tsaf inda ya mutu yana da shekaru 103 ...
05/10/2022

Wani mutumin kasar Ghana mai suna Wilson Gbli Nartey daga Ningo ya more rayuwarsa tsaf inda ya mutu yana da shekaru 103 a duniya.

A cewar rahotanni, mutumin ya auri mata 20 da yara fiye da 110 kuma yana daukar dawainiyarsu su dukka.

An yi jana'aizar wani mutumin kasar Ghana mai suna Wilson Gbli Nartey, wanda ya auri mata 20 tare da haihuwar yara fiye da 100 shekaru uku bayan mutuwarsa.

Uwargidar shugaban kasa ta bayyana yadda tayi jinyar mijinta shugaba Buhari tun tana yar shekara 19 Aisha Buhari ta cacc...
05/10/2022

Uwargidar shugaban kasa ta bayyana yadda tayi jinyar mijinta shugaba Buhari tun tana yar shekara 19

Aisha Buhari ta caccaki yan siyasan da ke nuna fushinsu kawai don sun fadi zaben fidda gwani

Uwargidar shugaban kasa, Hajiya Aisha Buhari, a jiya ta bayyana cewa mijinta ya yi fama da ciwon Post Traumatic Stress Disorder (PTSD) na tsawon shekaru da dama

Wani hazikin dan achaba ya nuna cewa mutum na iya cimma abubuwa da dama a rayuwa a kowani irin bangare na kasuwancinsa.M...
05/10/2022

Wani hazikin dan achaba ya nuna cewa mutum na iya cimma abubuwa da dama a rayuwa a kowani irin bangare na kasuwancinsa.

Mutumin mai suna Kahii Cucu ya wallafa hoton wani hadadden gida da ya ginawa kansa da wacce za ta zama abokiyar rayuwarsa a gaba.

Idan Allah ya sanyawa kasuwancin mutum albarka, zai cimma nasarori da dama a rayuwa duk kankantar sana'ar. Wani dan achaba ya baje hoton gidan ya kerawa kansa.

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) ta yi Allah wadai da matakin da Koriya ta Arewa ta dauka na harba makami mai linzami a sara...
05/10/2022

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) ta yi Allah wadai da matakin da Koriya ta Arewa ta dauka na harba makami mai linzami a sararin samaniyar Japan.

Wannan ba komai bane face takalar fada.

Allah ya yi wa jarumin Kannywood, Umar Malumfashi, wanda aka fi sani da Yakubu Kafi Gwamna a Shirin Kwana Casa'in rasuwa...
27/09/2022

Allah ya yi wa jarumin Kannywood, Umar Malumfashi, wanda aka fi sani da Yakubu Kafi Gwamna a Shirin Kwana Casa'in rasuwa.

Marigayin ya rasu ne bayan magriba yau Talata a wani Asibiti a Kano, za'a gudanar da Jana'izarsa a Gidansa dake Hotoro gobe da safe.

Rahotanni daga jihar Kano sun tabbatar da cewa fitaccen jarumin masan'antar sgirya fina-finan Hausa, Umar Malumfashi, watau Kafi Gwamna na Kwana Casa'in ya rasu

DA DUMI DUMIN TA:Babban Kotun Jihar Adamawa ta Dakatar da Gwamnatin Jihar Adamawa daga kara Kudin Haraji sama da Dari Bi...
24/09/2022

DA DUMI DUMIN TA:
Babban Kotun Jihar Adamawa ta Dakatar da Gwamnatin Jihar Adamawa daga kara Kudin Haraji sama da Dari Biyar N500.

Kotun wanda Kungiyar Masu Dillacin Dabbobi s**a shigar da Karar Gwamnatin Jihar Adamawa, Antoni Jenar na Jihar da Hukumar Shigar da Kudin (Haraji) na Jihar Adamawa da kuma Komishinan Yan Sanda da Baban Jami'i tsaro na Civil Defense na Jihar Adamawa a gaban kutun.

Kotun ta Umarci Gwamnatin Jihar Adamawa data Dakatar da Karban Kudin Haraji sama da naira 500 nan take ba tare da wata wata ba.

Gwamnan jihar Benue ya bayyana irin yadda ayyukan ta'addanci s**a kai ga rasha mutanen jiharsa sama da 5000.A kasa da sh...
22/09/2022

Gwamnan jihar Benue ya bayyana irin yadda ayyukan ta'addanci s**a kai ga rasha mutanen jiharsa sama da 5000.

A kasa da shekaru 11, gwamnan ya ce an kai hare-hare sama da 200, kuma mutane sama da 5000 ne s**a mutu.

A hare-hare kusan 200 da aka kai jihar Benue, akalla mutane 5000 ne s**a rasa rayukansu ta sanadiyyar barnar tsageru cikin shekaru 11, Daily Trust ta ruwaito.

Wani rahoto yace Bello Turji da wani hatsabibin ɗan bindiga, Ɗan Bokolo, sun kaure da azababben yaƙi kan wani hari da ak...
22/09/2022

Wani rahoto yace Bello Turji da wani hatsabibin ɗan bindiga, Ɗan Bokolo, sun kaure da azababben yaƙi kan wani hari da aka kashe bayin Allah a yankin Shinkafi.

Wata majiya tace Tawagar Turji bata ji daɗin munanan hare-haren da aka kaiwa mutane ba, bisa haka ya yanke yaƙar Ɗan Bokolo. Sojoji sun zafafa luguden wuta kan yan ta'addan.

Wasu bayanai daga yankin karamar hukumar Shinkafi ta Zamfara sun nuja cewa tawagar Bello Turji ta fara yaƙar wani hatsabibin ɗan ta'adda kan kashe bayin Allah.

Wata kotu a Jihar Legas ta yanke wa wani fasto hukuncin daurin gidan yari saboda bada cek na bogi.Faston ya bada cek din...
22/09/2022

Wata kotu a Jihar Legas ta yanke wa wani fasto hukuncin daurin gidan yari saboda bada cek na bogi.

Faston ya bada cek din ga wani abokin huldarsa duk da cewa ya san babu kudi a cikin asusun bankinsa.

Kotun laifuka na musamman a Ikeja a ranar Laraba ta yanke wa wani Ayodeji Oluokun, mataimakin fasto a cocin Redeemed Christian Church of God (RCCG), a Victoria

Sufeta Janar na yan sandan ƙasar nan, IGP Usman Alƙali Baba, ya shiga ganawa da manyan jami'an hukumar yan sanda na faɗi...
22/09/2022

Sufeta Janar na yan sandan ƙasar nan, IGP Usman Alƙali Baba, ya shiga ganawa da manyan jami'an hukumar yan sanda na faɗin Najeriya.

Bayanai sun nuna cewa zasu tattauna kan zaɓen 2023, da kuma karuwar cin mutuncin 'yan sanda a bakin aiki da sauran batutuwa.

Shugaban rundunar 'yan sanda na ƙasa, IGP Usman Alƙali Baba, ya gana da AIGs, DIGs da kwamishinonin 'yan sanda na jihohi 36 da birnin tarayya Abuja kan batutuwa

Sojojin Najeriya sun yi nasarar ragargazar wasu 'yan ta'addan Boko Haram a wani kazamin harin da s**a kai a jihar Borno....
22/09/2022

Sojojin Najeriya sun yi nasarar ragargazar wasu 'yan ta'addan Boko Haram a wani kazamin harin da s**a kai a jihar Borno.

A harbe-harben da aka yi dasu, an hallaka 'yan ta'adda bakwai, wasu kuwa sun tsere da munanan raunukan harbin bindiga.

Sifeto Janar na yan sanda, IGP Usman Baba, ya bada umurnin hukunta Farfesa Zainab Duke Abiola da mai'aikinta Rebbeca Enechido bisa dukan tsiya da s**a yiwa

Malamai da Fastoci Sun Gudanar da Addu'a a Cikin Ruwa Kan samun Yardan Allah ha PDP a Zaben 2023Jam'iyyar PDP reshen jih...
19/09/2022

Malamai da Fastoci Sun Gudanar da Addu'a a Cikin Ruwa Kan samun Yardan Allah ha PDP a Zaben 2023

Jam'iyyar PDP reshen jihar Ogun ta koma ga Allah a yayin da ake shirin fara kamfen da gabatowar zaben 2023 An gano malaman Musulunci da fastoci suna rokon Allah alfarma yayin da ruwan sama ke bugunsu Musamman aka shirya taron don neman nasarar jam'iyyar a babban zabe mai zuwa tare da addu'an neman rabuwan kan jam'iyya mai mulki.

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jihar Ogun ta mika lamuranta ga Allah inda ta tashi tsaye da addu’o’i kan babban zaben 20023. A wasu hotuna da s**a yadu a intanet, an gano wasu malaman addini durkushe a cikin ruwan sama kamar da bakin kwarya suna masu addu’o’i a garin Abeokuta, babban birnin jihar.

Taron addu’an ya gudana ne a sakatariyar PDP, wanda ke kusa da ofishin Gwamna Dapo Abiodun, jaridar Premium Times ta rahoto.

A wajen taron, mambobin jam’iyya da malaman addinin da s**a yi biris da ruwan sama sun yi addu’a cikin kankan da kai don neman goyon bayan Ubangiji yayin da kamfen da zabe ke kara gabatowa.

Jama’ar wadanda s**a gudanar da addu’o’insu musamman don nasarar jam’iyyar a zaben, sun kuma yi addu’o’in neman raba kan jam’iyya mai mulki, musamman a jihar.

Da yake magana a taron, sakataren jam’iyyar, Sunday Solarin ya ce:
“Koda dai mutane basa yin jam’iyyar All Progressives Congress, APC, ya zama dole jam’iyyar ta nemi kariya daga masu bita da kulli da za su so tarwatsa shirin da PDP ta rigada tayi.”

Ya kara da cewa shugabannin matan jam’iyyar ne s**a bayar da shawarar yin taron addu’o’in, yana mai cewa ya kasance irinsa na farko da jam’iyyar tayi a jihar Ogun.

Address

No 16 Arhan Kunu Mubi South LGA
Mubi
64267

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when PAKKA FM Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to PAKKA FM Radio:

Share