Raga 24

Raga 24 Raga 24 Tasha ce da ke wallafa Sahihan Labarai Cikin Hotuna da Bidiyo da ma Rubutu na abubuwan da suke faruwa a Duniya.

Ana iya tuntubar mu a kan wannan Lambar Waya:
(09041856935)

Gwamnatin sojin kasar Mali karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita, ta ce ta dakile wani yunkurin juyin mulki da ake zar...
16/08/2025

Gwamnatin sojin kasar Mali karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita, ta ce ta dakile wani yunkurin juyin mulki da ake zargin ya samu goyon bayan kasar Faransa da kuma wasu manyan jami'an sojin Kasar ta Nijar.

A wani jabin kai tsaye da aka watsa a fadin kasar, gwamnatin mulkin sojin kasar Niger, ta sanar da k**a wasu janar-janar da wani dan kasar Faransa, Yann Vezilier, da ake zargi da yin leken asiri na kasar sa, gami da hada baki da masu goyon bayan juyin mulkin.

Ministan tsaron kasar Nijar, Janar Daoud Aly Mohammedine, ya yi zargin cewa dan kasar Faransar, yana aiki da wasu shugabannin siyasa a ƙasar, da ’ya yan kungiyoyin farar hula da ma wasu jami’an sojin kasar, wajen yunkurin hambarar da gwamnatin rikon kwaryar.

Wannan lamarin dei, ya zo ne watanni biyu bayan da gwamnatin mulkin sojin kasar ta rusa dukkanin jam'iyyun siyasa a Niger, duk kuwa da matsin lamba da ake yi na maido da mulkin farar hula da shirya zabe a kasar da ke yammacin Nahiyar Afirka.

Kanar Goita wanda ya karbi mulki a shekarar 2020, tun daga lokacin ya kara karfafa ikonsa, tare da hada kai da Kasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Chadi, sannan ya janye kasar Mali daga kungiyar ECOWAS, biyo bayan bukatar dawo da mulkin demokradiyya.

Raga 24

Yadda Ambaliyar ruwa ta haddasa ɓarna a Garin Potiskum.
16/08/2025

Yadda Ambaliyar ruwa ta haddasa ɓarna a Garin Potiskum.

Da safiyar ranar Litinin ne dei Tsohon Gwamnan Sokoton, Aminu Waziri Tambuwal.
12/08/2025

Da safiyar ranar Litinin ne dei Tsohon Gwamnan Sokoton, Aminu Waziri Tambuwal.

Jam'iyyar PDP a Najeriya na yunƙurin tsayar da Tsohon Shugaban Ƙasa Dr. Goodluck Ebele Jonathan takarar Shugaban Ƙasan N...
07/08/2025

Jam'iyyar PDP a Najeriya na yunƙurin tsayar da Tsohon Shugaban Ƙasa Dr. Goodluck Ebele Jonathan takarar Shugaban Ƙasan Nigeria a zaɓen 2027

Abun a jira a gani dei shine; Mr Jonathan zai amince da wannan tayin ko ah ah!

Hukumar zaben Nigeria INEC za ta fara Rajistar masu ka da Kuri'a a Nigeria.
06/08/2025

Hukumar zaben Nigeria INEC za ta fara Rajistar masu ka da Kuri'a a Nigeria.

Check out Raga 24’s video.

Nafisa Abdullah Aminu ta lashe gasar Iya Turanci ta 'Teen Eagle' a birnin London na kasar Birtaniya.
06/08/2025

Nafisa Abdullah Aminu ta lashe gasar Iya Turanci ta 'Teen Eagle' a birnin London na kasar Birtaniya.

Check out Raga 24’s video.

Nafisa Abdullah Aminu Yar shekara 17 ɗ haihuwa daga jihar Yobe a Najeriya, ta zama zakara a duniya a fannin fasahar hars...
05/08/2025

Nafisa Abdullah Aminu Yar shekara 17 ɗ haihuwa daga jihar Yobe a Najeriya, ta zama zakara a duniya a fannin fasahar harshen turanci a gasar Iya Turanci ta duniya, wato 'TeenEagle' na shekarar 2025 da aka gudanar a birnin Landan na kasar Birtaniya.

Nafisa, wacce ta fito daga Makarantar 'Nigerian Tulip International College' dake jihar Yobe, ta doke dalibai sama da dubu ashirin daga kasashe sittin da tara, ciki har da da yawa daga kasashen da Turanci shine harshen na Uawa.

A Gasar an taɓo fannoni daban-daban kan ƙwarewar turanci da sadarwa, wanda hakan ya sa nasarar da ta samu ya zama shaidar ƙwazonta, har ma da ingancin ilimin da ta samu a Najeriya.

A cewar rahoton, wannan gagarumin nasarar na cikin wata sanarwa da Hassan Salifu, wanda ya danganta nasarar Nafisa da sadaukarwa, da'a, da kuma tallafin gwamnatin jihar Yobe.

Iyalan Nafisa sun mika godiyar su ga mahukunta da ma’aikatan Kwalejin Tulip bisa yadda suke renon dalibai k**ar Nafisa don samun ci gaba a duniya.

Sun kuma yi kira ga gwamnatocin jihohi da na tarayya da su karrama nasarar da ta samu a hukumance, inda s**a ce nasarar da ta samu ya nuna cewa daliban Najeriya za su iya yin takara da kuma yin fice a duniya idan aka ba su ilimin da tallafi da ya dace

05/08/2025

Rahoton da Hukumar Hasashen Yanayi ta Nigeria NIMET ta sake fitarwa ya jefa jama'a a Nigeria cikin fargaba.

05/08/2025

Watch, follow, and discover more trending content.

Ƙasar Saudiyyar ta zartas da hukuncin kan mutum takwas ɗin ne bisa samun su da laifin TA'AMMALI da Miyagun Kwayoyi.
04/08/2025

Ƙasar Saudiyyar ta zartas da hukuncin kan mutum takwas ɗin ne bisa samun su da laifin TA'AMMALI da Miyagun Kwayoyi.

Omar bin Laden mai shekara 44 da haihuwa a bana, da ya zama marubuci kuma mai zane-zane, ɗa na huɗu ne ga Osama bin Lade...
04/08/2025

Omar bin Laden mai shekara 44 da haihuwa a bana, da ya zama marubuci kuma mai zane-zane, ɗa na huɗu ne ga Osama bin Laden.

Omar ya kasance jika ga Mohammed bin Awad bin Laden, ɗaya daga cikin manyan attajirai na ƙasar Saudiyya. Ya raka mahaifinsa zuwa gudun hijira zuwa Sudan da Afghanistan.

Yana da ƴan uwa 26, inda cikinsu akwai maza 11.

Ya riƙa baje kolin zane-zanensa a ƙasar Faransa har zuwa shekarar 2023, amma daga baya an haramta masa shiga da zama a ƙasar saboda yana wallafa bayanai masu "ɗaukaka ta'addanci" a shafukan sada zumunta.

Ana iya ganinsa tare da matarsa, Zaina Mohamed Al-Sabah, wacce asalin sunanta Jane Felix-Browne.

Zaina baturiyar ƙasar Ingila ce, wacce ya aura a 2008, a lokacin tana mai shekara 51 da haihuwa, shi kuma yana da shekara 27.

Auren shi da Zaina shi ne na biyu, ita kuma aurenta na shida ke nan. Ya fara ganinta ne yayin wata ziyara da ta kai kasar Masar, kuma bayan wata bakwai s**a yi aure, inda aka yi kasaitaccen bikin a Masar da Saudiyya.

Attajirin da ya ya fi kowa kuɗi a nahiyar Afirka, Aliko Ɗangote ya fara ja da baya, inda sannu a hankali yake miƙa ragam...
04/08/2025

Attajirin da ya ya fi kowa kuɗi a nahiyar Afirka, Aliko Ɗangote ya fara ja da baya, inda sannu a hankali yake miƙa ragamar kamfanoninsa ga ƴaƴansa mata uku.

Mujallar Bloomberg ta ƙiyasta cewa Ɗangote na da dala biliyan 28.5 na dukiya zuwa ranar 28 ga watan Yulin 2025.

A misali, ɗan kasuwar mai shekara 68 da haihuwa, ya ajiye muƙaminsa na shugaban kamfanin Ɗangote Sugar Refinery a watan Yuni. Sannan ranar Juma'ar da ta gabata, ya sauka daga jagorancin kamfanin Ɗangote Cement.

Babbar ƴarsa Mariya ce ta maye gurbinsa a kamfanin na Ɗangote Cement.

Kafin wannan lokacin ta kasance babbar daraktar kamfanonin Dangote Sugar da Ɗangote Investments Limited (DIL), tun 2016 bayan ta kammala karatun digirinta na biyu kan kasuwanci a Jami'ar Coventry da ke Birtaniya.

Ita kuma ƴarsa ta biyu Halima Ɗangote, an naɗa ta ga muƙamin darakta a kamfanin Ɗangote Cement tun 2022, jim kaɗan bayan rasuwar kawunta Sani Ɗangote.

A baya ta riƙe muƙamai a Ɗangote Investments Limited tun 2019, da kamfanin Dangote Flour Mills, kafin sayar da shi ga Olam Group na Singapore.

Sai kuma ƴarsa ta uku mai suna Fatima, wacce ita ce babbar daraktar kasuwanci a kamfanin zuba jari na Ɗangote Investments Limited.

Ita ma ta riƙe manyan muƙamai a wasu ɓangarori na rukunin kamfanonin na Ɗangote.

Aliko Ɗangote ya yaba wa gudunmawar da ƴaƴan nasa mata ke bayar wa ga kamfanoninsa:

"Duka ƴaƴana mata uku, wato Mariya da Halima da Fatima suna riƙe da manyan muƙamai a kamfanonina, kuma ina tabbatar muku cewa suna taka muhimmiyar rawa wajen samar da nasarorin da muke gani a harkokinmu na kasuwanci."

Address

Mubi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Raga 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share