
16/08/2025
Gwamnatin sojin kasar Mali karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita, ta ce ta dakile wani yunkurin juyin mulki da ake zargin ya samu goyon bayan kasar Faransa da kuma wasu manyan jami'an sojin Kasar ta Nijar.
A wani jabin kai tsaye da aka watsa a fadin kasar, gwamnatin mulkin sojin kasar Niger, ta sanar da k**a wasu janar-janar da wani dan kasar Faransa, Yann Vezilier, da ake zargi da yin leken asiri na kasar sa, gami da hada baki da masu goyon bayan juyin mulkin.
Ministan tsaron kasar Nijar, Janar Daoud Aly Mohammedine, ya yi zargin cewa dan kasar Faransar, yana aiki da wasu shugabannin siyasa a ƙasar, da ’ya yan kungiyoyin farar hula da ma wasu jami’an sojin kasar, wajen yunkurin hambarar da gwamnatin rikon kwaryar.
Wannan lamarin dei, ya zo ne watanni biyu bayan da gwamnatin mulkin sojin kasar ta rusa dukkanin jam'iyyun siyasa a Niger, duk kuwa da matsin lamba da ake yi na maido da mulkin farar hula da shirya zabe a kasar da ke yammacin Nahiyar Afirka.
Kanar Goita wanda ya karbi mulki a shekarar 2020, tun daga lokacin ya kara karfafa ikonsa, tare da hada kai da Kasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Chadi, sannan ya janye kasar Mali daga kungiyar ECOWAS, biyo bayan bukatar dawo da mulkin demokradiyya.
Raga 24