23/08/2026
AL’UMMAR NGURU NA CIGABA DA FAMA DA RASHIN WUTA
Akwai masu faɗa a ji da za su iya ɗaukar waya su kira sau ɗaya kawai, kuma hakan na iya taimakawa wajen magance irin wannan matsalar da al’ummar garin Nguru ke fuskanta a yanzu.
Matsalar wutar lantarki ta yi yawa, abin takaici kuma ana ganin kamar akwai rashin kulawa daga wasu masu faɗa a ji a cikin gari. Ban sani ba ko hakan yana da alaƙa da rashin sanin halin da ake ciki, musamman ganin cewa wasu daga cikinsu suna da Solar a gidajensu.
Amma abin da ke faruwa yanzu ba ƙaramin abu ba ne. Rashin wutar lantarki ya jefa al’umma cikin matsala, har ana ganin mutane suna ta yawon neman ruwan sha saboda rashin wutar da za ta taimaka wajen samar da shi. Gaskiya abin ba daɗi ne.
Waɗanda suke kusa da masu faɗa a ji, muna roƙonku da ku isar musu da halin da al’ummar Nguru suke ciki. Akwai buƙatar a ɗauki mataki cikin gaggawa domin rage wannan matsala.
Allah Ya kawo mana sauƙi, Ya kyauta.