Labari Daga Ningi

Labari Daga Ningi Kamfanin yada Labarai Wanda aka bude a shekarar 2020
📞Tuntuɓa
07063938533
07036505748
09034829145

Da Dumi-Dumi: An Dakatar da Shiga Ruwan Yankari Bayan Ƙaruwar Ruwa.Mahukuntan Ruwan Yankari sun sanar da dakatar da shig...
07/06/2026

Da Dumi-Dumi: An Dakatar da Shiga Ruwan Yankari Bayan Ƙaruwar Ruwa.

Mahukuntan Ruwan Yankari sun sanar da dakatar da shiga ko yin wanka a ruwan na ɗan lokaci bayan da aka lura da ƙarin ruwa fiye da yadda aka saba a yammacin ranar Asabar.

An ɗauki matakin ne a matsayin kariya domin tabbatar da lafiyar baƙi da masu yawon buɗe ido, yayin da ake ci gaba da sa ido kan yanayin ruwan domin kauce wa duk wani haɗari.

Mahukuntan sun bayyana cewa dakatarwar ta wucin gadi ce, tare da tabbatar da cewa za a buɗe wurin ga baƙi da zarar yanayin ruwan ya daidaita kuma ya koma yadda aka saba.

A ranar 6 ga Yuni, 2026, Sanatan da ke wakiltar Mazabar Bauchi ta Tsakiya, Abdul Ahmed Ningi, ya kaddamar da aikin gina ...
06/06/2026

A ranar 6 ga Yuni, 2026, Sanatan da ke wakiltar Mazabar Bauchi ta Tsakiya, Abdul Ahmed Ningi, ya kaddamar da aikin gina hanyar da ta haɗa Nasaru, Tudun Wada da Dallaji a Ƙaramar Hukumar Warji.

an fara aikin nan take bayan kaddamarwar, tare da ci gaba da aiwatar da shi bisa tsarin da aka tanada.

Haka kuma, an gudanar da kaddamar da aikin hanyar garin Burra da ke Ƙaramar Hukumar Ningi.

Rahotanni sun nuna cewa aikin zai fara ne daga cikin garin Burra, inda ake sa ran zai taimaka wajen inganta hanyoyin sufuri da zirga-zirga a yankin.

Ayyukan hanyoyin na daga cikin ayyukan raya ababen more rayuwa da ake aiwatarwa a sassan Mazabar Bauchi ta Tsakiya.

KOTUN BAUCHI TA YI WATSI DA KARAR KALUBALANTAR ZAƁEN FIDDA-GWANIN GWAMNAN PRPBabbar Kotun Jihar Bauchi ta yi watsi da ƙa...
06/06/2026

KOTUN BAUCHI TA YI WATSI DA KARAR KALUBALANTAR ZAƁEN FIDDA-GWANIN GWAMNAN PRP

Babbar Kotun Jihar Bauchi ta yi watsi da ƙarar da Barrista Idris Safiyanu Gambo ya shigar kan zaɓen fidda-gwanin gwamna na jam’iyyar PRP, tare da cin sa tarar Naira miliyan biyu.

Kotun ta yanke hukuncin ne bayan mai ƙarar ya nemi janye shari’ar da ya shigar yana zargin an cire shi daga zaɓen fidda-gwanin jam’iyyar da aka gudanar a watan Mayu.

Alƙalin kotun, Kunaza N. Hamidu, ya ce bayan ɓangarorin sun riga sun shiga muhawara kan shari’ar, abin da ya dace shi ne a yi watsi da ƙarar maimakon a janye ta.

Jam’iyyar PRP da ɗan takararta na gwamna, Shehu Buba Umar, sun yi maraba da hukuncin, suna masu cewa ya kawo ƙarshen rashin tabbas tare da bai wa jam’iyyar damar ci gaba da shirye-shiryenta na siyasa.

06/06/2026

Yayin da tawagar Sanata Abdul Ahmed Ningi ke shiga filin taro.

Hotuna: Yanzu haka Sen. Abdul Ahmed Ningi yana gudanar da taron kaddamar da hanyar Burra dake karamar hukumar Ningi a  r...
06/06/2026

Hotuna: Yanzu haka Sen. Abdul Ahmed Ningi yana gudanar da taron kaddamar da hanyar Burra dake karamar hukumar Ningi a ranar Asabar 6/6/2026

06/06/2026

Bidiyo: Kaɗan daga cikin Jawabin Sen. Abdul Ahmed Ningi yayin ƙaddamar da aikin hanyar Dallaji a ranar Asabar 6/06/2026.

Hotuna: Shirye-shirye sun kankama gabanin kaddamar da aikin titin Dallaji da Sanata Abdul Ahmed Ningi ya samar a Ƙaramar...
06/06/2026

Hotuna: Shirye-shirye sun kankama gabanin kaddamar da aikin titin Dallaji da Sanata Abdul Ahmed Ningi ya samar a Ƙaramar Hukumar Warji.

DA ƊUMI-ƊUMI: AN GYARA AUREN DA AKA ƊAURA SHI BA BABISA ƘA'IDA BA, WANDA AKA BADA SADAKI DUBU UKU (3000) A BAUCHIKwamiti...
06/06/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: AN GYARA AUREN DA AKA ƊAURA SHI BA BABISA ƘA'IDA BA, WANDA AKA BADA SADAKI DUBU UKU (3000) A BAUCHI

Kwamitin Yaki da Cin Zarafin Jama’a (GBV) na Jihar Bauchi, tare da haɗin gwiwar Hukumar Hisba da kuma goyon bayan Ofishin Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi, sun samu nasarar sasanta rikicin da ya shafi auren da ya janyo ce-ce-ku-ce kan sadakin Naira 3,000.

Bayan zaman sulhu da shawarwari tsakanin bangarorin da abin ya shafa, an cimma matsaya tare da ɗaura auren Muhammad da Kamila bisa tsarin Shari’ar Musulunci a kan sadakin Naira N250,000 a gaban iyaye, waliyyai da shaidu kamar yadda addini ya tanada.

Shugaban Hukumar Hisba ta Jihar Bauchi, Barista Aminu Balarabe Isa, ya bayyana cewa an bi matakan da s**a dace wajen warware lamarin, tare da ɗaukar matakan da s**a dace kan abin da ya faru a baya bisa tanadin doka da shari’a.

Ya kuma yi kira ga al’umma da su rika bin hanyoyin da addinin Musulunci ya tanada wajen gudanar da aure, yana mai gargadin cewa za a ci gaba da ɗaukar mataki kan duk wani abu da ya saɓa wa ƙa’idojin aure.

A nata jawabin, Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Yara ta Jihar Bauchi, Hajiya Talatu Musa, ta taya ma’auratan murna tare da yi musu nasiha kan muhimmancin hakuri, fahimtar juna da zaman lafiya a rayuwar aure.

Iyalan ango da amarya sun nuna godiya ga Kwamitin GBV, Ofishin Uwargidan Gwamna da Hukumar Hisba bisa kokarin da s**a yi wajen sasanta lamarin da tabbatar da gudanar da auren cikin tsari.

Wannan nasara na nuna irin kokarin da gwamnati da masu ruwa da tsaki ke yi wajen kare martabar aure, tabbatar da bin doka da kuma inganta zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Allah Ya sanya albarka a auren Muhammad da Kamila, Ya ba su zaman lafiya da zuri'a ta gari. Ameen.

Shin me kuke ganin za a iya yi domin kauce wa irin wannan rikici a harkokin aure nan gaba?

A Yau Asabar 06/06/2026, Sen. Abdul Ahmed Ningi zai kaddamar da aikin hanyar Dallaji a karamar hukumar Warji da gyaran h...
06/06/2026

A Yau Asabar 06/06/2026, Sen. Abdul Ahmed Ningi zai kaddamar da aikin hanyar Dallaji a karamar hukumar Warji da gyaran hanyar Burra zuwa Ningi.

TURKASHI: Wani ɗan takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai neman wakiltar mazaɓar Haɗejia/Auyo/Kafin-Hausa a Ji...
06/06/2026

TURKASHI: Wani ɗan takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai neman wakiltar mazaɓar Haɗejia/Auyo/Kafin-Hausa a Jihar Jigawa ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2027, Kwamared Umar Ɗanjani, ya ziyarci wani ƙauye inda ya zauna tare da al’ummar yankin tare da cin abinci domin neman yardarsu da goyon bayansu.

Address

Ningi
742101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labari Daga Ningi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labari Daga Ningi:

Share