06/06/2026
DA ƊUMI-ƊUMI: AN GYARA AUREN DA AKA ƊAURA SHI BA BABISA ƘA'IDA BA, WANDA AKA BADA SADAKI DUBU UKU (3000) A BAUCHI
Kwamitin Yaki da Cin Zarafin Jama’a (GBV) na Jihar Bauchi, tare da haɗin gwiwar Hukumar Hisba da kuma goyon bayan Ofishin Uwargidan Gwamnan Jihar Bauchi, sun samu nasarar sasanta rikicin da ya shafi auren da ya janyo ce-ce-ku-ce kan sadakin Naira 3,000.
Bayan zaman sulhu da shawarwari tsakanin bangarorin da abin ya shafa, an cimma matsaya tare da ɗaura auren Muhammad da Kamila bisa tsarin Shari’ar Musulunci a kan sadakin Naira N250,000 a gaban iyaye, waliyyai da shaidu kamar yadda addini ya tanada.
Shugaban Hukumar Hisba ta Jihar Bauchi, Barista Aminu Balarabe Isa, ya bayyana cewa an bi matakan da s**a dace wajen warware lamarin, tare da ɗaukar matakan da s**a dace kan abin da ya faru a baya bisa tanadin doka da shari’a.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su rika bin hanyoyin da addinin Musulunci ya tanada wajen gudanar da aure, yana mai gargadin cewa za a ci gaba da ɗaukar mataki kan duk wani abu da ya saɓa wa ƙa’idojin aure.
A nata jawabin, Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Yara ta Jihar Bauchi, Hajiya Talatu Musa, ta taya ma’auratan murna tare da yi musu nasiha kan muhimmancin hakuri, fahimtar juna da zaman lafiya a rayuwar aure.
Iyalan ango da amarya sun nuna godiya ga Kwamitin GBV, Ofishin Uwargidan Gwamna da Hukumar Hisba bisa kokarin da s**a yi wajen sasanta lamarin da tabbatar da gudanar da auren cikin tsari.
Wannan nasara na nuna irin kokarin da gwamnati da masu ruwa da tsaki ke yi wajen kare martabar aure, tabbatar da bin doka da kuma inganta zaman lafiya a tsakanin al’umma.
Allah Ya sanya albarka a auren Muhammad da Kamila, Ya ba su zaman lafiya da zuri'a ta gari. Ameen.
Shin me kuke ganin za a iya yi domin kauce wa irin wannan rikici a harkokin aure nan gaba?