09/07/2026
EFCC Ta Gurfanar da Shugaban Miyetti Allah, Bello Bodejo, Kan Zargin Laifin Dala Miliyan $2.33
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (EFCC) ta gurfanar da shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal H**e, Bello Bodejo, a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Laraba, 9 ga Yuli, 2026, bisa zargin aikata laifukan kuɗi.
An gurfanar da Bodejo ne kan tuhume-tuhume guda 12 da s**a shafi halasta kuÉ—aÉ—en haram (money laundering), waÉ—anda jimillar kuÉ—insu ta kai dala miliyan $2.33.
A zaman kotun, lauyan masu gabatar da ƙara, Wahab Sh*ttu, SAN, ya roƙi kotun da ta karɓi takardar tuhume-tuhumen da aka shigar a ranar 25 ga Yuni, 2026, domin a karanta wa wanda ake tuhuma laifukan da ake zarginsa da su. Alƙalin kotun ya amince da buƙatar.
Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen ya ce Bodejo ya karɓi dala $100,000 a tsabar kuɗi daga Sa'idu Abubakar, tsohon Akanta Janar na Jihar Bauchi, a ranar 11 ga Janairu, 2022, ba tare da bi ta banki ba, duk da cewa kuɗin sun zarce iyakar da doka ta tanada. Wannan, a cewar EFCC, ya saɓa da Dokar Hana Halasta Kuɗaɗen Haram ta shekarar 2011.
Wani tuhume-tuhumen kuma ya ce a ranar 7 ga Fabrairu, 2024, Bodejo ya sake karɓar dala $980,000 a tsabar kuɗi daga Sa'idu Abubakar ba tare da amfani da banki ba, lamarin da ake zargin ya saɓa da Dokar Hana da Rigakafin Halasta Kuɗaɗen Haram ta shekarar 2022.
Bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, Bodejo ya musanta dukkan laifukan da ake zarginsa da su.
Lauyan EFCC ya roƙi kotun ta sanya ranar fara shari'a tare da tsare wanda ake tuhuma a gidan gyaran hali, yayin da lauyan Bodejo, Ahmed Raji, SAN, ya buƙaci kotun ta ba shi beli bisa buƙatar da ya gabatar tun ranar 30 ga Yuni, 2026.
Sai dai EFCC ta yi adawa da bayar da belin, tana mai cewa Bodejo na da haÉ—arin tserewa ko kuma yin tasiri ga shaidu, tare da bayyana cewa Hukumar DSS ma na bibiyarsa.
Daga ƙarshe, Mai Shari'a Inyang Edem Ekwo ya ba da umarnin a tsare Bodejo a cibiyar tsare mutane ta EFCC, sannan ya ɗage sauraron shari'ar zuwa 20 ga Yuli, 2026, domin yanke hukunci kan buƙatar belinsa.