Labari Daga Ningi

Labari Daga Ningi Kamfanin yada Labarai Wanda aka bude a shekarar 2020
📞Tuntuɓa
07063938533
07036505748
09034829145

EFCC Ta Gurfanar da Shugaban Miyetti Allah, Bello Bodejo, Kan Zargin Laifin Dala Miliyan $2.33Hukumar Yaƙi da Cin Hanci ...
09/07/2026

EFCC Ta Gurfanar da Shugaban Miyetti Allah, Bello Bodejo, Kan Zargin Laifin Dala Miliyan $2.33

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (EFCC) ta gurfanar da shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal H**e, Bello Bodejo, a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Laraba, 9 ga Yuli, 2026, bisa zargin aikata laifukan kuɗi.

An gurfanar da Bodejo ne kan tuhume-tuhume guda 12 da s**a shafi halasta kuÉ—aÉ—en haram (money laundering), waÉ—anda jimillar kuÉ—insu ta kai dala miliyan $2.33.

A zaman kotun, lauyan masu gabatar da ƙara, Wahab Sh*ttu, SAN, ya roƙi kotun da ta karɓi takardar tuhume-tuhumen da aka shigar a ranar 25 ga Yuni, 2026, domin a karanta wa wanda ake tuhuma laifukan da ake zarginsa da su. Alƙalin kotun ya amince da buƙatar.

Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen ya ce Bodejo ya karɓi dala $100,000 a tsabar kuɗi daga Sa'idu Abubakar, tsohon Akanta Janar na Jihar Bauchi, a ranar 11 ga Janairu, 2022, ba tare da bi ta banki ba, duk da cewa kuɗin sun zarce iyakar da doka ta tanada. Wannan, a cewar EFCC, ya saɓa da Dokar Hana Halasta Kuɗaɗen Haram ta shekarar 2011.

Wani tuhume-tuhumen kuma ya ce a ranar 7 ga Fabrairu, 2024, Bodejo ya sake karɓar dala $980,000 a tsabar kuɗi daga Sa'idu Abubakar ba tare da amfani da banki ba, lamarin da ake zargin ya saɓa da Dokar Hana da Rigakafin Halasta Kuɗaɗen Haram ta shekarar 2022.

Bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, Bodejo ya musanta dukkan laifukan da ake zarginsa da su.

Lauyan EFCC ya roƙi kotun ta sanya ranar fara shari'a tare da tsare wanda ake tuhuma a gidan gyaran hali, yayin da lauyan Bodejo, Ahmed Raji, SAN, ya buƙaci kotun ta ba shi beli bisa buƙatar da ya gabatar tun ranar 30 ga Yuni, 2026.

Sai dai EFCC ta yi adawa da bayar da belin, tana mai cewa Bodejo na da haÉ—arin tserewa ko kuma yin tasiri ga shaidu, tare da bayyana cewa Hukumar DSS ma na bibiyarsa.

Daga ƙarshe, Mai Shari'a Inyang Edem Ekwo ya ba da umarnin a tsare Bodejo a cibiyar tsare mutane ta EFCC, sannan ya ɗage sauraron shari'ar zuwa 20 ga Yuli, 2026, domin yanke hukunci kan buƙatar belinsa.

DA ƊUMINSA: Shugaban Ƙaramar Hukumar Jahun, jahar Jigawa Ya Tallafa wa Al'ummarsa da Bandir ɗin Langa-Langa.
09/07/2026

DA ƊUMINSA: Shugaban Ƙaramar Hukumar Jahun, jahar Jigawa Ya Tallafa wa Al'ummarsa da Bandir ɗin Langa-Langa.

Wanne fata za ku yi masa.?
09/07/2026

Wanne fata za ku yi masa.?

TURKASHI: 'Ina So Ya Zama Doka Cewa Duk Wanda Ya Kashè Shima A Kàshè Shi, Babu Wata Maganar Gyaran Hali Bayan Sun Tuba, ...
08/07/2026

TURKASHI: 'Ina So Ya Zama Doka Cewa Duk Wanda Ya Kashè Shima A Kàshè Shi, Babu Wata Maganar Gyaran Hali Bayan Sun Tuba, Haka Kurum Ka Sace Mutum Ka Kai Shi Daji Ka Azabtar Da Shi Kafin Ya Mutu, Sannan A Ce Za A Yi Maka Afuwa".

—Cewar Hon Yusif Gagdi

DA DUMI-DUMI: Duk Sojan Da Ya Ƙi Kãshe Dan Ta'ad-da Ya Tsaya Yana Jiran Umarni, To Za A Dauke Shi A Matsayin Ɗan Ta'ad-d...
08/07/2026

DA DUMI-DUMI: Duk Sojan Da Ya Ƙi Kãshe Dan Ta'ad-da Ya Tsaya Yana Jiran Umarni, To Za A Dauke Shi A Matsayin Ɗan Ta'ad-da Shima - Cewar Ministan Tsaro

Ministan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce duk sojan da ya ƙi kashe ɗan ta'adda ko ɗan bindiga yana jiran umarni daga manyansa, za a ɗauke shi a matsayin ɗan ta'adda. Ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin rabon sabbin kayan aikin soji a jihar Sokoto.

Ya ce gwamnati ta kashe biliyoyin naira wajen sayo kayan aikin domin ƙarfafa yaƙi da rashin tsaro, tare da umartar sojoji su yi amfani da su yadda ya kamata kuma su kula da su domin su daɗe suna aiki.

DA ÆŠUMINSA: Hukumar Raya Birane Ta Bai Wa Masu Kwantenonin da Aka Yi Wa Lamba A Ningi Wa'adin Mako Guda Su Kwashe Su Ko ...
08/07/2026

DA ÆŠUMINSA: Hukumar Raya Birane Ta Bai Wa Masu Kwantenonin da Aka Yi Wa Lamba A Ningi Wa'adin Mako Guda Su Kwashe Su Ko Su Fuskanci Matakin Doka.

Wata mata mai shekara 27 daga ƙasar Canada mai suna Carolina Moreno ta ba da labarin yadda ta haifi ɗanta na uku ba tare...
08/07/2026

Wata mata mai shekara 27 daga ƙasar Canada mai suna Carolina Moreno ta ba da labarin yadda ta haifi ɗanta na uku ba tare da ta sani ba, bayan ta yi barci yayin nakuda a asibiti.

Jaridar Punch ta ruwaito ta ce an saka mata maganin tayar da nakuda da kuma allurar rage radadi, lamarin da ya sa ta yi barci mai nauyi.

A cewarta, yayin da ma’aikatan jinya ke neman bugun zuciyar jaririn ta na’urar sa ido, ba su fahimci cewa jaririn ya riga ya fito da kansa ba.

Da aka buɗe bargon da ke kanta, sai aka tarar da jaririn kwance a ƙarƙashinta ba tare da yana kuka ba, abin da ya tayar da hankalin kowa da ke ɗakin karɓar haihuwar.

Mahaifiyar jaririn ta ɗauke shi nan take ta motsa shi har ya fara kuka. Daga baya likitoci s**a tabbatar da cewa jaririn yana cikin ƙoshin lafiya.

Yanzu haka dai yaron yana da wata uku a duniya, kuma mahaifiyarsa ta ce yana girma cikin koshin lafiya kuma shi ne mafi natsuwa a cikin ‘ya’yanta uku.

Wata Mata ta haihu tana bacci, inda ta tarar da jaririnta ƙarƙashin bargoKarin bayani:https://shorturl.at/dbG5m
08/07/2026

Wata Mata ta haihu tana bacci, inda ta tarar da jaririnta ƙarƙashin bargo

Karin bayani:
https://shorturl.at/dbG5m

Ma'aikatar Ilimi ta Bauchi Na Nazarin Yiwuwar Sake HaÉ—a Maza da Mata a Makarantu Domin Inganta KaratuKwamishinan Ilimi n...
08/07/2026

Ma'aikatar Ilimi ta Bauchi Na Nazarin Yiwuwar Sake HaÉ—a Maza da Mata a Makarantu Domin Inganta Karatu

Kwamishinan Ilimi na Jihar Bauchi, Hon. Abdulkadir Ibrahim Cikasoro, ya bayyana cewa Ma'aikatar Ilimi na nazarin yiwuwar sake haɗa ɗalibai maza da mata a makarantu domin inganta ingancin karatu da kuma bunƙasa ilimi a faɗin jihar.

Gwamnatin M.A. Abubakar ta hau karagar mulki da kyakkyawar manufar sauya tsarin ilimi a Jihar Bauchi, tare da mayar da j...
07/07/2026

Gwamnatin M.A. Abubakar ta hau karagar mulki da kyakkyawar manufar sauya tsarin ilimi a Jihar Bauchi, tare da mayar da jihar cibiyar ilimi mai inganci da kuma dawo da martabar da ta taɓa samu a baya.

A ƙarƙashin jagorancin M.A., an farfaɗo da ababen more rayuwa tare da zuba jari mai yawa a fannin ilimin firamare. An gina Makarantar Firamare ta Katije, sannan aka gyara Makarantun Firamare na Garko da Nasaru a Ƙaramar Hukumar Ningi.

Haka kuma, an gina sabon ginin ajujuwa a Makarantar Firamare ta Unguwar Abuja da ke Ƙaramar Hukumar Jama'are. An kuma gyara Makarantar Firamare ta Sabon Kafi B, tare da samar da kujeru da teburan karatu ga Makarantun Firamare na Wambiyo da Kyawa, duk a Ƙaramar Hukumar Jama'are.

Bugu da ƙari, tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019, an gina sabbin ajujuwa a Makarantun Firamare na Kaskindim da Yakori a Ƙaramar Hukumar Shira.

WaÉ—annan manyan nasarori sun nuna gagarumin ci gaba da aka samu wajen inganta ababen more rayuwa a fannin ilimin firamare, tare da tabbatar da cewa É—alibai suna samun ilimi a cikin muhalli mai kyau da dacewa.

Gwamnatin M.A. ta kuma ba da muhimmanci ga ilimi ga kowa (inclusive education), inda ta samar da cikakken kuÉ—aÉ—en aiwatar da ayyukan da aka tsara a tsawon wa'adin mulkinta na shekaru huÉ—u.

Waɗannan kaɗan ne daga cikin ayyukan da gwamnatin M.A. Abubakar ta aiwatar domin bunƙasa ilimi a Jihar Bauchi.

A rubutunmu na gaba, za mu ci gaba da bayyana sauran dimbin shirye-shirye da ayyukan ci gaban ilimi da wannan gwamnati ta aiwatar.

—Buhari Garba Doya

Address

Ningi
Ningi
742101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labari Daga Ningi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labari Daga Ningi:

Shortcuts

Share