NUMAN 24

NUMAN 24 Media /news company

To???????
09/11/2025

To???????

Turkiyyata ba da sammacin k**a Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da wasu manyan jami'an gwamnatinsa 37 kan zargin aikata laifukan yaƙi a Gaza.

09/11/2025

Barazanar Trump ga Nijeriya: Ya k**ata Amurka ta san cewa akwai doka a duniya - Russia

Gwamnatin Russia ta yi kira ga shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump da ya san da cewa akwai dokoki a duniya kuma ko wacce ƙasa tana da ikon cin gashin kan ta.

Ta kuma bayyana cewa ta na lura da irin rahotannin da ke cewa Amurka na iya ɗaukar matakin soja a Najeriya, bayan kalaman tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump, da ya ce zai iya tura dakarun Amurka domin “kare Kiristoci” a kasar.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha, Maria Zakharova, ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a Moscow ranar Juma’a, inda ta jaddada cewa Rasha na kira ga Amurka da sauran ɓangarorin da abin ya shafa su bi ƙa’idojin dokokin ƙasa da ƙasa.

Zakharova ta ce, “Muna bibiyar wannan batu sosai, kuma muna kira da a yi taka-tsantsan tare da mutunta ikon mallakar ƙasa.”

Kalaman nata sun biyo bayan jawabin Trump a ranar 1 ga Nuwamba, inda ya ce ya umarci Ma’aikatar Tsaron Amurka (Pentagon) da ta tsara shirin yiwuwar kai farmaki a Najeriya.

Duk da cewa babu wata sanarwa ta hukuma daga Washington kan lamarin, furucin Trump ya haifar da martani daga ƙasashen waje, ciki har da Moscow, wadda ta yi gargadin cewa duk wani mataki ya zama bisa tsarin doka da girmama ‘yancin kowace ƙasa.

09/11/2025

Kungiyar JIBWIS ta mayar da martani kan zargin “Kisan Kiristoci” da ya janyo takaddama tsakanin Najeriya da Amurka

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa’Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, ta bayyana damuwa kan takaddamar diflomasiyya da ke tsakanin gwamnatin tarayyar Najeriya da gwamnatin Amurka, sak**akon rahotanni marasa tushe da s**a zargi Najeriya da aiwatar da abin da aka kira “kisan Kiristoci” a kasar.

A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a ranar Talata, 4 ga Nuwamba, 2025, JIBWIS ta bayyana cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne kuma yana iya rura wutar rikici, tana mai jaddada cewa matsalolin tsaro da ake fuskanta a Najeriya irin su ta’addanci, garkuwa da mutane, da rikice-rikicen al’umma ba su da tushe daga addini, illa dai matsalolin tattalin arziki, cin hanci, da raunin tsarin mulki.

Kungiyar ta jaddada cewa Musulmai da Kiristoci duka sun kasance cikin wadanda s**a fi fuskantar tasirin wadannan matsaloli, inda ta ce kiran abin da ke faruwa “kisan Kiristoci” bai inganta ba kuma yana barazana ga zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

JIBWIS ta kuma yi kira ga kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) da sauran shugabannin addinin Kirista da su nesanta kansu daga irin wadannan zarge-zargen, tare da bayyana cewa dukkan shugabannin addinai a kasar suna da alhakin tabbatar da gaskiya da kuma guje wa amfani da addini wajen cimma manufar siyasa ko ta kasashen waje.

Kungiyar ta shawarci gwamnatin Amurka da ta yi la’akari da bincike na gaskiya da hujjoji kafin daukar matakai, tare da mutunta ikon Najeriya da kare martabar hadin kan kasar. Ta kuma bukaci Amurka da ta mayar da hankali kan bunkasa zaman lafiya, yaki da ta’addanci, da inganta tsaro, maimakon wani bangare.

Haka zalika, JIBWIS ta shawarci kungiyoyin farar hula, masu sa ido kan hakkin dan Adam, da cibiyoyin bincike su kasance masu rahotanni na gaskiya da hujja, saboda wallafa alkaluma marasa tushe na iya haifar da rikici da rashin fahimtar juna. Ta kuma yi kira ga ’yan jarida da masu amfani da kafafen sada zumunta da su guji yada labarai marasa inganci da kalmomin da ke tayar da hankali, domin bin diddigin gaskiya.

Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, wanda ya sanya hannu kan sanarwar, ya mika ta’aziyya ga Musulmai da Kiristocin da s**a rasa ‘yan uwansu ko dukiyoyinsu sak**akon matsalolin tsaro a fadin kasar, yana rokon Allah Ya basu hakuri.

A karshe, JIBWIS ta yaba da diflomasiyyar gwamnatin tarayya wajen shawo kan wannan batu, tare da kira ga ci gaba da hulda ta diflomasiyya da tattaunawa tsakanin Najeriya da Amurka. Kungiyar ta sake jaddada kudirinta na gaskiya, zaman lafiya, da hadin kai tsakanin addinai, tana mai kira ga ’yan Najeriya su kasance masu juriya, kishin kasa, da fata mai kyau a yayin fuskantar kalubalen kasa.

Signed: Sheikh Dr Abdullahi Bala Lau
National Chairman Jibwis Nigeria

Jibwis Nigeria

Address

Behind Rest House NASSARAWO
Numan

Telephone

+2348064158773

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NUMAN 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to NUMAN 24:

Share