Filin Muhawara

Filin Muhawara kukasance damu dan samun ingantattun labarai da ɗumi ɗuminsu da tallatamuku kasuwancinku da manufofinku da aikace aikacenku advertising marketing's agency

SIYASA RIGAR ANCI              tafiya saida jagora adalin jagora ɗaya ake samu ajihaa Yobe ma ɗayane
09/05/2025

SIYASA RIGAR ANCI

tafiya saida jagora
adalin jagora ɗaya ake samu ajiha
a Yobe ma ɗayane

07/05/2025

SIYASA SIYASA SIYASA SIYASA

siyasar yobe akwai ƙalubale

Gamayyar Ƙungiyoyi Sama Da Talatin Da Ke Shirin Fita Zanga-Zanga A Jihar Kogi Sun JanyeMu kungiyoyin fararen hula a kark...
27/07/2024

Gamayyar Ƙungiyoyi Sama Da Talatin Da Ke Shirin Fita Zanga-Zanga A Jihar Kogi Sun Janye

Mu kungiyoyin fararen hula a karkashin kungiyar Concerned Civil Society Organisations a jihar Kogi muna son yin kira ga ‘yan Najeriya musamman matasan jihar Kogi da kada su shiga cikin kiran da ake yi na zanga-zangar kasa a Najeriya. Mun ga hakan ya zama wajibi da kuma abin damuwa wajen ba ‘yan Najeriya da matasan Kogi musamman wajen musu nasihar kada su amsa kiran duk wata zanga-zanga a ko’ina a fadin jihar.

The Concerned Civil Society Organisation a jihar Kogi, hadaddiyar kungiyar matasa sama da talatin ne, kungiyoyin mata, masu sana’a da kungiyoyin farar hula, muna so mu bayyana cewa duk da yake hakkin kowane dan kasa ne ya yi zanga-zanga, dole ne kuma a yi la’akari da muhimman abinda ya dace. A kaucewa baragurbi wanda yakan kai ga halaka mutane da dukiyoyi kamar yadda aka shaida a karshen zanga-zangar ENDSARS.

Mun nemi sanin wadanda ke da hannu a wannan zanga-zangar, saboda fargabar da muke, har ya zuwa yau, ba a gano wani ko gungun jama’a da ke kiran wannan zanga-zangar ba, kuma wasu marasa kishi da fuska biyu za su iya jagorantar mu don mu yi zanga-zangar. Har ila yau, yana da mahimmanci mu yi la'akari da cewa dole ta wata fuskar ya kamata a zargi gwamnati mai ci gaba daya a wahalan da ake ciki a halin yanzu.

A yau ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya cika shekara daya da wata daya da kwana ashirin da hudu a kan karagar mulki a matsayin shugaban kasa, don haka ya dace a ba shi lokaci domin ya juya al’amura. A bayyane yake kuma gaskiya ne cewa tattalin arzikin Najeriya yana cikin wani yanayi mara kyau kuma yana tafiya ta hanyar dawo da martaba, al'ummar kasar na shiga wani lokaci mafi tsanani a tarihi, amma zanga-zangar ba ita ce mafita ga matsalarmu nan take ba, sai dai mu cigaba da shiga cikin gwamnati tare da tattaunawa da gwamnatin ta hanyar da ta dace.

’Yan uwa Matasan Jihar Kogi, Najeriya ba za ta iya dakatar da ayyukanta na tattalin arziki gaba daya ba, saboda wadannan tsare-tsare da ake shirin yi domin kasar, ba za ta iya farfadowa daga illar da ake shirin yi ba, kasashe irin su Sudan, Libya da Yemen sun lalace gaba daya har zuwa yau sakamakon rikicin 'yan kasa suna tada tarzoma ga gwamnatocinsu. Najeriya ba za ta iya daukar irin wannan halin ba, dole ne mu ci gaba da yin kira ga talakawa ta yadda ba zai zama mun kara wa ƙasar wahalhalu da abin da take ciki ba.

Sai dai kuma muna son jawo hankalin Gwamnati da ta gaggauta magance wadannan abubuwa kamar haka:

1- Magance hauhawar farashin da ya tashi daga 22.8 a 2023 zuwa 34.2 a Yuni 2024.
2- Kawo ƙarshen rashin tsaro a Najeriya.
3- Tabbatar da isasshen abinci ga 'yan Najeriya ta hanyar kare gonakanmu.
4- Sake dawo da farashin kuɗin makaranta na ɗalibanmu da ke karatu a manyan makarantu.
5- Dawo da farashin wutar lantarki.
6- abunta matatun mai don samun ƙarfin aiki mai inganci.
7- Rage farashin gudanar da gwamnati a duk matakai. Idan aka yi la'akari da abubuwan da ke sama za su dawo da Najeriya kan hanyar ci gaba da wadata.

Gwamnonin jihohi a Najeriya suma dole ne su tashi ta hanyar zuba jari cikin aikin gona da tsaro musamman yadda aka gani a Jihar Kogi da Gwamna Ahmed Usman Ododo wanda ya nuna ƙoƙari don ɗaukar Jihar Kogi zuwa alkibla. Muna nanata cewa idan duk jihohi za su zuba jari cikin samarwa fiye da cinye, to tattalin arziki zai sake dawowa da ƙarfi.

Sa hannu
Abubakar Onimisi

Yayin ganawar ta yammacin Alhamis, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce masu ɗaukar nauyin zanga-zanga mutane ne da s**a ...
26/07/2024

Yayin ganawar ta yammacin Alhamis, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce masu ɗaukar nauyin zanga-zanga mutane ne da s**a ɗora masalaharsu sama da ta ƙasar.

Jagoran Malaman, Sheikh Bala Lau ya ce za su ci gaba da taimaka wa ƙasar da addu'o'i da kuma wayar da kan mutane.

Zanga-Zanga ba shine mafita ba Majalisar Wakilai ta Nąjeriya ta buƙaci DSS su gayyaci masu shirya zanga-zanga kan tsadar...
22/07/2024

Zanga-Zanga ba shine mafita ba Majalisar Wakilai ta Nąjeriya ta buƙaci DSS su gayyaci masu shirya zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Najeriya

A cewar Majalisar bai kamata a zura ido a bari yan Najeriya su yi irin yadda yan ƙasar Kenya s**a yi ba wanda ya riƙide ya jawo wa ƙasar ta shiga ruɗani a yanzu haka, anyi äŝąrar râyųķã da dukiyoyi, an kori ministoci da jiga-jigan Gwamnati amma kuma duk da haka babu wata biyan buƙata da aka samu

"Don haka zanga-zanga ba zai zama mafita ba ya zama wajibi a dakatar da ita tun da wuri" -inji yan majalisar.

Me zaku ce?

Kungiyar wasu matasa daga yankin Arewa ta Tsakiya ta fasa shiga cikin zanga-zangar da aka shirya kan tsadar rayuwa a Naj...
21/07/2024

Kungiyar wasu matasa daga yankin Arewa ta Tsakiya ta fasa shiga cikin zanga-zangar da aka shirya kan tsadar rayuwa a Najeriya - Karin bayani a sashen sharhi.

Tsadar rayuwa ta sanya wasu mutane fara amfani da wasu kayan miya a madadin tumatur wajen dafa jar miya.Ko kun gwada haɗ...
21/07/2024

Tsadar rayuwa ta sanya wasu mutane fara amfani da wasu kayan miya a madadin tumatur wajen dafa jar miya.

Ko kun gwada haɗa miyarku da cucumber ko kankana?

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris, wanda ya bayyana hakan a hirarsa da BBC, ya ce gwamnatin Bola Tinubu ta ...
20/07/2024

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris, wanda ya bayyana hakan a hirarsa da BBC, ya ce gwamnatin Bola Tinubu ta ɓullo da motoci masu amfani da iskar gas ta CNG domin sauƙaƙa sufuri.

A daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke cewa sun gaji da alƙawarin gyara matatun man ƙasar, a yanzu dai shugaban kamfanin N...
18/07/2024

A daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke cewa sun gaji da alƙawarin gyara matatun man ƙasar, a yanzu dai shugaban kamfanin NNPCL, Mele Kyari ya bayyana lokacin da matatar man fetur ta Fatakwal za ta soma aiki.

A baya an sha sanar da lokacin da matatun ƙasar za su soma aiki amma ba a cimma tsarin da aka shirya.

Turkiyya da Nijar suna tattaunawar ƙulla ƙawancen soji da tattalin arziki
17/07/2024

Turkiyya da Nijar suna tattaunawar ƙulla ƙawancen soji da tattalin arziki

Hakan na nufin Gwamna Abba Kabir Yusuf ya mayar da Aliyu Ibrahim Abdulkadir kan karagarsa ta Sarkin Gaya, amma wannan ka...
17/07/2024

Hakan na nufin Gwamna Abba Kabir Yusuf ya mayar da Aliyu Ibrahim Abdulkadir kan karagarsa ta Sarkin Gaya, amma wannan karon a matsayin mai daraja ta biyu.

Gwamnatin Abba Gida-Gida ta ce jama'ar Kano sun ji dadin hukuncin tabbatar da rushe masarautu. Karanta karin bayani a sa...
16/07/2024

Gwamnatin Abba Gida-Gida ta ce jama'ar Kano sun ji dadin hukuncin tabbatar da rushe masarautu. Karanta karin bayani a sashen sharhi.

Address

Liman Abdullahi Street Bolewa'A Ward
Potiskum
622101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Filin Muhawara posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Filin Muhawara:

Share