AABC News

AABC News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AABC News, Media/News Company, Potiskum.

Musa Musa Yakubu(El-Yakub Shuraim)SHIN KO KUN SAN NAU'IN CUTAR DA TAYI SANADIYYAR KWANTAR DA BUHARI A ASIBITIN BIRNIN LA...
03/07/2025

Musa Musa Yakubu
(El-Yakub Shuraim)

SHIN KO KUN SAN NAU'IN CUTAR DA TAYI SANADIYYAR KWANTAR DA BUHARI A ASIBITIN BIRNIN LANDAN?

A Najeriya, an wayi gari da rahotannin dake bayyana cewa an garzaya da tsohon shugaban Najeriya, janar Muhamamdu Buhari zuwa wani asibiti a birnin Landan dake Birtaniya.

Dama dai an kwana biyu ba'a ji ɗuriyar tsohon shugaban ba tun bayan komawarsa birnin Kaduna da zama bayan kwashe kimanin shekaru biyu a mahaifarsa ta Daura bayan saukarsa daga Mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

BBC ta ruwaito a shafinta na "Facebook" cewa "Malam Garba Shehu, da yake a matsayin tsohon mai taimakawa Muhammadu Buhari a fannin yaɗa labarai, ya shaida mata cewa "Buhari ya tafi Birtaniya ne domin duba lafiyarsa kamar yadda ya saba, amma daga baya sai ya kamu da rashin lafiya".

"Ina so in tabbatar muku cewa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari na rashin lafiya. Yana samun magani a Birtaniya.

"Idan kuka tuna, Buhari ya sanar da kowa cewa zaije duba lafiyarsa na shekara-shekara. Ya kamu da rashin lafiya ne a can, amma ina farin cikin sanar daku cewa yana samun sauƙi a yayin da ake ci gaba da jinyarsa", inda ya ƙara da cewa, "Muna addu'ar Allah Ya bashi cikakkiyar lafiya."

Sai dai kuma Garba Shehun bai bayyana irin rashin lafiyar da Buharin ke fama da ita ba a cewar BBCn, ko bayyana sunan asibitin da yake jinyar ba.

Sai dai BBCn tace "rahotanni na ruwaito wasu majiyoyi daga makusanta da iyalan tsohon shugaban na Najeriya cewa yana sashen kulawa da marasa lafiya na musamman a dalilin fuskantar rashin lafiya mai tsanani".

Musa Musa Yakubu(El-Yakub Shuraim)TSOHON SHUGABAN NAJERIYA, MUHAMMADU BUHARI, YA KAMU DA RASHIN LAFIYARahotanni na bayya...
02/07/2025

Musa Musa Yakubu
(El-Yakub Shuraim)

TSOHON SHUGABAN NAJERIYA, MUHAMMADU BUHARI, YA KAMU DA RASHIN LAFIYA

Rahotanni na bayyana cewa tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kamu da rashin lafiyar da har ya zuwa yanzu ba'a kaiga gano ko wace iriyar rashin lafiya bace.

Tsohon shugaba Buharin dai an kwantar dashi ne a ICU na ƙasar Landan a dalilin matsananciyar rashin lafiya da yake fama da ita.

Radiyo Najeriya Potiskum ta ruwaito cewa "Jaridar "The Cable" ta ruwaito daga "Empowered Newswire" cewa wani makusancin tsohon shugaban ya bayyana cewa Buharin ya kamu da rashin lafiyar ne a Landan yayin da tun asali yaje duba lafiyarsa".

A cewarta "rahoton yace an kwantar da Buhari a ɗakin ICU kafin daga bisani aka sallame shi a makon daya gabata".

Koda yake, bala bayyana irin nau'in cutar dake addabarsa ba, sai dai rahotanni sun nuna cewa yana samun sauƙi a Landan ɗin kuma ana sa ran zai dawo gida Najeriya da zarar ya samu sauƙi gaba ɗaya kamar yadda rediyo Najeriya ta fitar a shafinta na "Facebook".

02/07/2025
Musa Musa Yakubu(El-Yakub Shuraim)SHUGABAN ƘASAR AMURKA DONALD TRUMP YACE BAZAI NEMI SHUGABANCIN ƘASAR A WA'ADIN MULKI N...
02/07/2025

Musa Musa Yakubu
(El-Yakub Shuraim)

SHUGABAN ƘASAR AMURKA DONALD TRUMP YACE BAZAI NEMI SHUGABANCIN ƘASAR A WA'ADIN MULKI NA UKU BA

Donald Trump ya musanta cewa yana tunanin mulki wa'adi na uku. Wannan kuwa wani yunƙuri ne da masana s**a amince cewa an haramtata a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin ƙasar.

Yayin da yake bada amsar wata tambaya ta kafar watsa labarai na NBC da ɗan jarida Kristen Walker a ranar Lahadi, Trump ɗin yace: "Zan zama shugaban shekaru takwas. Nan gaba kaɗan zan sake kasancewa shugaba a karo na biyu. Koda yaushe ina kallon hakan a matsayin yunƙuri mai matuƙar muhimmanci".

Trump ɗin mai shekaru 78, a baya dai ya bayyana cewa tabbas "da gaske ya keyi" game da buƙatar kasancewa a karagar mulki karo na uku, dama na huɗu a matsayin shugaban Amurka.

Sai dai daga baya Trump ɗin yace an yaɗa maganganun nasa ne a matsayin ƙanzon kurege .

An ruwaito cewa kamfaninsa "The Trump Organization" ya riƙa sayar da wasu hulunan hana-sallah waɗanda aka rubuta "Trump 2028" a jiki wanda hakan ke alamta zai nemi shiga ofishi bayan kammala wa'adinsa a 2029.

A wata hira da aka naɗa a ranar Juma'a a gidansa dake Florida, Trump ɗin ya nuna yana da wasu buƙatu a wajen jama'a nasu mara masa baya a zaɓe mai zuwa.

"Trump ɗin yace: "Mutane da yawa suna buƙatata da "tazarce", wannan ya faru ne bayan kamar kwanaki 100 na farkon wa'adin mulkinsa na biyu.

"Wannan wani abu ne da a iya sanina, babu shi a kundin tsarin mulki a hanaka fita takara. Ban san ko kundin tsarin mulki s**a dogara dashi ba na cewa bani da damar sake neman karagar mulki ba", inda ya ƙara da bayyana cewa: "Akwai mutane da dama suna sayar da hular hana-sallah da wannan alama na 2028, bawai kamfanina ne kaɗai mai sayarwa.

"Amma wannan ba wani abu bane da nake neman hatsaniya akai," yayin da yake lissafo jerin sunayen ƴan jam'iyyar Republican waɗanda ke neman kujerarsa ta shugaban ƙasa dana mataimakinsa JD Vance dana sakataren ƙasar Marco Rubio.

Sai dai sauye-sauyen kundin tsarin mulkin ƙasar yace: "Babu wani mahaluƙi da za'a zaɓa zuwa ofishin shugaban ƙasa fiye da sau biyu".

A dokar ƙasar, sauya tsarin mulki zai buƙaci amincewar biyu bisa uku na majalisar dattijai data wakilai, har ma da amincewa daga kashi uku na gwamnatocin jahar.

Koda yake, wasu magoya bayan Trump na bayyana cewa, akwai wasu tsare-tsare a cikin kundin tsarin mulki, waɗanda ba'a jarrabasu a kotu ba.

NBC ta tambayeshi ko akwai wanda ya kusance shi da waɗannan bayanai, sai Trump yace, "a damar kasancewa babban mai goyon baya, mutane da yawa sun bayyana ra'ayoyi daban-daban".

A yayin tattaunawar, Trump ya kuma yi watsi da zargi da matsalar tattalin arziƙin ƙasa.

Ya ce, "E, komai yayi kyau," yace bayan jadawalin kuɗin fito na jirgin saman duniya ya jagoranci tattalin arziƙin ƙasashen Amurka, an samu tazgaro a karon farko tun shekarar 2022.

Ya ƙara da cewa, "Nace, wannan zamani ne na sauyi. Ina tsammanin za muyi abin mamaki."

Yayin da aka tambayeshi, ko tattalin arziƙin Amurka na iya ci gaba ko kuma wani abu daban na iya faruwa? Sai yace: "Amma ina tsammanin zamu sami tattalin arziƙi mafi girma a tarihin ƙasarmu."

Daga baya ya ƙara da cewa, "akwai damar da ke binciken cewa na din-din-din na iya zama na din-din-din."

Har ila yau, Trump ya kuma musanta cewa Amurkawa zasu buƙaci shirin kota-kwana don hasashen ƙarancin kayan siyarwa a shagunan ƙasar, yayin da yaƙin kasuwanci yaci gaba: "A'a, ban faɗi haka ba. Ina cewa basa buƙatar samun wannan.

An tambayi Trump game da kwaskwarima na biyar dake a ƙarƙashin doka wanda ke tabbatar da wasu haƙƙoƙi ga mutanen da s**a zargi aikata laifi.

Masharhanta sunce shirin da aka ɗora shi ya keta wannan tsari, kuma cewa gwamnatinsa ta cire mutanen da ba'a doki kowa da wani laifi ba, saboda haka basu da wata dama ta gabatar da tsaron doka.

"Yayin tambayar Trump ɗin da yayi, Walker yace: "Baka buƙatar aiwatar da kundin tsarin mulkin Amurka a matsayin shugaban ƙasa?" yana nuna cewa zai iya yin watsi da ofishin shugaban ƙasa, wanda ya buƙace shi daya kiyaye tare da kare kundin tsarin.

A watan da ya gabata, Kotun ƙoli ta yanke hukuncin cewa "Fadar White House ta aika batun dawo da ɗan gudun hijira da cikin rashin sa'a aka turashi zuwa kurkuku a El Salvador. Gwamnatin ta Trump tace sun rasa ikon tilasta ƙasar Amurka ta dawo da shi ga Amurka.

Trump yace shi zai iya fitar da mutum da aka kora idan yaso.

An kuma tambayi Trump game da yanke shawarar bayyana dokar shige da fice a ranar farko a ofishinsa".

"Muna da madaidaicin iyaka da tabbatacce," yace, ya jagoranci mai ɗaukar hoto don me yasa shaidar ta ofis ta nuna cewa ba bisa ƙa'ida ba ta zama mafi ƙarancin matakai a shekarun da s**a fi ƙaranci. Yayi da'awar cewa gaggawa yana cikin tsarin kotun, ba'a kan iyakar ba.

"Babbar gaggawa a yanzu itace cewa muna da dubban mutane da muke son su fitar, kuma muna da wasu alƙalai da suke son kowa da kowa don komawa kotu."

"Yana da ban sha'awa gabaɗaya kan shige da fice," Trump yaci gaba da gayawa NBC, cewa bashi da shirin ɗauke doka da oda a nan gaba.

28/06/2025

Musa Musa Yakubu
(El-Yakub Shuraim)

Yayin da guguwar siyasa ke sake dannowa, jam'iyyu da dama ne ke ɗaura ɗamarar jan daga da sauran takwarorinsu.

AABC tayi hira da Shetiman malaman fadar mai martaba sarkin Fika kuma daraktan makarantar samar da ilmin zamantakewa a tsakanin ma'aurata, Mal. Abdurrazzaƙ Abdullahi Usman, kuma ga yadda hirar ta kasance:

YADDA MAKARANTAR MADINATUL HUDA TA GUDANAR DA BIKIN YAYE ƊALIBAIƘaramar hukumar Pataskum na jihar Yobe na ɗaya daga ciki...
28/06/2025

YADDA MAKARANTAR MADINATUL HUDA TA GUDANAR DA BIKIN YAYE ƊALIBAI

Ƙaramar hukumar Pataskum na jihar Yobe na ɗaya daga cikin jerin ƙananan hukumomi da su kayi fice a fannin mahaddata Alƙur'ani. Garin cike yake da manyan malamai masana ilmin addini dana zamani wanda wannan na ɗaya daga cikin dalilan da s**a sabbaba yawaitar makarantu a cikinta a fannoni daban-daban.

Makarantar Madinatul-Huda ɗaya ne daga cikin ɗumbin makarantun dake cikin garin na Pataskum kuma a karo na farko tayi gamo-da-katarin yaye wasu daga ɗalibanta bayan shuɗewar wasu ƙididdigaggun shekaru tana basu horo a fannonin ilmuka da dama.

Ustaz Muhammad Musa Hussaini shine shugaban makarantar kuma a hirarsa da kafar yaɗa labarai ta AABC ya yabawa sauran malamai kan namijin ƙoƙari da jajircewarsu wanda hakan shine ginshiƙin kaiwa ga waɗannan nasarori, sai dai ya fara ne da bayyana farin cikinsa da cewa: "Gaskiya kam muna cikin matuƙar farin ciki da miƙa godiya ga Allah, duba da yadda muka fara wannan karatu tsawon shekaru masu yawa kuma har Allah Ya tabbatar aka samu wannan gagarumar nasara ɗin, gaskiya muna cikin farin ciki sosai-sosai". Kana shugaban yaci gaba da cewa: "Wannan shine karo na farko da makarantar ta taɓa shirya gudanar da wannan al'amari".

Har ila yau, malam Musa Hussaini ya buƙaci haɗin kai da goyon bayan iyayen ɗalibai wajen inganta karatun yaran: "Abu na farko dai ya kamata iyaye duk lokacin da muke abubuwa na makaranta su zo mu zauna dasu su bamu shawara mu tattauna matsaloli dasu, to wannan zai kawo abubuwa na ci gaba sosai abin daya shafi makaranta da kuma karatun yaran gaba ɗaya, duba da su sun san halayyarsu a gida mu mun san halayyarsu a makaranta, don haka muna neman goyon bayan iyaye wajen wannan abin".

A ɓangare guda kuma, yayin da shugaban a jumlace yake bayanin jan hankalin ɗaliban baki ɗaya da kuma waɗanda ake bikin yaye su a keɓe, sai ya kada baki yace: "Ina jan hankalin waɗannan ɗalibai da su kayi wannan hadda musamman waɗanda s**a yi na yanzu wanda karatu ne s**a yi a matakin farko suna yi suna biyan hadda wanda daga baya ba'a samu haddarsu duka ba aka dai yi sauƙa da abinda yake hannu wanda dukansu bai wuce a samu izu talatin ko arba'in wadda yake hadda ba, shi yasa ma mamallakin makaranta yace ayi sauƙar nazari don haka ina basu shawara yanzu ne s**a share hanyar tafiya su zauna suyi karatu su karanta Ƙur'ani. Sannan masu zuwa su maida hankali saboda shi Ƙur'ani yana da buƙatar a maida hankali, sannan sai an bada lokaci za'a iya haddacewa".

Kana daga ƙarshe cikin bayanansa, shugaba Hussaini ya sake yiwa Allah godiya da kuma gabatar da addu'o'i na alheri ga ɗaliban da kuma makarantar: "To daga ƙarshe fatan da zanyi mana shine muna godiya ga Allah da kuma Allah Ya tabbatar damu akan wannan turba ta addinin Musulunci da muka zama daga cikin makaranta Ƙur'ani kamar yadda Annabi SAW yace: "Khairukum man ta'allamal Ƙur'an, wa allamah". Allah Yasa aiyukan da muke yi karɓaɓɓene sannan kuma muna fatan Allah Ya tabbatar damu a wannan turba ta Ƙur'ani".

A tattaunawar da tayi da wasu daga cikin ɗalibai da ake bikin yaye su, AABC tayi hira da wata mai suna Hauwa Musa Yerima kuma ta bayyana farin cikinta da cewa: "A gaskiya yau farin cikina bazai misaltu ba saboda in aka ce ma Ƙur'ani yau ka kammala gaskiya ba abinda zance wa Allah SWT sai dai in gode maSa, kuma Allah Ya yiwa rayuwarmu albarka, kuma Allah Yasa Ƙur'ani ya cece mu ranar gobe ƙiyama".

A bayananta na ƙarshe, Malama Hauwar tayi kyakkyawar fata ga iyayensu, dukkan malamai da kuma su kansu ɗaliban: "Fata na a garesu shine, mudai da farko muna musu godiya Allah Ya saka da alkairi! Jajircewa da s**a yi a kanmu Allah Ya biya su don ba zamu iya biyansu da komai ba. Sannan iyayenmu ma da s**a bamu dama s**a bamu ƙwarin gwiwa Allah Ya saka musu da alkairi gaba ɗayansu dasu da malaman Allah Ya saka musu da gidan aljannah".

Har ila yau, AABC ba tayi ƙasa a gwiwa ba wajen garzayawa wajen wata ɗalibar cikin masu sauƙa mai suna Hussaina Abubakar Aliyu: "Lalle na gabatar da maƙala akan muhimmancin Alƙur'ani ga rayuwar ɗan Adam a duniyarsa da kuma lahira. Sannan nayi sha'awar gabatarwa akan wannan maudu'i ne saboda in faɗakar da iyayenmu da ƙannenmu da yayunmu waɗanda s**a halarci wannan taro domin su samu ƙwarin gwiwar sa yaransu kuma su tilasta musu suyi ƙoƙari wajen karanta Alƙur'ani dama littattafan da s**a biyo bayan Alƙur'ani. Saboda Alƙur'ani nada matuƙar muhimmanci kuma sannan muna sa ran zai cecemu ranar gobe ƙiyama shi yasa na karɓi wannan maudu'i dan na gabatar kuma alhamdulillahi saƙo ya isa inda ake so ya isa".

Kana nan take wakilin AABC Musa Musa Yakubu El-Yakub Shuraim ya sake nausawa ga wasu gungun ɗaliban inda yayi kaciɓus da wata ɗalibar: "Sunana A'isha Adamu Hassan. Haƙiƙanin gaskiya ina godiya ga malamanmu. Sunyi ƙoƙari sun jajirce da-muje-da-kar-muje ba-dare-ba-rana babu safiya babu damina. Malamai ne waɗanda basu yi mana karatu don kuɗi ko don wani abu ba, saboda in da don kuɗi ne ba zasu taɓa tsayuwa a garemu ba, don lokacinsu mai tsada suke sadaukar mana. Lokaci ne na asuba wanda yafi daɗin bacci ga kowane ɗan adam amma s**an hana idansu bacci har ma s**an rigamu zuwa sai dai muje mu same su suna jiranmu, kuma s**an jure ɗaci da raɗaɗin dukkanin abubuwan da muke musu har kawowa ga wannan mataki, lalle muna godiya a garesu Allah Ya saka musu da alkairi kuma ina fatan Alƙur'ani ya cecemu ranar tashin alƙiyama kuma ina fatan Alƙur'ani ya zama hujja a garemu ba akanmu ba. Sannan ina jan hankalin ƴan uwana ɗalibai su zage dantse su tsaya akan karatun Alƙur'ani da sauran littattafai saboda sune gatanka na lahira da kuma duniya baki ɗaya. Saboda in kana da Alƙur'ani babu littafin da ba zaka iya karantawa ba. Koda karatun boko kake yi in ka dubi wanda ya haɗa bibbiyu boko da kuma Arabiyya zaka kalli tashi fahimtar tasha ban-ban da wanda ya riƙi ɗaya zalla, bawai don mun kushe wancan ba sai dai don ita wannan ɗin ta musammance, Allah Yasa mu dace. Allah Ya kyautata ƙarshenmu".

A nasa jawaban, mamallakin makarantar, Shaikh Abdurrahman Ahmad, ya yiwa ɗaliban fata na gari amma ya fara ne da yiwa mahukunta makarantar yabo bisa bajintar da s**a nuna har aka kaiga wannan mataki: "Muna godiya ga Allah SWT, muna kuma yiwa waɗannan ɗalibai fatan Allah Ya sanyawa karatunsu albarka. Kuma akwai waɗanda akayi ta faɗi-tashi dasu wajen karantarwa a wannan makaranta waɗanda ba zamu taɓa mantawa dasu ba har yanzu kuma ana tare suna bada gudunmowa kamar irinsu Malam Muhammad dasu shaikh Salis da saura daga cikin ɗalibai mata waɗanda har yanzu ana yi dasu da kuma wasu ɗaliban da a halin yanzu sun zama malamai anan muna fatan Allah Ya sanya musu da kuma wannan makaranta tamu albarka da dukkanin sauran makarantun Islamiyya. Baƙinmu da s**a halarto wannan wuri Allah Yasa yadda s**a zo lafiya Allah Yasa kowa ya koma makomarsa cikin farin ciki, was salamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh".

Musa Musa Yakubu(El-Yakub Shuraim)GIDAUNIYAR "CHARITABLE FOUNDATION" TA GUDANAR DA GASAR KACI-CI-KACI-CI NA GORON SALLAR...
28/06/2025

Musa Musa Yakubu
(El-Yakub Shuraim)

GIDAUNIYAR "CHARITABLE FOUNDATION" TA GUDANAR DA GASAR KACI-CI-KACI-CI NA GORON SALLAR WANNAN SHEKARAR

Kamar yadda gidauniyar ta saba gabatarwa a kowace shekara yayin bukukuwan sallar Layya, wannan karon ma ta gabatar da gasar a babban ɗakin taron "Multi purpose" dake Kwalejin ilmi, fasaha da koyon ƙere-ƙere na tarayya dake ƙaramar hukumar Pataskamu.

Koda yake, gidauniyar da cibiyar tata ke ƙaramar hukumar ta Pataskamu a jihar Yobe, ta faro shirye-shiryen nata na baya ne da gudanar da gasar karatun Alƙur'ani mai girma, sai dai a wannan karon ta sauya tsarin shirye-shiryen nata ne zuwa gabatar da gasar kaci-ci-kaci-ci wajen sanin ilmummukan dake taimakawa akan sanin ma'anonin Alƙur'ani.

Kafar watsa labarai ta AABC Hausa ta ruwaito cewa: "A wata amsar tambayar daya bayar, shugaban gidauniyar Ustadz Suhailu Musa Ɗahiru yace: "Manufar kafa gidauniyar itace dawo da hankulan ɗalibai mahaddata Alƙur'ani daga ɗebe hankulansu da wasu shirye-shirye na raye-raye, kaɗe-kaɗe da guje-guje da ake gudanarwa a lokutan bukukuwan sallolin Azumi da Layya s**a yi".

Shugaban yace: "Mafi akasari zaka ga ƙarfin haddar ɗalibai yana samun rauni a dalilin halartar wasu taruka da ake gabatarwa a bukukuwan salla wanda suna halarta ne a rashin wasu taruka masu amfanarwa da s**a shafi harkokin addini", inda yaci gaba da cewa, "ganin haka ne yasa muma muka ɓullo da wannan shirin. Domin idan akwai shirin daya shafi addini, to su ɗaliban ba zasu halarci waɗancan tarukan shirmen dake kawo musu koma bayan karatun Alƙur'aninsu ba".

Koda na tambayeshi ta kafar manhajar WhatsApp kan dalilin da yasa gidauniyar tayi turjiya ga barin gudanar da gasar akan abin daya shafi haddar Al'ƙur'ani mai girma, sai shugaba Ɗahirun yace: "To dalili shine, lalle mun ɗauki tsawon shekaru uku muna gabatarwa akan haddar Alƙur'ani mai girma, to amma kasan yau da gobe idan kana aiwatar da wani shiri, zaka riƙa cin karo da sabbin ci gaba da kuma wasu matsaloli da ka iya ɓullowa tare da samun hanyoyin magancesu. Don haka, mun lura da cewa galibi makarantu da duk wasu cibiyoyi da suke gabatar da gasa s**an gabatar ne akan haddar Alƙur'ani. Sannan alhamdulillahi, a nazarinmu mun gano cewa a yanzu an samu abinda ake buƙata na yawan mahaddata Alƙur'ani a garin Pataskamu. A dalilin haka muka ga ya kamata mu faɗaɗa manufar tafiyar zuwa ga ilmantar da yara sanin ilmin ma'anonin Alƙur'ani mai girma, tunda bayan hadda ɗin yana da kyau ɗalibi ya san cewa akwai wani sabon abu kuma daya kamata ya sani dangane da Alƙur'ani ba wai ya ɗauka cewa don ya kai matakin kammala haddar Alƙur'ani kuma shike nan ba".

Shirin Taskar labarai na gidan rediyon tarayya Sunshine FM na garin Pataskamu ya ruwaito cewa: "Taron ya samu halartar makarantu 11 daga cikin 15 da aka gayyata, inda ƴan takara 31 s**a samu damar fafatawa".

Har ila yau, kafar labaran AABC, a bayanin data wallafa a shafinta na Facebook tace: "Shugaban gidauniyar, Ustadz Suhailu Musa Ɗahiru ya bayyana cewa: "Tun kafa gidauniyar mun gabatar da gasar haddar Alƙur'ani mai girma har karo uku a jere a kowace shekara, inda a karo na farko muka gabatar da gasar bayan kammala "Daura" a masallacin Juma'ar da ake kira masallacin Waziri, inda muka samu ƴan takara daga matakin izu 3 zuwa na izu 40. A shekarar data kewayo kuma wacce itace karo na biyu, mun gabatar ne a babban ɗakin taron dake sakatariyar ƙaramar hukumar Pataskamu, shima mun samu ƴan takarkaru daga matakin izu 3 har zuwa na 40. Sai kuma karo na ƙarshe wanda daga shine muka sauya tafiyar daga tsarin gasar haddar Alƙur'ani zuwa tsarin gasar kaci-ci-kaci-cin sanin ilmin ma'anonin Alƙur'ani. Shi kuma mun gabatar da shine a ɗakin taro na IBB dake kwalejin tarayya na garin Pataskamu, inda muka samu ƴan takarkaru daga izu 3 har zuwa izu 60 kuma haƙiƙa muna yiwa Allah godiya bisa wannan ni'imar domin Alhamdulillahi muna samun nasara".

A tsarin gudanar da gasar, gidauniyar kan gabatar da gayyata ne ga makarantun dake garin na Pataskamu bisa buƙatar ƴan takarkaru 2 a kowane izu da gidauniyar ta buƙata gwargwadon girma ko ci gaban makaranta.

Haka kuma, gidauniyar ta tsara gasar kaci-ci-kaci-cin ne bisa tsarin rukuni-rukuni. Rukunin A, rukunin B da kuma rukunin C tare da shirya tambayoyi 60 inda ta raba tambayoyin 60 zuwa gida 3, ya kasance tambayoyi ashirin-ashirin ga kowane rukuni, sannan ta gabatar da tambayoyi 20 izuwa ga kowane rukuni daga rukunnan na A, B da kuma C inda kowane ɗan takara zai amsa tambayoyi daga jerin tambayoyin da aka gabatarwa rukuninsa.

A sakamakon gasar, ƴan takara 2 ne s**a yi ragas s**a zamto gwarazan shekara. Waɗannan ɗalibai sune Asiya Usman Ibrahim daga makarantar Al-Minnah International Academy dake unguwar "Tandari" wacce kuma ta fito daga rukunin "A". Ɗalibar ta samu nasarar zuwa na ɗaya ne da jimillar maki 400 inda ta samu makin na abareji 100. Sai kuma ɗaya ƴar takarar Maryam Abdullahi Adamu da tazo daga makarantar Mu'assasah Adamu Idi dake unguwar "Central" wacce ita ma ta fito daga rukunin na "A" ta kuma kasance na 1 da maki 400 inda ita ma ta samu jimillar maki 100 bisa tsarin abareji.

Gasar ta samu halartar ƴan takarkaru 31 da s**a fafata inda ɗalibai 2 su kayi kunnen doki a lamba na 1, sai lamba na 2 da aka samu ɗalibi 1, kana lamba na 3 kuma aka samu ɗalibai 3 dasu kayi kunnen doki. Haka kuma lamba na 4 ƴan takara 3 ne su kayi ragas a yayin da aka samu ɗalibi 1 da yazo na biyar shi kaɗai a lamba na 5.

Wannan gasar ta gudana ne ƙarƙashin alƙalancin Mallam Shaikh Rabi'u Alhaji Abdullahi; shugaban alƙalai, Mallam Ibrahim Haruna Musa; sakatare, Ustadz Abubakar Z***r Yarima, Ustadz Anas Abdullahi Maikuɗi, Mallam Alhassan Saleh; mai lura da lokaci.

A bayanin da AABC ta fitar, "Gidauniyar an assasata ne a 1st, Agusta, 2022 kuma daga wannan lokacin ta riƙa gudanar da muhadarori a duk hutattakin da gwamnati ta riƙa bayarwa na makarantu. Gidauniyar tace ta gabatar da muhadarori akan ilmin Tajwidi musamman kan abin daya shafi "Tafkhimi da kuma Al-Ghunna".

28/06/2025

Address

Potiskum

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AABC News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share