YOBE News FORUM

YOBE News FORUM Barka da zuwa YOBE News FORUM
Amintacciyar majiyar labarai, nazari da rahotanni masu inganci daga Yobe, Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

Muna aiki da gaskiya, daidaito da amincewa. Ku biyo mu domin samun labarai a kan lokaci.

🔴 PROFESSORIAL THINKING YA FI SIYASAR MAGANGANU ƘARFI — GajiWani jigo a harkar siyasa, Gaji, ya bayyana cewa bambancin ƙ...
02/05/2026

🔴 PROFESSORIAL THINKING YA FI SIYASAR MAGANGANU ƘARFI — Gaji

Wani jigo a harkar siyasa, Gaji, ya bayyana cewa bambancin ƙuri’u 711 ba alamar rauni ba ce, sai dai nuna cewa an yi gasa mai ƙarfi sosai. A cewarsa, zaɓe ba a tantance shi da yawan ƙuri’u kaɗai ba, domin dabaru, tsari, tasiri da ƙarfin gindin jama’a su ne ke tabbatar da nasara.

Ya ƙara da cewa jam’iyyu ba sa zaɓar ‘yan takara bisa tausayi ko son rai, sai dai suna yin lissafi da nazari mai zurfi kafin yanke hukunci.

Gaji ya jaddada cewa shugabanci ba wai game da wanda ya kusa faɗuwa ko wanda ya yi nasara da ƙyar ba ne, amma game da wanda ke da basira, iya warware matsaloli, da kuma kawo sakamako mai anfani ga al’umma.

A ƙarshe, ya buƙaci a karkatar da hankali daga batun ƙuri’u zuwa batun ƙwarewa da cancanta, yana mai cewa duk wani abu dabam “hayaniya ce kawai.”

🔴 Sanata Bomai Ya Yi Allah-Wadai da “Yobe Consensus”, Ya Ce Ba Bisa Ka’ida Ba NeSanata Ibrahim Mohammed Bomai ya bayyana...
02/05/2026

🔴 Sanata Bomai Ya Yi Allah-Wadai da “Yobe Consensus”, Ya Ce Ba Bisa Ka’ida Ba Ne

Sanata Ibrahim Mohammed Bomai ya bayyana rashin amincewarsa da abin da ake kira “Yobe Consensus”, inda ya ce matakin ya sabawa doka tare da tauye tsarin dimokuradiyya a Jihar Yobe.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Sanatan ya zargi wasu da yin gaggawar ayyana dan takarar hadin kai tun kafin karewar sayar da fom din takara na jam’iyyar APC, wanda a cewarsa hakan ya nuna an riga an kammala yanke hukunci ba tare da bai wa sauran masu neman takara dama ba.

🗳️ Ya tunatar da cewa jam’iyyar APC ta fara sayar da fom din Expression of Interest da Nomination tun daga ranar 25 ga Afrilu, 2026, tare da sanya ranar 4 ga Mayu, 2026 a matsayin ranar rufe sayarwa.

Sai dai ya ce ayyana “consensus” a ranar 29 ga Afrilu ya saba wa ka’idojin jam’iyya da kuma tsarin dimokuradiyya.

⚖️ Sanata Bomai ya kara da cewa:

Wannan mataki ya sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya

Ya ci karo da dokar zabe

Kuma ya saba da jadawalin INEC na zaben 2027

Ya jaddada cewa ka’idojin APC sun tanadi cewa dole ne: ✔️ A tantance duk masu neman takara
✔️ A samu yardar kowa cikin son rai
✔️ A rubuta amincewa kafin a cimma “consensus”

❗ A cewarsa, abin da ake kira “Yobe Consensus” bai bi wadannan sharudda ba, don haka ya zama abin da ya sabawa doka da adalci.

👉 Shin kai me kake tunani kan wannan batu? Ka bayyana ra’ayinka a sashen sharhi.

🔴 Muhawara Ta Kunno Kai Kan Tikitin Sanata a Yobe Bayan Maganar Sheriff AlmuhajirWani fitaccen mai sharhi kan harkokin s...
01/05/2026

🔴 Muhawara Ta Kunno Kai Kan Tikitin Sanata a Yobe Bayan Maganar Sheriff Almuhajir

Wani fitaccen mai sharhi kan harkokin siyasa, Sheriff Almuhajir, ya jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta bayan wata magana da ya wallafa a shafinsa na Facebook dangane da batun tikitin takarar Sanata a Jihar Yobe.

A cikin rubutunsa, ya bukaci jama’a da su yi nazari cikin natsuwa kan sakamakon zaben Sanatan Yobe ta Kudu na shekarar 2023, inda ya bayyana cewa:

*APC ta samu kuri’u 69,596

*PDP ta samu kuri’u 68,885

*Banbanci kuwa kuri’u 711 kacal

Ya jaddada cewa wannan zabe an gudanar da shi ne a yankin da ke da kananan hukumomi hudu kacal daga cikin 17 na jihar, lamarin da ke nuna yadda aka fafata sosai ba tare da tazara mai yawa ba.

Sheriff Almuhajir ya kara da cewa, idan har aka yi la’akari da irin wannan sakamako mai cike da kalubale, ya kamata jam’iyya ta yi taka-tsantsan wajen yanke hukunci kan wanda za ta bai wa tikitin takara. A cewarsa, akwai bukatar a duba karfin dan takara da yiwuwar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kuma yi tambaya mai jan hankali ga masu ruwa da tsaki a siyasa da cewa:

"Shin wace jam’iyya ce za ta dauki irin wannan hadari ta danne sauran ‘yan takara, ta bai wa mutum tikiti, alhali hakan na iya jefa ta cikin hadarin faduwa a zabe?"

Maganar tasa ta haifar da muhawara a tsakanin masu bibiyar siyasar Yobe, inda wasu ke ganin yana kokarin fadakar da jam’iyya kan muhimmancin zabar dan takara mai karfi, yayin da wasu ke kallon kalaman nasa a matsayin s**a ga wasu ‘yan siyasa.

A halin yanzu, jama’a na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan wannan batu, musamman yayin da shirye-shiryen siyasar 2027 ke kara daukar zafi a jihar.

🔴 Gagarumin Yunkuri: YG Bello Beneficiaries Sun Fara Tattara Kudi Domin Sayen Fom na House of RepsKungiyar YG Bello Bene...
01/05/2026

🔴 Gagarumin Yunkuri: YG Bello Beneficiaries Sun Fara Tattara Kudi Domin Sayen Fom na House of Reps

Kungiyar YG Bello Beneficiaries Forum ta kaddamar da wani gagarumin yunkuri na tara kudade domin sayawa YG Bello fom na tsayawa takarar kujerar Member, House of Representatives, matakin da ke kara jan hankali da haifar da zazzafar muhawara a tsakanin al’umma.

A cewar wasu daga cikin jagororin kungiyar, an fara wannan shiri ne domin nuna goyon baya da kuma godiya ga irin gudummawar da YG Bello ya bayar wajen tallafawa matasa da al’umma a fannoni daban-daban. Sun bayyana cewa manufar wannan yunkuri ita ce bai wa mutumin da s**a amfana da shi damar wakiltar su a matakin kasa.

Rahotanni sun nuna cewa tun bayan fara wannan kamfe na tattara kudade, an samu amsa mai karfi daga jama’a, fiye da yadda masu shirya shirin s**a yi hasashe. Mutane da dama daga cikin wadanda s**a ci gajiyar ayyukan YG Bello sun fito karara suna bayar da tasu gudummawa, tare da bayyana dalilan da s**a sa s**a yanke wannan hukunci.

Abin da ya fi daukar hankali shi ne yadda wannan yunkuri ya wuce iyakokin jiha, inda aka samu rahoton cewa mutane daga jihohi daban-daban na kasar nan suna turawa da gudummawarsu. Wasu daga cikinsu ma sun bayyana cewa ba su taba haduwa da YG Bello kai tsaye ba, amma sun gamsu da irin ayyukan alheri da s**a ji ko s**a gani daga wasu, wanda hakan ya sa s**a ga dacewar mara masa baya.

Wannan ci gaba ya kara tayar da sha’awa da hankalin jama’a, inda ake ganin ana samun karin goyon baya a kullum. A wasu wurare ma, matasa da kungiyoyi na shirya hanyoyi daban-daban domin fadakar da jama’a da kuma kara jawo hankalin masu son bada gudummawa.

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa irin wannan hadin kai da goyon bayan al’umma na nuni da yadda jama’a ke kara fahimtar muhimmancin zaben wakilai nagari, musamman wadanda s**a riga s**a nuna halayen taimako da kishin jama’a tun kafin neman mukami.

Duk da haka, wasu na kallon wannan yunkuri a matsayin wata sabuwar hanya ta nuna

🔴 Sanata Bomai Ya Zargi An Tafka Zagon Kasa ga Dimokuradiyya a Yobe”Sanata Ibrahim Mohammed Bomai ya bayyana cewa abin d...
01/05/2026

🔴 Sanata Bomai Ya Zargi An Tafka Zagon Kasa ga Dimokuradiyya a Yobe”

Sanata Ibrahim Mohammed Bomai ya bayyana cewa abin da aka rahoto na “nuna magajin Gwamna (SSG) daga tsohon Gwamnan Jihar Yobe” na nuna wata babbar matsala ga tsarin dimokuradiyya.

A cikin bayaninsa da ya wallafa a Facebook, Sanatan ya ce irin wannan mataki idan ya tabbata, zai zama tamkar cin zarafin tsarin dimokuradiyya da rashin bin ka’ida, domin yana nuna cewa mutum ɗaya ne zai iya yanke shawarar shugabancin miliyoyin jama’a ba tare da sahihin tsarin zaɓi ba.

Ya ƙara da cewa:
Irin wannan mataki ba ya da tushe a dimokuradiyya
Yana keta ka’idojin adalci da wakilcin jama’a
Yana rage rawar da jama’a ya kamata su taka a zaɓen shugabanninsu
Sanatan ya jaddada cewa Jihar Yobe mallakar al’umma ce, ba ta wani mutum ko ƙungiya ba, don haka dole ne shugabanci ya kasance bisa ra’ayin jama’a.

Ya kuma bayyana cewa zai ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen kare dimokuradiyya ta hanyar lumana da bin doka, tare da yin kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su kiyaye gaskiya da adalci a tafiyar da mulki.

A ƙarshe ya ce ba za a amince da duk wani nau’i na tilastawa, nuna wariya ko tauye haƙƙin jama’a ba.

🔴 YG Bello Beneficiaries Sun Taya Dr. Goje Murna, Sun Jinjinawa Gwamna BuniKungiyar YG Bello Beneficiaries Forum ta taya...
01/05/2026

🔴 YG Bello Beneficiaries Sun Taya Dr. Goje Murna, Sun Jinjinawa Gwamna Buni

Kungiyar YG Bello Beneficiaries Forum ta taya Dr. Muhammad Goje murna bisa nadin da aka yi masa a matsayin Mukaddashin Sakataren Gwamnatin Jihar Yobe.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar, inda ta kuma mika godiya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Yobe, Hon. (Dr) Mai Mala Buni, bisa wannan mataki da ta bayyana a matsayin mai muhimmanci ga cigaban matasa da jihar baki daya.

Kungiyar ta ce nadin Dr. Goje ya nuna yadda gwamnatin jihar ke baiwa matasa masu kwarewa da nagarta dama a harkokin shugabanci, tare da kara karfafa musu gwiwa wajen bada gudummawa ga cigaban al’umma.

Ta kara da cewa matasan Yobe za su ci gaba da mara baya ga manufofi da shirye-shiryen alheri na gwamnatin jihar domin tabbatar da dorewar cigaba.

A karshe, kungiyar ta yi addu’ar Allah (SWT) ya baiwa Dr. Muhammad Goje hikima da ikon sauke nauyin da aka dora masa.

Allah Ya albarkaci Jihar Yobe****Allah Ya albarkaci Tarayyar Najeriya 🇳🇬

✍️ *Daga:*YG Bello Beneficiaries Forum

28/04/2026

🔴 ’Yan Najeriya Sun Mayar da Martani kan Sabon Jadawalin Zaben 2027 da APC ta Fitar

Jam’iyyar APC ta fitar da sabon jadawalin zaben shekarar 2027 da aka gyara, lamarin da ya janyo martani daga sassa daban-daban na al’ummar Najeriya.

Rahotanni sun nuna cewa gyaran jadawalin ya shafi muhimman ranakun shirye-shiryen zabe, ciki har da lokacin tsayar da ‘yan takara da kuma gudanar da zabukan fidda gwani a cikin jam’iyyar.

Wasu ‘yan Najeriya sun bayyana goyon bayansu, suna mai cewa wannan mataki zai taimaka wajen inganta tsari da kuma tabbatar da gaskiya a harkokin zabe. Sai dai wasu kuma na ganin cewa akwai bukatar a kara bayyana dalilan da s**a sa aka yi wannan gyara, domin kauce wa rudani.

Masu sharhi kan siyasa sun ce irin wadannan sauye-sauye na iya yin tasiri ga shirye-shiryen jam’iyyun siyasa da ‘yan takara, musamman a daidai lokacin da ake tunkarar zaben 2027.

Ana sa ran jam’iyyar APC za ta ci gaba da bayyana karin bayani domin wayar da kan jama’a game da sabon jadawalin.
© Yobe News Forum

DA DUMI-DUMI: Bola Ahmed Tinubu Ya Yi Watsi da Bukatar Wasu Sanatoci Kan Basu Tikitin Takara Kai TsayeShugaban ƙasa, Bol...
23/04/2026

DA DUMI-DUMI: Bola Ahmed Tinubu Ya Yi Watsi da Bukatar Wasu Sanatoci Kan Basu Tikitin Takara Kai Tsaye

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙi amincewa da yunƙurin da wasu sanatoci s**a gabatar na neman a ba su tikitin komawa takara kai tsaye a zaɓe mai zuwa.

Rahotanni sun nuna cewa sanatocin sun nemi wannan dama ne domin sauƙaƙa musu hanyar sake tsayawa takara ba tare da shiga zaɓen fidda gwani ba, sai dai shugaban ƙasar ya nuna cewa dole ne a bi tsarin dimokuraɗiyya da jam’iyya ta tanada.

Me za ku ce?

DSS Ta Gurfanar da El-Rufa'i a Kotu!
23/04/2026

DSS Ta Gurfanar da El-Rufa'i a Kotu!

🔴 GOBE BUNI ZAI BAYYANA ƊAN TAKARAR GWAMNA NA 2027 A APC YOBEAna ci gaba da zaman jira da fatan ji daga bakin gwamnan ji...
22/04/2026

🔴 GOBE BUNI ZAI BAYYANA ƊAN TAKARAR GWAMNA NA 2027 A APC YOBE

Ana ci gaba da zaman jira da fatan ji daga bakin gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, yayin da ake sa ran zai bayyana sunan ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC domin zaɓen 2027.

Tun tuni dai aka daɗe ana jiran wannan lokaci, musamman ganin yadda ake samun ra’ayoyi mabanbanta a cikin jam’iyyar sakamakon yawaitar masu neman takara daga yankuna daban-daban.

A halin yanzu, an riga an fara samun rabuwar kai tsakanin mabiya jam’iyyar, inda wasu ke cewa “daga Buni sai Bomai”, wasu kuma na cewa “daga Buni sai Bade”, yayin da wasu ke tsayawa kan cewa “daga Buni sai abin da Buni ya faɗa” a matsayin nuna cikakkiyar biyayya ga shugabancin gwamnati.

Wannan yanayi na nuna cewa akwai gasa mai ƙarfi da kuma bambancin ra’ayi a cikin jam’iyyar, wanda ke ƙara ɗaga hankalin jama’a kan irin sunan da za a bayyana.

Masu sharhi na ganin cewa sanarwar da Buni zai yi za ta zama wata muhimmiyar alama da za ta bayyana ko waɗanda ke cewa “daga Buni sai abin da Buni ya faɗa” na da cikakkiyar biyayya, ko kuwa akasin haka.

Sai dai a gefe guda, wasu na fargabar cewa za a iya samun ɗan hargitsi ko rashin jituwa idan ba a zaɓi wanda suke goyon baya ba.

Yanzu dai idanu sun karkata ne zuwa gobe, domin jin wane mataki gwamnan zai ɗauka a wannan muhimmin lokaci.

YOBE News FORUM

🔴 CECE-KUCE TA KARA KARFI A APC YOBE KAN TAKARAR GWAMNAAna ci gaba da samun cece-kuce mai zafi a cikin jam’iyyar All Pro...
22/04/2026

🔴 CECE-KUCE TA KARA KARFI A APC YOBE KAN TAKARAR GWAMNA

Ana ci gaba da samun cece-kuce mai zafi a cikin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Yobe, dangane da batun fitar da ɗan takarar gwamna gabanin zaɓen 2027.

Rahotanni na nuni da cewa akwai ‘yan takara da dama daga yankuna daban-daban, inda kowa ke da magoya baya da ke goyon bayansa, lamarin da ya sa ake fuskantar ƙalubale wajen tsaida mutum guda.

A cikin wannan yanayi, wasu hotuna da ke nuna tsohon gwamnan jihar Yobe, Ibrahim Gaidam, tare da gwamna mai ci Mai Mala Buni da kuma shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, suna yawo a kafafen sada zumunta.

Wannan lamari ya ƙara tayar da hankalin jama’a, inda mutane da dama ke kokarin fahimtar ko akwai wata alama da ke nuna wanda zai zama zaɓin jam’iyyar.

Har yanzu dai babu wata sanarwa a hukumance daga jam’iyyar APC dangane da wanda za a tsaida, yayin da ake sa ran za a ci gaba da tattaunawa kafin yanke hukunci na ƙarshe.

🗣️ Jama’a na ci gaba da bibiyar lamarin tare da jiran matakin da jam’iyyar za ta ɗauka.

YOBE News FORUM

🔴 SANARWAMuna sanar da al’umma cewa live video interview da muka sanar za mu yi da YG BELLO a yau, an ɗaga shi zuwa wani...
20/04/2026

🔴 SANARWA

Muna sanar da al’umma cewa live video interview da muka sanar za mu yi da YG BELLO a yau, an ɗaga shi zuwa wani lokaci daban saboda wasu dalilai.

Za mu sanar da sabon rana da lokaci nan ba da jimawa ba, In Sha Allah.

Muna godiya da fahimta da haƙurin ku.

YOBE News FORUM

Address

Tsalle Biyu Dogo Nini Ward Potiskum
Potiskum

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when YOBE News FORUM posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share