17/05/2026
🔴 HON. YAHAYA GARBA BELLO YA JANYE DAGA TAKARAR MAJALISAR TARAYYA TA NANGERE/POTISKUM
Yobe News Forum
Mai neman takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar mazabar Nangere/Potiskum, Hon. Yahaya Garba Bello, ya sanar da janye takararsa bayan tuntuba da shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Yobe.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Hon. Yahaya Garba Bello ya bayyana godiyarsa ga Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, tare da shugabannin APC, dattawa da masu ruwa da tsaki bisa irin jagoranci, shawarwari da kokarin da suke yi domin tabbatar da hadin kai da zaman lafiya a jam’iyyar da jihar baki daya.
Ya kuma gode wa magoya bayansa, abokai, ‘yan uwa da masu fatan alheri bisa addu’o’i, goyon baya da jajircewar da s**a nuna masa tun farkon wannan tafiya ta siyasa.
Hon. Yahaya Garba Bello ya ce bayan doguwar tuntuba da la’akari da maslahar jam’iyya, hadin kai da ci gaban al’umma sama da bukatar kai, ya yanke shawarar janye takararsa duk da cewa hakan bai kasance abu mai sauki ba.
Ya bayyana cewa tun daga farko manufarsa ba ta kasance son rai ko neman anfani na kai ba, illa yi wa al’umma hidima, kawo ci gaba da samar da kyakkyawan wakilci ga mutanen Nangere/Potiskum.
Sai dai ya tabbatar wa jama’a cewa ayyukan taimakon al’umma, tallafa wa mabukata, karfafa matasa da ci gaban al’umma da aka sanshi da su ba za su tsaya ba ko da babu mukami.
A karshe, ya yi kira ga magoya bayansa da su kasance masu hakuri, hadin kai da kuma ci gaba da bai wa zaman lafiya da ci gaban jihar muhimmanci.
Allah Ya albarkaci Nangere/Potiskum, Jihar Yobe da Najeriya baki daya.