Zaharaddeen Muhd Ghali

Zaharaddeen Muhd Ghali Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Zaharaddeen Muhd Ghali, Digital creator, Rogo.

Alhamdulillah🙏
14/11/2024

Alhamdulillah🙏

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Ikram Sani Idris, SoudaĂŻssi Abdourahim, Ibrahim Tukur, An...
03/11/2023

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Ikram Sani Idris, SoudaĂŻssi Abdourahim, Ibrahim Tukur, Anas Isag, Marzuk Musa Muhammad

16/07/2023

Mutuwar Sarki Yazid
Ga dukkan alamu Yazidu ya bar duniya da juyayin
abu guda daya da yake fargaban gamuwa da
Allah a kan sa. Wannan lamarin kuwa shine kisan
Husaini da danginsa. An fadi cewa, karshen
kalaman da ya furta a duniya su ne: “Ya Allah!
kada ka rike ni da abinda ban so ba kuma ban
bada umurni ba. Ya Allah! Kayi hukunci a tsakani
na da Ibnu Ziyad – yana nufin gwamnansa na
Kufa wanda ya sa aka kashe Husain. Yazid ya
rasu a ranar 14 ga Rabi’ Awwal na shekarar 64H.
Duka duka mulkinsa bai cika shekaru hudu ba
amma al’ummar musulmi ta samu ja da baya
matuka daga karfinta da kwarjininta a cikin
wannan bakin lokaci. Rundunar Husain bin
Numair wacce take tsare da Ibnuz Zubair da
jama’arsa suna dako a wajen Makka ba su samu
labarin mutuwar Yazid ba sai bayan sati uku cur.
Abu kadan ya rage wannan runduna ta hada kai
da Ibnuz Zubair bayan sun samu wannan labari.
Amma abinda ya kawo cikas shi Bin Numair ya
nemi ya dora hannunsa a kan na Ibnuz Zubair ya
yi masa mubaya’a da sharadin a yafe duk
jinainan da s**a gudana a baya. Ya ce kuma idan
an yi haka na lamunce ma kasar Sham gaba
daya zan sa su yi maka mubaya’a. Shi kuma sai
ya ki karbar wannan sharadi. A nan ne Bin
Numair ya juya yana nadama, ya ce, “Dubi yadda
nake kiran sa zuwa sarauta yana neman ci gaba
da fitina”. Ashe dai Allah bai kaddare shi da
zama sarki ba. A can kuma birnin Dimashka ta
Sham an sha takaddama sosai a kan wa za a
nada bayan Yazidu tun da shi bai bar wani wasici
a kai ba. Daga bisani sai aka dora wa dansa
Mu’awiyah karami jan wannan ragama. Amma
ina dadin mulki a lokacin tashin hankali! Ba da
jimawa ba shi wannan sai ya yi murabus ya bar
wuri wayam ana ta muhawara ba mai bukata. A
nan ne Umawiyyawa s**a bukaci su je su
sasanta da Ibnuz Zubair a Makka, su yi masa
mubaya’a daga bisani kuma sai Allah ya sa aka
jitu a kan Marwan bin Al Hakam wanda shi ne
mulki ya ci gaba a cikin zuriyarsa. Matsayin
Malaman Sunna A Kan Wadannan Fitinu
Annabinmu Sallallahu Alaihi Wa Alihi Wasallam
ya sanar da cewa fitinu zasu gudana a bayansa.
Kuma ya fadi cewa alherinka yana gwargwadon
nisantarka daga gare su. Wadannan hadisai suna
na a shimfide cikin littafan Sunna a Kitabul Fitan
na kowane littafi. Duba alal misali: Sahihul
Bukhari, Kitabul Fitan, Babun takunu fitnatun al
qa’idu fi ha khairun minal qa’im, Hadisi na 6670.
Game da abinda ya faru a Karbala, ba wani
sabani a tsakanin malamai cewa, an tafka barna
wadda ba ta dace ba. Abin takaici ne da ya nuna
cewa ba a mutunta Manzon Allah ba a cikin
sha’anin iyalinsa. Wanda kuwa duk yake da
hannu a ciki to, ba abinda zai hana shi gamuwa
da fushin Allah in ba tuba ya yi ba tuba
ingatacciya. Amma a game da wa ke da alhakin
wannan ta’asa, to kowa ya fadi albarkacin
bakinsa. Duk wanda yake da kyakkyawan nazari
da sa adalci cikin hukunci zai iya lura da cewa
kaddarar Allah ita ce babban jigon abinda ya
faru. Kuma duk abinda ka ga Allah ya yi to,
tabbas akwai hikima a cikinsa, ko mun san ta ko
bamu sani ba. Hasashen da Ibnu Taimiyyah ya yi
a nan abin sauraro ne matuka. Ga abinda ya ce:
Hasan da Husaini sun rayu a cikin kuruciya
zamanin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Alihi
Wasallam. Don haka ba su samu damar taimaka
masa ba a wajen jihadi da yada kalmar Allah
kamar yadda sauran sahabbai s**a yi. (A
Lokacin wafatin Manzon Allah, Hasan yana da
shekaru bakwai ne da wata tara, a yayin da
Husaini yake da shekaru shida da watanni
takwas). Duk wahalhalun da sahabbai s**a sha a
Makka da tsangwama da tashin hankali, haka ma
duk gwagwarmayar da s**a yi bayan sun bar
gidajensu da yakokan duk da aka yi; Badar da
Uhud da Khandak da Tabuk da sauransu inda
Allah ya yi ta rabon darajoji da gafara ga
sahabbai su wadannan bayin Allah ba su samu
kasancewa a ciki ba. Kasancewar Allah ya zaba
masu wani babban matsayi a aljanna ya sa Allah
ya jarabce su da wata jarabawa a irin nasu
matsayi kuma ya basu shahada. Don haka ma
Ibnu Taimiyyah ya kara da cewa, kashedinka ka
zargi Husaini a kan fitowar da ya yi bayan duk
shawarwarin da aka ba shi. Ka sani Allah ne
yake ingiza shi zuwa ga daukaka da darajar da
ya hukunta masa. Duba Minhajus Sunnatin
Nabawiyyah na Ibnu Taimiyyah (4/527-536).

Digital creator

Canker SoreCanker sore: itace gyembon baki, kurji ne yake fita a baki, mafi yawa yana somawa ne da dan karamin kurji mai...
04/07/2023

Canker Sore

Canker sore: itace gyembon baki, kurji ne yake fita a baki, mafi yawa yana somawa ne da dan karamin kurji mai zafin gaske, wanda yakan iya fitowa a kowacce bangare na baki.

Alamomin Canker Sore sun hada da:
- Farin kurji a baki
- Ciwo mai tsanani
- Wani lokocin yana zama jaa.
- Yana zuwa da zazzabi

Mutum zai iya daukan Canker sore lokocin mu'amala ko kiss ?

Mafi yawan canker sore bata yaduwa ta hanyar mu'amala ko kiss sai dai kadan daga cikin su, kuma hakanan yana warkewa da kansa ko ba'asha magani ba cikin kwana uku zuwa hudu.

Me yake kawo matsalar Canker Sore ?

1- Karancin sinadaran Vitamin B12, Zinc da folate a jiki yakan iya kawo matsalar Canker score.

2- Jin rauni a baki lokocin goge baki yakan iya kawo wannan matsalar.

3- Allergy: Idan garkuwar jiki ya kyamaci wata kwayar bakteria ko abinci yakan iya kawo wannan matsalar.

4- Mata suna fuskantar wannan matsalar lokocin al'ada ta dalilin rikicewar sinadaran hormones.

4- Yawan damuwa (stress) yakan iya kawo wannan matsalar.

5- Kwayar cutar bakteria Wanda akafi sani da H-pyloria yana kawo wannan matsalar.

6- Haka Kuma wassu cututtaka kamar:
-Chrons disease
- Irritable bowel syndrome
- ulcerative colitis
- HIV da sauaran su s**an iya kawo wannan matsalar.

Yadda za'a magance wannan matsalar a lokocin da ya fito:

1- A sa gishiri/manda chokoli guda cikin ruwa kopi daya mai zafi a kurkure baki da shi safe da yamma.

2- Ko kuma a sa bakin soda chokoli guda cikin ruwa kopi daya mai zafi a kurkure baki da shi a kalla lokoci uku a rana.

3- Bayan haka a samu zuma mekyeu a shafa a wajen a kalla lokoci hudu a rana ( zuma na dauke da sinadaran kashe kwayar cutar bakteria da kuma sinadaran rage kuburi da radadi).

4- Idan ba'a samu zuma mekyeu ba za a iya amfani da man kwakwa shima lokoci uku zuwa hudu za'a shafa a wajen.

5- Za'a iya hadawa da Kwayar vitamin B complex a kalla so daya zuwa biyu a rana.

Dan Ghana Islamic Medicine centre cibiya ce data shahara wajen gudanar da bin cike dan gano ingantattun magun guna da s*...
01/07/2023

Dan Ghana Islamic Medicine centre cibiya ce data shahara wajen gudanar da bin cike dan gano ingantattun magun guna da s**a inganta a cikin alqur'ani da hadisan manzon Allah (SAW).

Yayin Da akaji Chanjin Yanayi A gaggawar Tuntubar Dan Ghana Islamic Medicine akan wadannan lambobi kamar haka

Katsina 08037833338

Kano 09120000903

Kaduna 08060484444

Zaria 08060484444

Address

Rogo

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zaharaddeen Muhd Ghali posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share