Oriya Reporters Hausa

Oriya Reporters Hausa Labaran abubuwan dake faruwa a Kano, Najeriya dama Duniya baki ɗaya.

Zamu Dinga baku labarai da ɗumi-ɗuminsu kuma Sahihai ingantattu a kowanne Lokaci awa 24 babu ƙaƙƙautawa

30/05/2026

Jirgi mara matuki zan nada ministan tsarona idan na zama shugaban Nijeriya - Omoyole Sowore, Dan takarar shugaban ƙasa a jami'iyyar AAC.

Me zaku ce?

Cikin Waɗannan Mawaƙan wanene Gwaninka?
30/05/2026

Cikin Waɗannan Mawaƙan wanene Gwaninka?

Mutum Uku Sun Mutu a sakamakon fadawa Rijiyoyi Daban-daban a KanoKatsinaTimes Mutane uku, ciki har da wata mata da ƙaram...
30/05/2026

Mutum Uku Sun Mutu a sakamakon fadawa Rijiyoyi Daban-daban a Kano

KatsinaTimes

Mutane uku, ciki har da wata mata da ƙaramin ɗanta, sun rasa rayukansu sakamakon faɗawa rijiyoyi a wasu yankuna daban-daban na Jihar Kano, kamar yadda Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar.

Mai magana da yawun hukumar, Saminu Abdullahi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

A cewarsa, lamarin farko ya faru ne a yankin Semegu da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso, inda wani mutum da ba a tantance sunansa ba ya faɗa cikin rijiya ya mutu.

Ya ce hukumar ta samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 7:06 na safe daga wani mai suna Hafizu Garba-Saminu, wanda ya sanar da su aukuwar lamarin.

“Nan take muka tura jami’an ceto zuwa wurin, inda s**a fito da gawar mutumin daga cikin rijiyar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa an miƙa gawar ga jami’in binciken manyan laifuka na ofishin ‘yan sanda na Panshekara, Salisu Salihu, domin ci gaba da bincike.

A wani lamari na daban kuma, wata mata mai shekaru 32 mai suna Maimuna Sh*tu tare da ɗanta mai watanni 18, Harisu Muntari, sun mutu bayan sun faɗa cikin rijiya a ƙauyen Madarin Taba da ke Ƙaramar Hukumar Warawa.

Abdullahi ya ce hukumar ta samu wani kiran gaggawa da misalin ƙarfe 9:40 na safe daga wani Buhari Sa’idu, wanda ya sanar da cewa wata mata da ɗanta sun faɗa cikin rijiya.

Ya bayyana cewa an tura jami’an ceto cikin gaggawa zuwa wurin, inda aka fito da gawarwakin mutanen biyu daga cikin rijiyar.

A cewarsa, an miƙa gawarwakin ga shugaban unguwa, Yusuf Surajo, da kuma mijin matar, Muhammad Sh*tu.

Hukumar kashe gobarar ta ce ana ci gaba da bincike domin gano musabbabin aukuwar hadurran.

Sai dai hukumar ta yi kira ga al’umma musamman iyaye da masu kula da yara da su tabbatar an rufe rijiyoyi yadda ya kamata domin kauce wa irin waɗannan munanan haɗurra.

Ƙungiyar Gwamnoni Ta Nemi Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Maida Mafi Ƙarancin Albashi Ya Zama Naira Dubu 100Ƙungiyar Gwamnonin N...
30/05/2026

Ƙungiyar Gwamnoni Ta Nemi Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Maida Mafi Ƙarancin Albashi Ya Zama Naira Dubu 100

Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta bayyana goyon bayanta ga manufofin gyaran tattalin arziƙi na gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tare da neman a ɗaga mafi ƙarancin albashin ma’aikata zuwa Naira Dubu Ɗari.

Shugaban NGF kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ne ya bayyana hakan inda ya ce sabon albashin zai dace da halin matsin tattalin arziƙi da tsadar rayuwa da ake ciki yanzu, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

Ya ce gwamnatocin jihohi na ci gaba da tattaunawa da gwamnatin tarayya da kuma ƙungiyoyin ƙwadago domin cimma matsaya mai ɗorewa kan batun mafi ƙarancin albashi.

Ana sa ran wannan kira na neman albashin Naira 100,000 zai ƙara tasiri a tattaunawar da ake yi tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin ƙwadago kan sabon tsarin albashi da sauran matakan rage raɗaɗin tattalin arziki ga ƴan Najeriya.

Shekarau Daga APC, Gawuna Daga NDC Kwankwasiyya,wanne ne zaɓinka a kujerar sanatan Kano ta tsakiya?
29/05/2026

Shekarau Daga APC, Gawuna Daga NDC Kwankwasiyya,wanne ne zaɓinka a kujerar sanatan Kano ta tsakiya?

Sanata Aishatu Binani ta samu tikitin takarar gwamnan jihar Adamawa a jam'iyyar NDC bayan yarjejeniyar maslaha da s**a y...
29/05/2026

Sanata Aishatu Binani ta samu tikitin takarar gwamnan jihar Adamawa a jam'iyyar NDC bayan yarjejeniyar maslaha da s**a yi da abokanan hamayyarta.

Binani ta kasance 'yar takara tilo da za ta fafata da maza akalla bakwai da ke takarar gwamnan Adamawa a jam'iyyu daban-daban.

Faɗa mana abu ɗaya daka amfana da shi cikin shekaru uku na kamun ludayin shugaban ƙasa Bola Ahmad Tunubu?
29/05/2026

Faɗa mana abu ɗaya daka amfana da shi cikin shekaru uku na kamun ludayin shugaban ƙasa Bola Ahmad Tunubu?

Duk Wanda S**a Kawo Maka Raini Ka Nuna Musu Ƙarfin Gwamnati — Sanusi II Ga Gwamnan KanoSarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ...
29/05/2026

Duk Wanda S**a Kawo Maka Raini Ka Nuna Musu Ƙarfin Gwamnati — Sanusi II Ga Gwamnan Kano

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya shawarci Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya sa ƙafar wando ɗaya da duk wanda ya kawo masa raini a siyasance.

ZABEN GWAJI: Waye Zabinka a Takarar Gwawman nan Kano TsakaninA - Abba Kabir Yusuf B - Aminu Abdussalam GwarzoZamu bayyan...
29/05/2026

ZABEN GWAJI: Waye Zabinka a Takarar Gwawman nan Kano

Tsakanin

A - Abba Kabir Yusuf

B - Aminu Abdussalam Gwarzo

Zamu bayyana Wanda yayi Nasara nan da awa 24.

Kwankwaso na shirin bayyana Aminu Abdussalam a matsayin ɗan takarar gwamna na NDC a KanoRahotanni daga majiyoyi masu tus...
28/05/2026

Kwankwaso na shirin bayyana Aminu Abdussalam a matsayin ɗan takarar gwamna na NDC a Kano

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin bayyana tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Comrade Aminu Abdussalam, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a jihar Kano.

Aminu Abdussalam ya yi murabus daga mukaminsa na mataimakin gwamna a watan Maris, makonni kaɗan bayan Majalisar Dokokin Jihar Kano ta aika masa da takardar tsige shi daga mukamin.

Majiyoyi sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa an cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa ta sirri da aka gudanar a tsakanin manyan jiga-jigan tafiyar Kwankwasiyya da abokan siyasa na kusa da Kwankwaso.

Tun da farko dai tsohon ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, na daga cikin waɗanda ake ganin suna da ƙarfi wajen samun tikitin takarar gwamnan. Sai dai rahotanni sun ce daga ƙarshe Kwankwaso ya amince da Aminu Abdussalam a matsayin wanda zai tsaya takarar.

Rahotannin sun ƙara da cewa Kwankwaso ya bai wa Gawuna tayin kujerar mataimakin gwamna ko kuma tikitin takarar Sanatan Kano ta Tsakiya, amma ana zargin Gawuna ya ƙi amincewa da tayin tare da bayyana cewa zai ci gaba da aiki domin nasarar jam’iyyar.

Majiyoyi sun ce Gawuna ya shaida wa Kwankwaso cewa ya shiga tafiyar Kwankwasiyya ba tare da wani sharadi ba, saboda haka rashin samun tikitin gwamna ba zai sa ya fice daga tafiyar ba.

An kuma rawaito cewa ƙin amincewar Gawuna da tayin ne ya jinkirta sanar da Aminu Abdussalam a hukumance, yayin da wasu masu ruwa da tsaki ke matsa lamba kan a sake duba cancantar Gawuna saboda ƙarfin siyasarsa.

Wasu daga cikin masu goyon bayan Gawuna sun bayyana cewa ya kamata ɗan takarar da zai fafata da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fito daga Kano ta Tsakiya, kasancewar yankin ne ke da mafi yawan ƙuri’u a jihar.

Sai dai masu goyon bayan Aminu Abdussalam suna ganin tsohon mataimakin gwamnan ya nuna cikakkiyar biyayya, jajircewa da sadaukarw

Da Dumi Dumi: Babu Wata Jam Iyyar Da Tabawa Talaka Rayuwa Mai Tsafta Da Sauki Da Yiwa Talaka Adalci Kamar Jam Iyyar PDP,...
27/05/2026

Da Dumi Dumi: Babu Wata Jam Iyyar Da Tabawa Talaka Rayuwa Mai Tsafta Da Sauki Da Yiwa Talaka Adalci Kamar Jam Iyyar PDP, Nasani Akwai Dan Kura Kurai Da Wasu S**ayi Acikin Jam Iyyar, amma Talakawa Sunfi Jin Dadin Jam iyyar Fiyeda Ko Wacce Jam iyyar a yanzu~ Sheik Isah Ali Pantami.

Address

Sabon Gari Bagadawa

Telephone

+2348182936818

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Oriya Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Oriya Reporters Hausa:

Share