Media Forum Saminaka

Media Forum Saminaka Shafi mallakin "Media Forum Saminaka", Domin isar da saƙonni da rahotonni na Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sheikh Ibraheem Zakzaky (H).

Gayyata Zuwa Taron Makon Imam Khumain (QS) A Da'irar Saminaka Gobe Talata Yan uwa musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Zakz...
01/06/2026

Gayyata Zuwa Taron Makon Imam Khumain (QS) A Da'irar Saminaka Gobe Talata

Yan uwa musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na Dandalin Dalibai (Academic Forum) na gayyatar al'umma Zuwa wajen taron Makon Imam Khumain (Imam Week).

Za a gabatar da taron ne Gobe Talata 2/June/2026. Taron zai gudana ne a wurare biyu a fadin Da'irar:

Za a gabatar a garin Saminaka a Hussainiyyatu Shaheed Turi da karfe 4:00pm. Za kuma a gabatar a garin Ramin Kura (Fudiyyah) shima da karfe 4:00pm.

SANARWA: Media Forum Saminaka

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya yi layya yau Laraba 10 ga Dhul Hijja 1447, wanda yayi daidai da 27/05/2026, a gid...
27/05/2026

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya yi layya yau Laraba 10 ga Dhul Hijja 1447, wanda yayi daidai da 27/05/2026, a gidansa dake Abuja.






10/ZulHijja/1447
27/05/2026

SANARWA:Daga Ofishin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ  اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُح...
26/05/2026

SANARWA:

Daga Ofishin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ

وَمَا كَانَ الْمُؤْمِنُونَ لِيَنفِرُواْ كَآفَّةً فَلَوْلاَ نَفَرَ مِن كُلِّ فِرْقَةٍ مِّنْهُمْ طَآئِفَةٌ لِّيَتَفَقَّهُواْ فِي الدِّينِ وَلِيُنذِرُواْ قَوْمَهُمْ إِذَا رَجَعُواْ إِلَيْهِمْ لَعَلَّهُمْ يَحْذَرُونَ.

Muna sanar da ƴan'uwa tashar ABS ta koma sabon frequency:

Eutelsat 16est/Amos17 Frequency 10928/H/30000

Sannan an samar da sabon channel na YouTube:

https://youtube.com/?si=O3OMAak_JQwucQy5

Wassalam






09/DhulHijja/1447
26/05/2026

Shahadar Imam Muhammad Al-Baqir (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) 7 ga Zulhijja. Lokacin da Hisham Ibn Abdul Malik y...
24/05/2026

Shahadar Imam Muhammad Al-Baqir (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) 7 ga Zulhijja.

Lokacin da Hisham Ibn Abdul Malik ya karbi mulki, mulkinsa ya koma na ta'addanci da zalunci. Siyasar zalunci da azabtarwa ita ce ta haifar da tawayen su Shahid Zaid ɗan Imam Ali Al-Sajjad (SA) wanda ya yi shahada tare da sahabbansa aka ƙone gawarsu.

Haka kuma Hisham ya tsanantawa ɗaliban Imam Muhammad Al-Baqir (SA), duk da haka waɗannan matakan zalunci ba su hana yaɗuwar musulunci da wayar da kan Al'umma akan addini ba. Hisham Ibn Abdulmalik ya bada umarnin sanya wa Imam Muhammad Al-Baqir (SA) guba wanda ya zama sanadin shahadarsa (S) a tafarkin Allah. Imam yayi shahada yana da shekaru 57.

السلامُ عليكَ يا حجة الله على الخلق أجمعين،

أعظم الله أجورنا وأجوركم بذكرى شهادة الإمام الباقر عليه السلام






07/ZulHijja/1447
24/05/2026

Shawarwari:1- A irin wannan lokacin, ɗan uwa almajirin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya kara kokarin kusantan Jagor...
23/05/2026

Shawarwari:

1- A irin wannan lokacin, ɗan uwa almajirin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya kara kokarin kusantan Jagoran, da ruhinsa da gangan jikinsa.

2- Kusanci da Ruhi da ma'anar, mutum ya kara gyara dabi'unsa, ya tsarkake zuciyarsa, ya yi kokarin inganta ayyukansa bisa Iklasi da neman kusanci ga Allah Ta'ala, ya kuma ta yin addu'ar da Jagora (H) ya bashi na; "Ya Allah, Ya Rahman, Ya Raheem, Ya Muqallibal Quluwb Thabbit Qalbiy alaa Diynik.”

3- Kusanci da gangan jiki kuwa, shi ne bibiyan Jagoran tif da tif, musamman ta hanyar sauraron jawabansa masu albarka na Munasabobi, da Ziyarori da ake kai masa, da ganawa da bangarorin yan uwa. Zuwa yanzu akalla Jagora (H) ya yi jawabai sama da 200 daga fitowarsa, bai k**ata ace dan uwa mai amsa sunan Buraza ko Sister, ɗaya daga jawaban nan su wuce su ba su saurare su ba. In ka ji ana batun Fikirar Jagora (H) baka gane ba, ko kaga mutum yana ta kumfar baki cewa, wai mene ne Fikirar Jagora (H)? To bai sauraron Jagora din. Domin da sauraron ne ake jin Fikirar, kuma ake gane bauɗe ma Fikirar.

4- Da yake kwana biyu YouTube Channel din ABS TV ya samu matsala. Ana kokarin shawo kansa, da sai in ce mutum zai samu duk jawaban Jagora (H) a can na tsawon shekaru biyar din nan. Amma dai mutum zai iya samun wasu daga jawaban a shafin Cibiyar Wallafa ta wannan adireshin https://www.cibiyarwallafa.org/mp3-jawaban-shaikh-ibraheem-zakzaky-h-2021-2022/, ko kuma a Telegram Channel mai adireshin t.me/cibiyarwallafa. Na'am, akwai da dama da ba mu riga mun dora ba, amma za mu saka su ba da jimawa ba, musamman a Website din.

5- Shawara ta gaba ita ce, kowane dan uwa da yar uwa, a kara sa'ayi wajen ganin ana halartan tarurrukan Harka Islamiyya a Abuja. Wanda Jagora (H) ya ke ta nanata cewa, a madadin na Zaria ne aka mai da su Abuja din, kuma budaddun tarurruka ne wanda ake gayyatar kowa, babban buraza ko ƙarami ba tare da ƙaidi ba. Na'am, in an samu muhalli ba matsala su Jagora kan fito, in aka samu matsalar muhalli ba lallai su fito ba, sai a zabi wakilcin ba'adin yan uwa su yi ganawa a daidai lokacin, amma can babban taro yana cigaba da gudana. Kuma dai bisa irshadin Jagora (H), ko yana wajen ko baya nan, ya k**ata yan uwa su je don Allah ne, ba don Jagora din na wajen ba. Ghadeer na gabanmu. Haka ma Ashura da sauransu.

6- Mu kara saka ido akan yan Shubha da wadanda suke karɓan Shubuhohin nasu ba tare da sun ankara ba. Za ka ji suna soke-soke ga Harka, wanda in ka natsu da kyau za ka ga Jagora (H) suke hari kaitsaye, amma za su yi ta kewaye kewaye, suna cewa, a ce kaza kaza? A ce ba kaza ba? Ko kuma su yi ta zubo da wahamomi a fakaice da sunan yabon wasu Malamai, alhali suna shagube ne ga Jagoran Gwagwarmayan nan da Jagoran Musulmi, Na'ibul Imam (AJ) ya yi masa stamp akan aikinsa, tare da kira gare shi akan ya cigaba da dagewa a tafarkin da ya kira shi na Jihadi a tafarkin Allah. Mu ankare da su, mu musu nasiha, in basu ji ba, mu nisance su.

7- Mu kiyaye zage-zage, zagin Musulmi fasikanci ne, kuma Jagora (H) yana ta tunatar da mu cewa in ma aka ga wani na zagi to ba daga cikinmu yake ba. Ma'ana ko an san buraza ne, yanzu ba Burazanci din yake yi ba. Saboda haka k**ar yadda Amirulmumin (AS) ya yi wasiyya akan kar a zagi wasu mutane, a fadi ayyukansu ne, sai mutane su gane su da ayyukan nasu. Mu ma mu zama hakan. Mu ankarar da junanmu da tausayawa, da kira mai kyau, da bayani mai gamsarwa. Da yawa ba a fahimci inda aka karkata ba, amma a hankali ta hanyar bayanan wasu daga masu saka hikima mutane na dawowa hayyacinsu, suna kara kankame Jagoran shiriya.

8- Kowane dan uwa, ya saurara, ko bai saurara ba, ya nemi Jawabin rufe Mu'utamar ɗin Kano na bara, da na rufe Mu'utamar ɗin Bauchi na bana, ya sake sauraron Jagora (H). Tabbas zai fahimci matsalar da ke faruwa, kuma zai shiga taitayinsa. Insha Allah da wadannan, zai ma kansa matsaya akan ko dai zai yi Harka Islamiyya karkashin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), ko zai cigaba da rudewa da sunan bai gane me ake cewa, ko wane Fikira ake magana, ko a ina ake shigo da wasu abubuwa Harka da sauransu ba.

9- Kar mu yarda mu zama 'yan uwan Social Media kawai, mu kara kusantar junanmu a zahiri, ta hanyar halartan tarurruka da Ta'alimomin Harka a Da'irori da Halkokinmu. Ya zama tare da gudummawarmu Harka tana motsi a yankunan da muke ta kowane bangare. Kuma musamman matasa, mu kara kokari wajen ɗamfarewa da lajanonin da muke bayar da gudummawa a cikinsu, ya zama kullum tunaninmu yadda za mu inganta ayyukan Harka ta cikin Lajanonin ne. Mu sadaukar saboda Allah.

10- Mu kula da sababbin 'accounts' din da makiya ke budewa a Facebook da boyayyun sunaye, suna haddasa rikice-rikice, zage-zage, ko jeho Shubuhohi. Wasu kuma an san su, amma su wawaye ne, ko wadanda basu da wanda suke ganin mutuncinsa a doron ƙasa, sai su yi ta shirme. Ire-iren wadannan ba a musu ko da 'comment' belle 'like' a shafinsu, ballantana kuma a yi 'sharing' shirmen nasu ko da da sunan musu raddi ne. In aka kau musu da kai, suna ta yi ba a kula su a shafin nasu, za su gaji su bari. In kuwa ana kula su, to k**ar ana 'promoting' din shafukan nasu ne, sai su samu 'engagement' da yawan da shafin nasu zai rika girma. Ganin haka sai su yi ta cigaba da kawo hatsaniyar da gangan. In mutum cin mutunci yake, ta yadda ba za ka jure ba, da ka masa comment gara ka yi report din shafin nashi ka yi blocking dinsa ka huta. In shubha ce yake kawowa da waswasa, samu lokaci ka yi martani a inda ya dace, ba a shafinsa ba, ka warware shubhar ba tare da ka ma ambaci da shi kake ba.

Allah Ta'ala Ya bamu sabati a tafarkinSa. Ya sakawa Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) da dukkan alkairinsa. Ya tabbatar da mu a bayansa.

— Saifullahi M. Kabir
6 Zulhijja 1447 (23/5/2026)

HOTUNA: Yanda aka gabatar da Pre-Khudubah a babban masallacin Juma'a na Unguwan Bawa dake Da'irar Saminaka a yau Juma'a ...
22/05/2026

HOTUNA: Yanda aka gabatar da Pre-Khudubah a babban masallacin Juma'a na Unguwan Bawa dake Da'irar Saminaka a yau Juma'a 22 ga watan Mayu 2026. Malam Salisu Nazifi shine ya gabatar da jawabi a wajen bayan idar da Sallah a harabar Masallacin.

© Media Forum Saminaka

21/05/2026

Har Yanzu Lokaci Bai Ƙure Ba; ga wasu ƙadan daga cikin ayyukan da akeson mutum ya yawaita aikatawa a waɗannan kwanaki goman na farkon watan Zul-hijjah.

© Media Forum Saminaka
4 ZUL-HIJJAH 1447

20/05/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Muhammad Bakir Aliyu Sisterny, Yahaya Abdullahi T-owner, Maiakwai Baqoshi, Sharif Salisu Muhammad, Zakiya Muhammad Siraj, Aminu MMuh'd, Furtuu Sabaa, Auwal M Yusuf Midiya, Shamwilu Rabi'u, Muhd Salisu Nuhu Wa'ek, Musan Sarki, M Radi Ridwan, Saluhu Abdullahi, Autan Ummanshi, Abdoul Aziz Murtala, Jawad Lawal Ziza, Hafsat Salisu, Xainab Yahuza Nuhu, Fulatan Stf, Izzuddeen Ishaq, Muhammad Yusufa

KARATUN MAKARANTAR AHLULBAIT (AS)Masu hankali, sun daina cewa Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) bai yi karatun Sunnah b...
18/05/2026

KARATUN MAKARANTAR AHLULBAIT (AS)

Masu hankali, sun daina cewa Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) bai yi karatun Sunnah ba. Ko ba komai, a baya-bayan nan, wasu 'Video Clips' guda biyu sun yi yawo a 'Social Media'; ɗaya na Dakta Bashir Aliyu (Alfurkan), wanda a baya can Buraza ne, yanzu kuma Malami ne Bawahabiye, inda sam ba boye ba, ya bayyana cewa tun suna Jami'a, Malam Ibraheem Zakzaky ke koyar da su karatun addini. Wato tun a ƙarshen shekarun shekarun 80s kenan.

Haka ma, kwanan nan, aka yi hira da yayan Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), wanda yake babban Malami ne na Ƙungiyar Izala a Zaria har a yanzu haka, kuma da gaske bai tare da Shaikh Zakzaky din ko kadan k**ar yadda ya bayyana, Malam Sani Yaqoub, amma shi ma in mutum ya kalli hirar, zai ji yadda ya nuna yadda s**a riƙa fadi tashin zuwa neman ilimi tare da Shaikh Zakzaky tun suna kanana har aka taso. Ya tabbatar da Malam Zakzaky ya yi karatun Zaure yadda ya k**ata.

A baya, an yi hira da babban yayan su Shaikh Zakzaky (H), wanda yake shi ma Malamin Sunnah ne a Zaria, Shaikh Abdulƙadir Yaqoub, inda ya bayyana cewa Shaikh Zakzaky na da basirar daukan karatu, ta yadda tun suna yara in s**a je Zauren karatu ana biya musu, in s**a dawo gida suna bita s**a manta, Shaikh Zakzaky ke tuna musu karatun nasu, tare da cewa ba irin wanda ake masa ba ne a daidai lokacin, sun wuce shi.

Ni da kaina, na taba hira da ƙanina shaƙiƙi na Shaikh Zakzaky, wanda shi ke bin sa a haihuwa, wato Malam Badamasi Yaqoub, yake faɗa min yadda karatun Malam Zakzaky (H) ya kasance. Malam Badamasi yace: “Babu wani littafi na Luga ko na Fiqihu da Aqida, wanda ake karantawa a Zauren ilimi a wancan shekarun a zaurukan ilimi na Zazzau, wanda Shaikh Zakzaky bai karance shi ba. Wani ma ya yi ya maimaita ne.”

Fahimtar karatun kuwa, Jagora (H) ya fada a littafin Tarihinsa mai suna RAYUWATA, cewa, in aka biya masa karatu sau daya, biyu, ya biya, in aka kara na uku, to ya haddace kenan a lokacin yana ƙarami. Bisa haka ne ma ya haddace kananan littafan Fiqihun Malikiyya tun bai san me ake nufi da wasu abubuwan da ake cewa an haramta a littafan, irin su c**a, zina, hassada da sauransu ba.

Fahimtar Mazhabar Ahlulbait (AS) kuwa, tun a shekarar 1980 Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya yi Istibsari, bayan yin tozali da Bawan Allah, Ruhullah Imam Khomaini (QS), da ganin irin yadda Allah Ta'ala Ya bashi nasara.

Jagora (H) ya faɗi cewa: “A farkon shekarar 1980 ne na je Iran, to bayan dawowata sai mutane s**a ga ina yin wani irin Alwala, da wata iriyar Sallah. Tun a wancan lokacin (1980 kenan), s**a ce, ai ga shi sun ga yana shafan ƙafa, kuma Idan ya yi Sujjada yana Tasbihi a bayyane, yana ta wasu irin abubuwa, su ba su gane ba. Ganin haka, don gudun rashin fahimta, wasu abubuwa da dama sai na daina yinsu a bayyane....”

Yace: “Ni kuwa kafin in tafi Iran ne ma na yanke shawarar cewa, duk abinda Imam Khomaini (QS) yake yi, to shi zan yi. Kasancewar Allah Ya ba shi nasara, ya nuna ya samu karɓuwa a wajen Allah Ta'ala, sannan idan wata Ɗarika yake yi, lallai zan karɓi wannan Ɗariƙar (in na je wajenshi).

“Bayan na je, na tambaya, sai aka ce da ni Imamiyyah yake yi. Da na dawo, ban ce wa mutane ku zo a yi Imamiyyah ba. Don da haka na yi, da tuni an yi rigima a lokacin. Sai na bar mutane akan yanzu dai a je a yi addini dai.” inji Jagora (H).

Daga abinda za mu fahimta a bayanan su, tun zuwansu Iran na farko a shekarar 1980 s**a fara bin Mazhabar Ahlulbait (AS), kuma s**a yi riƙo da tafarkinsu (AS), illa dai sun cigaba da rainon 'yan uwa da gwargwadon yanayin da zai sa su fahimci ba kawo musu sabon abu aka yi ba, musamman yadda dama mutane s**a ginu ne akan Ɗariku, a lokacin Izala ta bayyana ta fara kafirta su, su Jagora (H) sai s**a cigaba da Da'awa a irin salon Imam Khomaini (QS), wanda shi tare da cewa inda yake mafi yawa Shi'a ne, amma kullum maganarsa akan Musulmi ne da Musulmi, ba Shi'a ko Sunnah ba.

Shi ma Shaikh Zakzaky sai ya cigaba akan wannan, har ya zama a hankali yake Taujihin mutane, ya Ahhala su zuwa ga fahimtar Mazhabar Ahlulbait (AS) din da kansu, ta hanyar sa'ayinsa da zantukansa masu cike da hikimomi. In mutum ya koma zuwa ga jawabin Jagora (H), mai suna Shi'a-Sunnah, da jawabinsa na Mauludin Sayyida Zahra (SA) na farko da Sisters s**a gabatar a Zaria a shekarun 90s, zai fahimci hakan.

Na'am. Ina magana ne akan karatun Imamiyya. Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya faɗi cewa: “Tun zuwana Iran, na zo da littatafai, musamman zuwana na biyu (a 1986), amma zuwana na farko ma (a 1980) na zo da littatafai da yawa. Ƙaton akwati guda na littafai na zo da shi....

“Kuma da na koma na biyu a 1986, lokacin bikin 22-Bahman, shi ma na zo da littatafai da yawa. Cikin littatafan da na zo da su har da littafan Shaikh Ɗusi mai suna 'Al-Mabsuɗ', da 'Al-Istibsar', da wasu littafai da yawan gaske, wasu ma na Ahlussunnah ne, duk na samo a Iran din na zo da su.

“Haka ma ina bin littafin Shaikhud Ɗa'ifa, da littafan Muhaqqiqul Hilli mai suna “Shara'i'ul Islam Fiy Masa'ilul Halal wal Haram”, duk na zo da su a lokacin. Don haka ma, ko da aka tsare ji a kamun Babangida a 1987, akwai littafan da na ce a kawo min lokacin ina tsare, na Shaikh Ɗusi, wato At-Tahzibul Ahkam, mai Mujalladi huɗu, na riƙa bin ƙa'idojin salloli da addu'o'i na cikin littafin Tahzib din.” Inji Shaikh Zakzaky (H).

Na'am, duk a wadannan lokacin, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) da kansa yake karanta littafan kaitsaye yake, saboda dama yana da asasi na karatun Luga da Addini tun na Zaurukan Malamai, yanayi bai ba shi damar ya fara zuwa ga Malaman Imamiyya su karantar da shi ba a wadannan shekaru goman na farkon Da'awarsa 1980-1990, domin kuwa ya shafe shekaru kusan shida ne a tsare a Kurkuku, kamu daban-daban a wannan shekaru goman.

Don haka sai a shekarar 1990, da yanayi ya bayar, sannan Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya fara zuwa Dauran karatun Hauza Ilmiyya a ƙasar Ghana, inda yake karatu a wajen wani Malami mai suna Sayyid Tabataba'i.

Shaikh Zakzaky (H) ya bayyana cewa: “Ban san tsawon lokacin da muka yi muna karatu ba, amma k**ar tun daga 1990 ne har kusan 1993 ko ma ya fi haka. Kusan duk wata zan je, mu yi karatu in dawo. Sannan kuma karatu mai yawa muke yi.”

Jagora (H) ya ba da bayani mai tsawo akan yanayin yadda suke karatun a wajen Sayyid Tabataba'i a lokacin, da yadda ya rika mamakin irin yadda aka rufe Ilmummukan Ahlulbait (AS), har ya kan rika tunani a lokacin. In muka koma littafin RAYUWA na 1 duk za mu ga wannan. Wanda hakan ya kara sa wa Jagora (H) su ƙara zage damtse wajen ankarar da mutane, da saka su a layin tunanin da kan sa su fahimci faɗin addini fiye da ts**akken fahimtar da s**a yi masa a lokacin.

Ana wannan yanayin ne kuma Fitinar Tawayiyya ta kunno kai a Harka, wanda wasu daga manyan da suke ganin su ke gudanar da Harka s**a ce sun gano Malam (H) Shi'a yake yi, ya canza hadafinsa, ba za su bi shi ba, s**a yi abubuwan da za su yi, karshe s**a b***e daga Harkar s**a fita s**a kafa kungiyarsu akan za su cigaba da gwagwarmaya da yunƙurin tabbatar da addini a bisa tafarkin Sunnah. Bayan kwaranyewarsa ba jimawa kuma sai ga Wakiar Abacha da ita ma aka k**a Malam (H) a cikinta, tun a Satumba 1996 har sai a Disamba 1998 aka sako shi.

Don haka, wadannan yanayoyin s**a hana Jagora (H) zarafin zuwa cigaba da karatu a wannan tsakanin. Sai a farkon shekarar 2000, Jagora ya cigaba da zuwa Jamhuriyar Musulunci ta Iran don Dauran karatun Hauza Ilmiyya, wanda ya kan shafe wata guda ko fiye yana karatun kafin ya dawo a duk lokacin da ya je.

Jagora (H) ya riƙa ɗaukan karatu daga Malamai daban-daban, k**ar Shaikh Ja'afarul Hadi, wanda ya karantar da Jagora (H) ilimin Aqida, karatu mai zurfi.

Dangane da Shaikh Ja'afarul Hadi, Jagora (H) ya bayyana cewa: “Da yake shi almajirin Ayatullahi Subahani ne, kuma kan batun Aqa'id, Ayatullah Subahani ya yi rubuce-rubuce sosai, musamman dangane da firqoqin nan, da irin tunanin kowannensu daban-daban. Shi Shaikh Ja'afarul Hadi ya ce, shi k**ar duk a kansa abin yake, saboda haka sai muka fara wannan darussan da shi.”

To, hatta Nahjul Balagha da Jagora (H) ya karantar, sai da ya nemi iliminsa a Hauza Ilmiyyah kafin ya fara karantarwa.

Jagora ya ba da labarin yadda karatunsa na Nahjul Balagha ya kasance tare da wani Malami mai suna Shaikh Suwaidi. Yace: “Lokacin da za mu fara, ya ce min, mene ne tsammaninka dangane da karatun Nahjul Balagha?”

Jagora ya bashi amsa da cewa: “Abinda nake tunani shi ne, ina so zan fara karantawa mutane Nahjul Balagha ne, to ina so in ji bayaninsa a taƙaice daga wajen wani (Malami). Ina so in san gabaɗaya me Nahjul Balagha ya ƙunsa, me kuma yake koyarwa a dunƙule, kasancewa zan fara karantar da mutane shi.”

A nan ne Shaikh Suwaidi ya kaɗa kai, ya ce, “Yadda ka faɗa ɗin nan haka na yi mafarki an faɗa min.” Jagora yace, dama ya shirya kwasa-kwasansa bakidaya, haka muka bi Nahjul Balagha gabaɗaya a cikin kankanin lokaci.

Haka ma ɓangaren Tafsirin Alƙur'ani, Jagora (H) ya yi karatunsa a wajen Malaman Imamiyya daban-daban a lokuttan wannan Daura da yake zuwa akai-akai ya shafe wata guda ko fiye in ya je, daga ciki akwai Tafsirin Tasnim Fiy Tafsirul Qur'an, na Ayatullah Jawad Amuliy, wanda Shaikh Haaqani ya riƙa biyawa Jagora (H) shi, tun yana matakin takardu kafin a kai ga kammala aikinsa a buga shi. Ban sani ba, ko hakan na daga dalilin Jagora (H) na bayyana Taqalidinsa akan abinda ya shafi Tafsirin Alƙur'ani da Ayatullah Jawadi Amuliy din? Allah masani. Haka ma akwai irin su Shaikh Munzir Hakeem, wanda shi ma Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya yi karatun Tafsirin Alƙur'ani a wajensa.

Malamai daban-daban, su Shaikh Ɗabasi na Qom, da irin su Ayatullah Ahmad, da Shaikh Ridawiy, wanda Jagora s**a yi Usul a wajensa, da Farfesa Ɗahiriy, da Jagora s**a yi Mandiq a gunsa. Karatu mai zurfi a matsayinsa na wanda yake da ido a fagen ilimi tun kafin lokacin.

Kamar yadda aka ambata, a shekara Jagora (H) kan je sau biyu, in yanayi bai bayar da dama ba ya sai ya je sau daya, kuma in Jagora (H) ya je, s**an shafe wata guda zuwa kwanaki 40 ne ko fiye a can. Kuma wasu daga Malaman, Jagora (H) ya kan bi su gida ne ya yi karatun a wajensu, a yayin da wasu s**an zo inda Jagora ke zama ne su bashi karatun.

Jagora (H) ya ba da labarin yadda ya kan fi so ya bi Shaikh Ja'afarul Hadi zuwa gidansa ne din ya ɗauki karatun da suke yi, amma shi Shaikh Jafar din kan ce, shi ya fi so ya zo inda su Jagora (H) suke. Yace: “Akwai wani bayani da na taɓa yi masa, cewa, ni na fi so in zo gidanka ne mu yi karatu. Sai ya ce, a'a, shi ya fi son ya zo inda nake saboda dalilai biyu; na ɗaya, yana fama da rashin lafiya, kuma duk lokacin da ya zo muka yi karatu yana jin sauƙi. Na biyu kuma ya ce, ita Ka'aba ana zuwa wajenta ne, ba ita take zuwa ba.”

Allahumma salli ala Muhammad wa Ali Muhammad wa ajjil farajahum.

Har aka yi Waki'ar Zaria, Jagora (H) na zuwa domin yin wannan karatun. Kamar yadda jiya na ga dan uwa Husaini Ahmad ya ba da labari, cewa wani lokaci in mutum na zauraron Karatun Nahjul Balagha ko Tafsir din Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) da ya gabatar aka dauka, zai ji yana cewa, kwana biyu an daina ganinsu, sun yi tafiya ne don karo karatu, sun je sun yayyago abinda s**a yago, ko wani abu mai k**a da haka nan. Kuma har yanzu, tare da alfaharin godiya ga Allah da jindadi, su Malam (H) s**an ba da labarin waɗannan Malaman nasu na ɓangaren Imamiyya.

Wannan yana kashe duk wata shakku, ko shubuhar maƙiya da s**an ce, ba a yi karatun Hauza ba, ba a san Imamiyya ba, ba a da ilimin Shi'a da sauransu. In ka saurari karatuttukan Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), za ka gane shi masani ne ga duniyar Musulunci gabadaya; Shi'a da Sunnah. Masanin da masana na hakika a kullum suke kara tabbatar da cewa shi masani ne. Alhamdulillahi, ba kawai masani ba, kuma mai aikata sanin da ya yi a aikace.

Hoton da ke ƙasa, ɗaya daga cikin Malaman da su Jagora (H) ke karatu a wajensa ne, a yayin da suke karatun.

Allah Ya kara masa lafiya da aminci, ilimi da taqawa, yarda da dacewa. Alfarmar Sahibul Asr waz Zaman (AS). Ya bamu sabati a karkashinsa.

— Saifullahi M. Kabir
1 Zulhijja, 1447 (18/5/2026)

Sanarwa: AN GA JINJIRIN WATAN ZHUL HIJJAH 1447Daga: Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).بِسْمِ اللَّـهِ الرَّحْمَـٰنِ ال...
18/05/2026

Sanarwa:

AN GA JINJIRIN WATAN ZHUL HIJJAH 1447

Daga: Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

بِسْمِ اللَّـهِ الرَّحْمَـٰنِ الرَّحِيمِ

اللهم صل على محمد وعلى آل محمد🌹

Ya zuwa yanzu mun sami labarin tabbacin ganin jinjirin watan Zhul Hijjah a cikin garin Mafara a wata unguwa da ake kira Kartawa da wasu ƙauyuka da ke kewaye da Mafara k**ar Birnin Wake, Basara Ƙarama da Basara Babba. Har wala yau an gani a garin Ɗandume. Duk a waɗannan wurare ƴan'uwa ne da jama'a masu yawa s**a ga jinjirin watan.

Don haka gobe Litinin za ta zama 1 ga watan Dhul Hijjah 1447, in sha Allah.

Kada a manta da ayyukan kwanuka goma na wannan wata wadda Allah Ta'ala ya kira su layalul ashar (ليال العشر) a Suratul Fajr. Da kuma ladubban layya don tunawa da sadaukarwar Annabi Ibrahim (AS).

Allah ya ba mu sa'a.

Wassalam







29/Dhul Qa'adah/1447
17/May/2026

Address

Saminaka

Telephone

+2348067666867

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Forum Saminaka posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Media Forum Saminaka:

Share