27/03/2025
Harkar Musulunci Za Ta Yi Muzaharar Ranar Qudus ta Duniya A Ranar 28 Ga Maris, 2025
Harkar Musulunci na kira ga al'umma baki ɗaya da kafafen yaɗa labarai da su halarci muzaharorin tunawa da ranar Qudus ta Duniya, wanda aka shirya gudanarwa a ranar Juma’a, 28 ga watan Ramadan 1446 daidai da 28 ga Maris, 2025.
Wannan muzaharori zai gudana ne a dukkannin jihohin Nijeriya, ciki har da Babban Birnin Tarayya, a matsayin wani ɓangare na yunkurin da duniya ke yi a duk shekara na nuna goyon baya ga al’ummar Falasɗinu tare da kuma yin tir da zaluncin da haramtacciyar ƙasar Isra’ila ke aikatawa a kodayaushe.
Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran, Ayatullah Imam Ruhollah Khomeini ne ya ayyana ranar Juma'ar ƙarshe na watan Ramadan a matsayin ranar Qudus ta duniya domin al'umma masu neman adalci a duniya su tunkari zalunci tare da nuna goyon baya ga gwagwarmayar Falasɗinawa.
Kusan shekaru arba’in ke nan Harkar Musulunci tana gudanar da wannan muzaharori a irin wannan rana, duk da hare-haren da take fuskanta daga mahukumta.
Qudus na wannan rana ta na da muhimmanci musamman ma yadda aka cika shekaru 11 da gwamnatin Nijeriya ta aukar da mummunan hari a watan Yulin 2014, inda sojojin Nijeriya s**a kai hari kan masu muzaharar ranar Qudus a Zariya. Wanda a wannan harin ne s**a shahadantar da mutane 34 ciki har da ‘ya’yan Shaikh Ibraheem Zakzaky guda uku—Ahmad, Hameed, da Mahmud Zakzaky.
Kuma Qudus ta bana ta zo a daidai lokacin da ake ci gaba da gallazawa al’ummar Falasɗinu da kuma irin zaluncin da girman kan duniya ke ci gaba da yi wa masu fafutukar kare haƙƙinsu, Harkar Musulunci na kira ga duk masu neman adalci, ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam, da duk wanda ke neman gaskiya da adalci da su shiga cikin waɗannan jerin gwanon goyon baya ga al'ummar Falasɗinu.
Waɗannan muzaharori za su kasance don jaddada goyon bayanmu ga waɗanda ake zalunta tare da buƙatar neman adalci ga duk waɗanda aka zalunta a faɗin duniya.
Ana ƙarfafar kafafen yaɗa labarai da su ba da rahoto ba gaski