A.B.C HAUSA

A.B.C HAUSA Kafar yada labarai dake kawo muku ingantattun labarai da dumi-dumin su.

Hotunan yadda aka gudanar da sallar jana'izar marigayi Muhammad Buhari a Daura jihar Katsina
15/07/2025

Hotunan yadda aka gudanar da sallar jana'izar marigayi Muhammad Buhari a Daura jihar Katsina

Tawagar Jamhuriyar Nijar ta isa Katsina domin halartar jana'izar tsohon shugaban Nijeriya Muhammad Buhari
15/07/2025

Tawagar Jamhuriyar Nijar ta isa Katsina domin halartar jana'izar tsohon shugaban Nijeriya Muhammad Buhari

Jiragen sama sai shawagi suke domin sauka a Katsina
15/07/2025

Jiragen sama sai shawagi suke domin sauka a Katsina

ALLAH SARKI: A Dalilin Irin Soyayyar Da Aka Nunawa Buhari, Aka Sanyawa Wannan Yaro Suna Buhari, Kuma Shi Ma Ya Rasu A Da...
15/07/2025

ALLAH SARKI: A Dalilin Irin Soyayyar Da Aka Nunawa Buhari, Aka Sanyawa Wannan Yaro Suna Buhari, Kuma Shi Ma Ya Rasu A Daren Ranar Da Buhari Ya Rasu

Wannan yaron da kuke gani sunan shi Buhari, an yi wa tsohon shugaban kasa takwara ne da shi. Shi ma Allah Ya yi masa rasuwa jiya da misalin karfe takwas na dare.

Allah Ya jikansu da rahama.

Wàni Bòķa Ya Ýi Wà Watà Matashìya Fyadè A Kànò, Ammà Ya Ce Ba Shi Da Masaniyar Hakan, Kwanķwàmansà Ne S**a Aikata Fýadèn...
14/07/2025

Wàni Bòķa Ya Ýi Wà Watà Matashìya Fyadè A Kànò, Ammà Ya Ce Ba Shi Da Masaniyar Hakan, Kwanķwàmansà Ne S**a Aikata Fýadèn, Ba Shi Ba

Me za ku ce?

Shugaba Bola Tinubu ya nuna alhinin rasuwar tsohon shugaban ƙasar inda ya miƙa ta'aziyarshi ga matar marigayin Aisha Buh...
13/07/2025

Shugaba Bola Tinubu ya nuna alhinin rasuwar tsohon shugaban ƙasar inda ya miƙa ta'aziyarshi ga matar marigayin Aisha Buhari.

Shugaban ya kuma umarci a yi ƙasa-ƙasa da tutocin Najeriya domin girmama tsohon shugaban.

Tsohon Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rasu yana da shekara 82 da haihuwa a wani asibiti da ke birnin Landan.A mak...
13/07/2025

Tsohon Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rasu yana da shekara 82 da haihuwa a wani asibiti da ke birnin Landan.

A makon da ya gabata ne aka kwantar da tsohon shugaban a asibiti bayan ya je duba lafiyarsa kamar yadda ya saba, amma daga baya sai ya kamu da rashin lafiya.

Marigayin ya mulki Najeriya a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa daga 2015 zuwa 2023, inda ya miƙa wa Bola Tinubu ragama bayan jam'iyyarsu ta APC ta sake lashe zaɓen shugaban ƙasa.

Hotuna 📷 Bikin Bokaye Da Mayu A Jamhuriyar Kasar Benin 🇧🇯 Na Ranar Talata 10 Ga Junairu 2023.Ranar gargajiya ko Fête du ...
12/07/2025

Hotuna 📷 Bikin Bokaye Da Mayu A Jamhuriyar Kasar Benin 🇧🇯 Na Ranar Talata 10 Ga Junairu 2023.

Ranar gargajiya ko Fête du Vodoun, biki ne na jama'a a Benin da ke bikin tarihin ƙasar da ke kewaye da addinin Vodoun (Addinin Bokanci Da Maita) na Yammacin Afirka. Ana gudanar da bikin kowace shekara a ranar 10 ga watan Janairu a duk fadin kasar amma musamman a birnin Ouidah.

Vodun tsohon addini ne da wasu mutane miliyan 30 ke yi a kasashen Benin, Togo da Ghana da Najeriya a yammacin Afirka.

Jama'a a yammacin Afirka, musamman Togo, Ghana da Najeriya suna da irin wannan akida amma a Jamhuriyar Benin an amince da ita a matsayin addini a hukumance, Su ne kusan kashi 40% na al'ummar kasar. Ranar Voodoo hutu ce Da Gwamnati ke Bayarwa A Kasar Benin 🇧🇯 kuma akwai gidan kayan Tarihi na Voodoo na ƙasa.

Wadanne alloli ne Benin suke bautawa?

Olokun ya kasance sanannen allahn, Kazalika Shi ne mai mulkin teku, shi ne Kuma allahn arziki. Sauran mashahuran alloli sune Ogun allahn ƙarfe da mayaka da Osun allahn magani da sihiri. Mutane sun gaskata cewa Obas na Benin su ne zuriyar Osanobua, allahn mahalicci.

Bikin na Benin da ake kira Voodoo Day yana faruwa a duk faɗin ƙasar a Ranar 10 Janairun Duk Shekara kuma abin kallo ne sosai, yayin da a Yanzu Ake Yinsa tare da bikin fina-finai na Quintessence a Garin Ouidah ya shahara Saboda masoyan sinima.

Al'ummar Benin na kallo da Bada muhimmancin da bukukuwan kamar Na kirsimeti na Kirista ko na Idin da Musulmi ke yi. Wannan biki na jama'a yana jan hankalin masu bi daga ko'ina cikin Afirka ta Yamma Da Brazil Da Amurka da duniya, don yin bikin na musamman Akwai bukukuwa da dama, wanda ya fi jawo cece-kuce a cikinsu shi ne sadaukarwar da wani limamin Voodoo zai kekketa wuyan kaza da hakora, Da Kuma Yanka Akuya Da Shanye Jinin A Lokaci Guda.

Mabiya da yawa sanye da fararen kaya suna fuskantar teku a birnin Ouidah a kowane biki don nuna girmamawa ga Mami Wata, wata Aljana ta teku.

An yi ittifakin wannan shi ne hoto na farko da a ka dauka, wanda mutum ya fito cikinsa. Ko ka hange shi? Louis Daguerre ...
12/07/2025

An yi ittifakin wannan shi ne hoto na farko da a ka dauka, wanda mutum ya fito cikinsa. Ko ka hange shi? Louis Daguerre ne ya dauke shi a birnin Paris na Faransa cikin shekarar 1838. Tab! Zamanin Ibrahim Dabo ke sarauta a Kano, shekaru dari da tamanin da bakwai (187) fa ke nan.

Shugaban ƙasar Mali ya amince da dokar ba wa kansa ikon yin mulki mara adadiShugaban mulkin wojin Mali Janar Assimi Goit...
12/07/2025

Shugaban ƙasar Mali ya amince da dokar ba wa kansa ikon yin mulki mara adadi

Shugaban mulkin wojin Mali Janar Assimi Goita, ya ƙara wa kansa wa'adin cigaba da shugabancin ƙasar na shekaru biyar, wanda za a iya sabuntawa "babu iyaka" ba tare da zaɓe ba, a cikin wata doka da aka fitar a ranar Alhamis.

Tun ba yau ba aka tsammanin Janar Assimi Goita zai amince da wannan mataki, kuma hakan ya zo ne bayan da majalisar zartaswa da sojojin ƙasar s**a naɗa ta zartar da ƙudirin a makon jiya.

Dokar, wacce Hausa Daily Times ta gano an fallasa kwafinta ga jama'a bayan da Goita ya sanya wa hannu a ranar Talata, ta ba shi damar jagorantar kasar da ke yammacin Afirka har zuwa aƙalla shekarar 2030, duk da alƙawarin da gwamnatinsa ta yi a farko na mayar da mulkin ga farar hula a watan Maris na 2024.

📸Presidence de la République du Mali

Jawabi Na Ba Shi Da Alaƙa Da Abinda Ya Faru A Jihar Rivers, Tsohon Tarihi Na Bayar, Cewar Kashim ShettimaOfishin Mataima...
11/07/2025

Jawabi Na Ba Shi Da Alaƙa Da Abinda Ya Faru A Jihar Rivers, Tsohon Tarihi Na Bayar, Cewar Kashim Shettima

Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa ya bayyana damuwa kan yadda wasu kafafen yaɗa labarai s**a juya maganganun Sanata Kashim Shettima da ya gabatar a lokacin da yake jawabi a wajen kaddamar da littafin “OPL 245: The Inside Story of the $1.3 Billion Oil Block” a Abuja, ranar Alhamis.

Sanarwar wacca mai bashi shawara kan harkokin labarai Stanley Nkwocha ya fitar ta bayyana cewa jawabin Shettima na nuni ne zuwa ga tsohon tarihin matsalolin da ya fuskanta a lokacin yana Gwamnan Borno sakamakon rikicin Boko Haram, ba wai yana tsokaci ne kan abubuwan da ke faruwa a Jihar Rivers ba.

Haka zalika, sanarwar ta bayyana cewa, Shettima ya yi amfani da misalan tarihi ne don yaba wa marubucin littafin, Mohammed Bello Adoke (SAN), bisa jajircewarsa a lokacin da yake Ministan Shari’a.

Ofishin ya kuma bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu bai tsige Gwamna Siminalayi Fubara daga mukaminsa ba, sai dai an dakatar da shi bisa matakin doka domin dawo da doka da oda a Jihar Rivers. An dauki matakin ne bisa tanadin Sashe na 305 na kundin tsarin mulki, tare da amincewar majalisar dokoki ta kasa.

A ƙarshe, Sanarwar ta bayyana cewa duk wani yunkurin juya kalaman Shettima a matsayin s**a ga gwamnatin yanzu ko wata alama ta rikici tsakanin manyan jami’an gwamnati, labari ne na ƙarya da kokarin kawo rashin zaman lafiya. Ofishin ya jaddada cewa Shettima da Tinubu suna aiki tare domin kare dimokuraɗiyya da doka a Najeriya.

Adalci shine a kyale Kudu ta cigaba da mulki a 2027 - Minista Hannatu Musawa
11/07/2025

Adalci shine a kyale Kudu ta cigaba da mulki a 2027

- Minista Hannatu Musawa

Address

Saminaka

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A.B.C HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share