Senator Ibrahim Lamido

Senator Ibrahim Lamido Senator Representing Sokoto East
Senatorial District In the 10th Nigerian Senate (APC).

Chairman Senate Committee on Primary Health Care Development and Disease Control.

A wani yunkuri na karfafa gwiwar manomanmu da sake farfado da harkar noma a yankin mu na Sokoto ta Gabas, mun kaddamar d...
31/07/2025

A wani yunkuri na karfafa gwiwar manomanmu da sake farfado da harkar noma a yankin mu na Sokoto ta Gabas, mun kaddamar da rabon taki kyauta ga manoman yankinmu na Sokoto ta Gabas da nake wakilta, a yau Alhamis.

Dukkanin kananan hukumomi takwas na yankinmu Sokoto ta Gabas da nake wakilta za su ci gajiyar wannan takin cikin tsanaki wanda ya hada da sarakunan Jihar Sokoto reshen Sokoto ta Gabas, kungiyoyin kwadago, kungiyoyin addinai, hukumomin tsaro, tare da sauran al’ummar wannan yanki.

Masu ruwa da tsaki ga harkokin siyasarmu da s**a yi jawabi a madadina a wajen taron kaddamar da rabon takin karkashin jagorancin babban wakilina Alh Kabir Sarkin Fulani, sun yabawa jagorancin mu kan wannan shiri, inda s**a bayyana cewa wannan ne karon farko da ake baiwa manoma takin zamani kyauta, inda s**a ce hakan zai taimaka wajen bunkasa harkar noma da kuma samar da wadataccen abinci a yankin Gabascin Sokoto.

Shirin takin zamani kyauta da muka kaddamar a yau ya nuna karara da tsayin daka wajen karfafa gwiwar manomanmu da sake farfado da fannin noma yankin Sokoto ta Gabas.

Noma ba kawai kashin bayan tattalin arzikin yankinmu ba ne, har ma yana da matukar muhimmanci ga ci gaban jiharmu da ci gaban kasarmu baki daya.

Wadannan tsare-tsare wani bangare ne na dabarun mu na inganta noma, inganta ababen more rayuwa, da tallafawa manomanmu. Don haka ina kira ga manoman mu da su yi amfani da wadannan takin cikin gaskiya da inganci. Muna da kwarin gwiwar cewa wadannan matakan za su kara yawan amfanin gonakin da muke noma da kuma karfafa samar da abinci a jihar Sokoto musamman al’ummarmu na Sokoto ta Gabas baki daya.-SIL.

I extend my warmest wishes to my dear Colleague, the Leader of the 10th Nigerian Senate, Senator (Dr) Michael Opeyemi Ba...
29/07/2025

I extend my warmest wishes to my dear Colleague, the Leader of the 10th Nigerian Senate, Senator (Dr) Michael Opeyemi Bamidele, CON, on his 62nd birthday today.

Today, we are proud to celebrate an iconic and exemplary leader, the Distinguished Senator (Dr) Michael Opeyemi Bamidele, CON, Leader of the 10th Senate of the National Assembly, Federal Republic of Nigeria.

On this special day, Distinguished Senator, we mark not just another year of your impactful life, but the remarkable journey of a statesman who, often at great personal cost and sacrifice, has consistently led by example and shown, through courage, a very deep sense of commitment to Nigeria's progress and an allegiance to her unity that is clear and unassailable.

Your leadership in the 10th Senate stands out for its thoughtfulness, maturity, and an unwavering dedication to the values that strengthen our democracy and bind us as a people. You have earned respect, not just by your words, but even more, by your actions, which continue to inspire hope across the country.

As you step into this new year, I pray that the Almighty will bless you with renewed strength and vigour, wisdom and good health; and that your path will be guided always, seasoned by grace. May you continue to lead with honour, dignity and humility in service to humanity and especially to our beloved nation.-SIL.

Yesterday, I welcomed Illela local Government Chairman of the Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Abubakar Sulaiman B...
24/07/2025

Yesterday, I welcomed Illela local Government Chairman of the Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Abubakar Sulaiman Baki (Abu Baki), to the All Progressives Congress (APC).

Abu Baki announced his exit from the Peoples Democratic Party (PDP) to the All Progressives Congress (APC) During his visit me at my residence in Abuja.

Joined by the Hon Bello Isah Ambarura Member House Representative Gwadabawa and Illela federal constituency, and my Personal aide Ameen Lameer, we proudly embraced Hon Abu Baki, a dedicated grassroots mobiliser to our party.

I assured him of our unwavering support as we work together to build a better future for the people of Sokoto East and, indeed, Sokoto at large.

Together, we will continue to promote the values of good governance, inclusivity and service to humanity.-SIL.

Yesterday, I paid a special visit to my loyal supporter Hon Ibrahim Lawal Danfari Rabah at  his residence in Abuja, I co...
20/07/2025

Yesterday, I paid a special visit to my loyal supporter Hon Ibrahim Lawal Danfari Rabah at his residence in Abuja, I congratulate him over the his welcoming birth of a baby boy.

I pray that Allah (SWT) blesses the new born with good health and long life, and may he grow to become a source of pride for his parents and the entire community.-SIl.

Inna Lillahi Wainna Ilaihi Raji'un Indeed I am saddened to received the shock news of passing away of Former President M...
13/07/2025

Inna Lillahi Wainna Ilaihi Raji'un

Indeed I am saddened to received the shock news of passing away of Former President Muhammadu Buhari GCFR. May aljannatul firdaus be his final abode.-SIL.

07/07/2025

Tare da Sanata Adamu Aleru bayan fitowar mu daga zauren majalisa a yammacin yau Litanin a Abuja.

As a Chairman Senate Committee on Primary Health Care Development And Disease Control, Yesterday, I paid a Courtesy visi...
07/07/2025

As a Chairman Senate Committee on Primary Health Care Development And Disease Control, Yesterday, I paid a Courtesy visit to the Honourable Minister State for Health, Dr. Dayo Adekunle Kadiri in his office in Abuja, as we continue to collaborate to achieve the agenda of President Bola Ahmed Tinubu (GCFR).-SIL.

Matsananciyar damuwa tare da bakin ciki mara misaltuwa ne ke damuna tun jiya Bisaga Hare-haren da ‘yan bindiga s**a kai ...
03/07/2025

Matsananciyar damuwa tare da bakin ciki mara misaltuwa ne ke damuna tun jiya Bisaga Hare-haren da ‘yan bindiga s**a kai a kauyen Kwalajiya dake karamar Hukumar Tangaza ta Jihar Sokoto duk da ba yanki na bane, Inda s**a kashe mutane 15 da basuji ba basu gani ba.

Da kuma harin da s**a kai a karamar Hukumar Rabah daya daga cikin kananan Hukumomi 8 da nake wakilta na yankin Sokoto ta Gabas a majalisar Dattawa ta kasa, a jiya laraba Inda s**a kashe mutane biyu ta hanyar yanka su, kamar yanda na samu labari.

Allah ya sani muna iya bakin kokarin mu wanda ba lallai sai mun fadawa duniya matakan da muke dauka ba a himmar mu ta tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a yankin mu.

Haka kuma Ina sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suke yi a ƙoƙarin da suke na kare rayukan al’umma, kuma zanci gaba da ba su duk wani nau’in gudummawa da ya dace domin yaƙar ‘yan bindiga, ba za mu huta ba har sai wannan yanki ya samu cikakken tsaro insha Allahu matukar muna a raye.

Ina sake jaddadawa al’ummar yankin mu, na Sokoto ta Gabas cewa, da yardar Allah zan ci gaba da bin dukkan matakan da s**a dace, a matsayina na wakilin wannan yanki don tabbatar da zaman lafiya a wannan yanki namu mai albarka.

Ina mika sakon ta’aziyya da jaje ga al’ummar karamar hukumar Tangaza da kuma na Rabah, musamman iyalai da ‘yan uwan wadanda s**a rasa rayukansu a sanadiyyar wadannan Hare-hare na ta’addanci, Allah (SWT) ya gafarta musu ya kuma dawo mana da Dawwa-mammen zaman lafiya, Amin.-SIL.

Assalamu Alaikum.A yau da muke murnar zagayowar shekarar Musulunci ta 1447 bayan Hijirar Annabi Muhammad (SAW) daga Makk...
26/06/2025

Assalamu Alaikum.

A yau da muke murnar zagayowar shekarar Musulunci ta 1447 bayan Hijirar Annabi Muhammad (SAW) daga Makka zuwa Madina, Ina mika sakon taya murna ga daukacin al’ummar Musulmi na Sokoto ta Gabas da nake wakilta da sauran ’yan Najeriya baki daya.

A wannan lokaci da muke murnar shigowar sabuwar shekarar musulunci kamar yadda aka al’adanta, Wannan sabuwar shekara wata dama ce a gare mu na rungumar tausayi, zaman lafiya, da goyon bayan juna.

Ina kara jaddada aniyar majalisar dokokin kasa na samar da dokokin da s**a dace don magance kalubalen da al’ummarmu ke fuskanta.

Tare da goyon bayan ku da kuma jagorancin hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, za mu cigaba da tafiya zuwa ga kyakkyawar makoma.

Ina yi muku barka da shigowa sabuwar shekara ta Musulunci 1447H.-SIL.

Earlier today, I attended at the commissioning of the newly constructed right-hand service carriageway of the inner Nort...
24/06/2025

Earlier today, I attended at the commissioning of the newly constructed right-hand service carriageway of the inner Northern Expressway (INEX) from Ring Road 3 (RR3) to outer Northerner Expressway (Murtala Muhammed Expressway), Abuja.

The project, is one of the mega projects embarked upon by the Minister of Federal Capital Territory (FCT), Barrister Nyesom Ezen Wike, CON, in line with this administration's Renewed Hope Agenda to address infrastructure gaps in the FCT and other parts of the country.

The President of Nigeria Asiwaju Bola Ahmed Tinibu, GCFR in his address as read by Deputy President of the Senate, Senator Barau I. Jiblirl Maliya to his Representing, during the commissioning described the project as a critical piece of the Federal Capital Territory’s master plan, designed to ease traffic flow, enhance connectivity, and improve urban mobility for millions of commuters, residents, and businesses in the city.-SIL.

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’unYanzu haka na samu labarin rasuwar shugaban matasan Jam’iyyar APC a karamar hukumar I...
23/06/2025

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un

Yanzu haka na samu labarin rasuwar shugaban matasan Jam’iyyar APC a karamar hukumar Illela ta jihar Sokoto, Daya daga cikin kananan Hukumomi takwas da nake wakilta, Alhaji Abdullahi Mirdiya Amarawa wanda ya rasu a safiyar yau a asibitin koyarwa ta Usmanu Dan Fodio Teaching Hospital Sokoto bayan Gajeruwar rashin lafiya.

Wanda kafin rasuwar sa ya kasance Dan siyasa na gari wanda ya jajirce wajen tabbatar da cigaban Jam’iyyar Apc a karamar Hukumar Illela.

Ina mika ta’aziyyata ga iyalansa, da daukacin al’ummar karamar hukumar Illela, da duk wadanda s**a yi jimamin rasuwarsa.

Allah (SWT) ya gafarta masa kurakuransa, Ya kuma ba shi Aljannatul firdausi.-SIL.

Inna Lillahi Wainna Ilaihi Raji'un.Harin da ya kai ga kashe ’yan uwanmu da ba su ji ba ba su gani ba a kauyen Tsabre da ...
15/06/2025

Inna Lillahi Wainna Ilaihi Raji'un.

Harin da ya kai ga kashe ’yan uwanmu da ba su ji ba ba su gani ba a kauyen Tsabre da ke mahaifata karamar hukumar Isa, Daya daga cikin kananan Hukumomi (8) da nake wakilta ya kasance mafi muni, mummuna, muni da kyama ta yadda bansan yadda zan misalta ba.

Abin takaici ne cewa a lokacin da mutanen da ba su ji ba ba su gani ba ke gudanar da ayyukansu na yau da kullun da kuma neman halalin su, wasu kuma suna gefe suna shirya mugun tanadi don kawo cikas ga zaman lafiyar wannan al'umma.

Abin da masu aikata wannan aika-aika s**a yi, abin Allah wadai ne, kuma ina kara kira ga jami’an tsaro da su kara kaimi duk da nasan irin kokarin da suke domin kakkabo masu aikata wannan aika-aika.

Haka kuma na mika sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda s**a rasa 'yan uwansu, ina addu'ar Allah ya jikan wadanda s**a rasu ya basu Jannatul Firdaus, ya kuma baiwa iyalai karfin gwiwar jure rashi mai raɗaɗi mara misaltuwa, Allah ya kawo muna karshen wadannan tashe-tashen hankula baki daya.-SIL.

Address

Sokoto

Telephone

+18038177706

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Senator Ibrahim Lamido posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share