Daula Hausa News

Daula Hausa News Daula Hausa News Gidan Jarida ne da suke kawo muku ingantattun labarai daga sassa daban-daban a faɗin Najeriya dama Duniya baki ɗaya.

Kuci gaba da kasancewa damu a koda yaushe.

10/05/2025

Wane fata kuke yiwa tashar Daula Hausa News ❓

06/05/2025

Daula Hausa News taku ce 💪

03/01/2025

Daula Hausa News 💪

16/11/2024

Kuci gaba da kasancewa damu domin samun sahihan Labarai na gaskiya akan sabon gidan jaridar mu na Daula Hausa News

Ronaldo - wanda yanzu haka ke wasa a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Al Nassr FC a Saudiyya, ya samu mabiya miliyan 10 a YouTub...
23/08/2024

Ronaldo - wanda yanzu haka ke wasa a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Al Nassr FC a Saudiyya, ya samu mabiya miliyan 10 a YouTube cikin kwana guda, sannan kuma ya samu mabiya miliyan guda a cikin awa ɗaya da rabi.

Ƙarin bayani - https://bbc.in/4dAAtHa

LAIFIN DA SARKIN GOBIR YAYI AKA KASHE SHIDaga Datty Assalafy Gwamnatin jihar Sokoto ne ta kira taro kan sha'anin tsaro (...
22/08/2024

LAIFIN DA SARKIN GOBIR YAYI AKA KASHE SHI

Daga Datty Assalafy

Gwamnatin jihar Sokoto ne ta kira taro kan sha'anin tsaro (security council meeting) wanda ya hada da manyan Sarakuna na jihar

Bayan kammala taro kan tsaro, an umarci Sarkin Gobir akan ya sanya hannu a takarda ya amince fulanin daji su dawo cikin gari, wai za'ayi sulhu

Shi kuma Sarkin Gobir yace gaskiya ba zai iya saka hannu ba, domin baya so ace shine yayi sanadin dawowar barayin daji cikin gari wadanda akace wai sun tuba, yace shi bai san da wani ido zai kalli al'ummarsa ba idan haka ta faru

Yace amma duk da haka shi bai da ikon ya hana Gwamnati aiwatar da abinda take so, amma dai shi ba da sa hannunsa ba

To bayan kammala taron ne akan hanyarsa na dawowa aka tura barayin dajin s**a kamashi tare da yaransa, wanda daga karshe s**a kashe shi, da ma shi din ake son kashewa saboda bai bada hadin kai aci amanar mutanen sa ba, don haka kisan sa ba komai bane face siyasa

Duk wulakancin duniyar nan da azabtar wa sun masa, yayi ta kuka yana rokon Gwamnatin jiha ta taimaka masa gashi bai da lafiya ga tsufa amma Gwamnati tayi biris da shi

Haka nan babu wani bayani na agaji gareshi daga Sarkin Musulmi b***e sauran takwarorinsa manyan Sarakuna masu daraja ta daya irin nasa, duk sun yi watsi dashi, wai a hakan sune suke wakiltar Musulunci a yankin Arewa

Ni dai ban ga wani abinda ya rage mana ba, yaki kam an gama cinye mu da shi, siyasar Demokaradiyya ta lalata komai, babu wani abu mai mutunci da daraja da ya rage mana

Dole mu tashi mu nemi mafita, 'yan siyasa ba zasu iya ba, sunci amanarmu, Sarakunanmu ba zasu iya ba saboda tsoron kujeran mulkinsu, Malamai ba zasu iya ba domin wasu daga cikinsu da ake jin muryansu sunci amana, sun karbi kudi sun sayar damu a hannun miyagu

Allah Ka tausaya mana, Ka bamu mafita na alheri.

YANZU-YANZU: Kotu ta ayyana Gawuna a matsayin zababban Gwamnan jihar Kano.
20/09/2023

YANZU-YANZU: Kotu ta ayyana Gawuna a matsayin zababban Gwamnan jihar Kano.

Wannan shine abinda mahaifiyata ta samu, a matsayin tallafi da Gwamnatin jihar Nassarawa ta raba mana, kamar yadda matas...
28/08/2023

Wannan shine abinda mahaifiyata ta samu, a matsayin tallafi da Gwamnatin jihar Nassarawa ta raba mana, kamar yadda matashi Shuraih Usman, ya bayyana a shafinsa na Facebook.

Da wasu s**a yiwa Matashin tambaya me k**e da mamaki, ya musu karin bayani a kasan comment na rantsuwa da Allah da cewa a hakanma mahaifiyar tashi ta samu da yawa, wasu ko 'yar taliyar ma ba'a saka musu ba. Allah ya kyauta.

Najeriya kenan, na ma rasa me zance 😢

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UNWasu mar*assa imani a jihar Bauchi, sun yanke wasu sa*ssa a ji*kin wannan yaron, sun...
27/08/2023

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN

Wasu mar*assa imani a jihar Bauchi, sun yanke wasu sa*ssa a ji*kin wannan yaron, sun boye gaw*arshi a cikin sokawe na ramin bandaki.

Sunan yaron Muhammad Abideen, bai wuce shekara guda ba, ance ankai tsawon kwanaki 8 ana nemanshi sai yau aka tsinci kawar tashi a cikin ramin shadda, na makarantar da mahaifiyar sa take a Games village da ke jihar Bauchi. Allah ya kyauta.

✍️ Comr Abba Sani Pantami

DA DUMI-DUMI: Alhaji Aliko Dangote, ya sake zama mutumin da yafi kowa kudi a Afirka, ya tara sama da Dala biliyan 11Daga...
27/08/2023

DA DUMI-DUMI: Alhaji Aliko Dangote, ya sake zama mutumin da yafi kowa kudi a Afirka, ya tara sama da Dala biliyan 11

Daga Comr Abba Sani Pantami

Aliko Dangote ya dawo da kambinsa a matsayin wanda ya fi kowa kudi a Afirka bayan da ya yi rasa matsayin ga hamshakin attajirin Afrika ta Kudu.

Adadin kudin Dangote a yanzu na kara haurawa duk da matsin karyewar darajar Naira a cikin kwanakin nan na baya.

A cewar Forbes, dukiyar dan kasuwan na fannin masana'anta ta haura zuwa dala biliyan 11.2 a yau Lahadi, 27 ga Agusta, 2023.

Wannan yana nuna karuwar 8.73% ko kuma dala miliyan 900 a dukiyar tasa idan aka kwatanta da dala biliyan 10.3 da ya mallaka a farkon watan Agusta.

Karin dukiyar Dangote a yanzu ta cike gibin da ke tsakanisa da babban abokin hamayyarsa, hamshakin attajirin Afrika ta Kudu Johann Rupert.

A cewar Forbes, Rupert yana da kudi dala biliyan 10.2 ya zuwa ranar Lahadi 27 ga watan Agusta, wanda ya yi kasa da na Dangote da dala biliyan 1 da Dangote.

A farkon watan Agusta, Forbes ta ruwaito Rupert yana da mallakar kudin da s**a kai dala biliyan 11.8. A cikin kwanaki 23 da s**a gabata, Rupert ya yi asarar sama da dala biliyan 1.1.

Karuwar arzikin Dangote ya biyo bayan irin ribar da ya kwasa daga kamfanoninsa na kasuwanci a kasuwar musayar hannayen jari ta Najeriya, musamman kamfanonin simintinsa a makon jiya.

Bincike ya nuna cewa a cikin kwanaki 8 kacal arzikin Dangote ya karu da dala miliyan 200.

Tankar ruwa ta ta*ke matashi Hassan a garin Dukku, jihar Gombe. A yau Asabar tankar ruwa ta ta*ke matashi Hassan Basheer...
26/08/2023

Tankar ruwa ta ta*ke matashi Hassan a garin Dukku, jihar Gombe.

A yau Asabar tankar ruwa ta ta*ke matashi Hassan Basheer El-Mangas, a shatale-talen tsakiyar garin Dukku da ke jihar Gombe. Tuni an sallaci matashin, kamar yadda addinin mus*ulunci ya tanadar. Muna mishi Addu'ar Allah ya jikanshi da Rahama.

📷 Labarun Kasar Dukku

INNAH LILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN Allah ya karbi rayuwar Goni. Malam Kabir (Abu Sumayya), yana tsaka da Sallar jumm...
25/08/2023

INNAH LILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN

Allah ya karbi rayuwar Goni. Malam Kabir (Abu Sumayya), yana tsaka da Sallar jumma'a a yau.

Ance a jiya Alhamis ma ya gabatar da karatun Daurah a kan Ilimin Tajwid a masallacin Kandahar Rijiyar Lemo da ke Kano. Muna mishi Addu'ar Allah ya jikanshi da Rahama idan tamu tazo Allah yasa mu cika da imani.

✍️ Comr Abba Sani Pantami

Address

Sokoto

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daula Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share