13/09/2021
KARE KAI: Shehin Malami a Sokoto Ya Nemi Gwamnati Ta Bashi Bindiga Domin Shiga Daji Don Fatattakar Yan Ta'adda, Ya Kuma Soki Dokokin da Aka Sanya a Sokoto.
Fitaccen malamin addinin musulunci na jihar Sakkwato dake arewacin Najeriya Sheikh Bello Yabo ya bukaci gwamnati ta mallaka masa bindiga tareda hada shi da jami'an tsaro domin ya fatattaki yan ta'adda a dazuka.
A cikin wani dogon bayani na babban malamin wanda ya gudanar a Mumbarin wa'azin sa ya ce, ya damu kan halin matsalar rashin tsaro a jihar da kasar Najeriya.
Sheikh Bello Yabo ya soki gwamnatin jihar Sakkwato kan matakin sanyan dokar hana shiga da fice da itatuwa a cikin mota da kuma haramta cin kasuwannin mako-mako domin dakilar da harkar ta'addanci a jihar.
Babban malamin ya ce, sanya dokar hana shigowa da itatuwa zai jefa al'umma cikin wani hali na kumci. Ya ce sam matakin bai yiba komai bai nuna alamun shawon kan matsalar tsaron.
"Tun harkan nan ta bace, tun da sojoji da jami'an tsaro sun yi kadan mu gamu bamu aikin komai a dauke mu abamu bindiga domin tinkarar yan ta'adda"
"Ire-ire na masu son shiga daji don ceto kasar nan su na da yawa sosai to a bamu dama mana, Amma bai yuwuwa wasu yan tsirarrun mutane sun yi kanfin cikin daji sun gagari gwamnatin Najeriya"~Inji Bello Yabo
Sheikh Bello Yabo ya ce, abin kumya yayi yawa a idon shuwagabannin Najeriya na kin kawo karshen yan ta'adda.
Babban malamin yace, sanya dokar hana shigowa da itatuwan abunci da haramta cin kasuwanni zai janyo matsatsi ga al'umman jihar musamman talakkawa. Ya ce zai dauki iyalansa duka ya kaiwa gwamnan Sakkwato su domin ya ciyar dasu.