Faruk Sidi Attahiru

Faruk Sidi Attahiru Network engineer
ICT by profession
Laboratory scientist
Student in Hauza Ilmiyyah
Scouter
Activist

Bazamu saki jika da wadanda tun zuwan Musulunci suke karya Alkawari ba._Faruk Sidi Attahiru A tarihin Musulunci, Manzon ...
24/06/2025

Bazamu saki jika da wadanda tun zuwan Musulunci suke karya Alkawari ba.

_Faruk Sidi Attahiru

A tarihin Musulunci, Manzon Allah (s.a.w.w) ya yi sulhu da wasu ƙabilun Yahudawa a Madina da kewaye, Amma da yawa daga cikinsu sun warware alkawari ko yin cin amana.

Bari mu dauki Darasi daga yin sulhu da jerin wasu daga cikin manyan ƙabilun Yahudawan da hakan ya faru da su:

1. Banu Qaynuqa‘a

Sulhu Bayan hijira zuwa Madina, Manzon Allah (s.a.w.w) ya amince da zaman lafiya da su a cikin Sahifatu Madina

Sun warware Sulhu Bayan da s**a keta doka da tozarta wata Musulma a kasuwa, Manzon Allah ya kai musu hari, aka ci su da yaki, aka kore su daga Madina.

Acikin Suratul Hashr, Aya ta 2, Allan ta'ala yana cewa:

"هُوَ الَّذِي أَخْرَجَ الَّذِينَ كَفَرُوا مِنْ أَهْلِ الْكِتَابِ مِن دِيَارِهِمْ لِأَوَّلِ الْحَشْرِ ۚ مَا ظَنَنتُمْ أَن يَخْرُجُوا وَظَنُّوا أَنَّهُم مَّانِعَتُهُمْ حُصُونُهُم مِّنَ اللَّهِ فَأَتَاهُمُ اللَّهُ مِنْ حَيْثُ لَمْ يَحْتَسِبُوا وَقَذَفَ فِي قُلُوبِهِمُ الرُّعْبَ يُخْرِبُونَ بُيُوتَهُم بِأَيْدِيهِمْ وَأَيْدِي الْمُؤْمِنِينَ فَاعْتَبِرُوا يَا أُولِي الْأَبْصَارِ"

Ma'ana: Shi ne (Allah) wanda ya fitar da waɗanda s**a kafurta daga Ahlul Kitab daga gidajensu a farkon korarsu. Ba ku yi tsammanin za su fita ba, su kuma sun yi zaton katangunsu za su hana su (azabar) Allah. Amma Allah ya zo musu daga inda ba su zata ba, kuma Ya jefa tsoro a zukatansu. S**a rusa gidajensu da hannayensu da kuma hannun muminai. To ku dauki darasi, ya ku masu basira.

2. Banu Nadir
Anyi sulhu da yarjejeniya tsakaninsu da Musulmi don zaman lafiya.

Daga baya s**a warware sulhu sunyi yunƙurin kashe Manzon Allah (s.a.w.w), sai aka kewaye su, s**a mika wuya, aka kore su daga Madina zuwa Khaybar.

A cikin Suratul Anfal, aya ta 56 Allah ta'ala yana cewa:

"الَّذِينَ عَاهَدتَّ مِنْهُمْ ثُمَّ يَنقُضُونَ عَهْدَهُمْ فِي كُلِّ مَرَّةٍ وَهُمْ لَا يَتَّقُونَ"

Ma'ana: "waɗanda ka yi yarjejeniya da su, sai su keta yarjejeniyar a kowane lokaci, kuma ba su jin tsoron Allah"

3. Banu Qurayza
Suma anyi sulhu dasu kuma sun kasance cikin yarjejeniyar sahifatu Madina.

Still suma s**a warware Sulhu, A lokacin yaƙin Khandaq, sun ci amanar Musulmi ta hanyar haɗin guiwa da maƙiya (Quraysh da Ahzab). Bayan nasarar Musulmi, aka kewaye su, aka yanke musu hukunci bisa dokarsu.

A suratul Ma'ida, aya ta 13, Allah madaukakin sarki yana cewa:

"فَبِمَا نَقْضِهِم مِّيثَاقَهُمْ لَعَنَّاهُمْ وَجَعَلْنَا قُلُوبَهُمْ قَاسِيَةً ۖ يُحَرِّفُونَ الْكَلِمَ عَن مَّوَاضِعِهِ وَنَسُوا حَظًّا مِّمَّا ذُكِّرُوا بِهِ ۚ وَلَا تَزَالُ تَطَّلِعُ عَلَىٰ خَائِنَةٍ مِّنْهُمْ إِلَّا قَلِيلًا مِّنْهُمْ ۖ فَاعْفُ عَنْهُمْ وَاصْفَحْ ۚ إِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ الْمُحْسِنِينَ"

Ma'ana: "saboda sun karya alkawarinsu, Mun la’ane su, Mun kuma sanya zukatansu masu tauri. Suna karkatar da kalmomi daga inda aka ajiye su, kuma sun manta da wani ɓangare na abin da aka tunatar da su. Kuma za ka ci gaba da samun cin amana daga cikinsu, sai kaɗan daga cikinsu. To ka gafarta musu, ka yi afuwa. Lallai Allah yana son masu kyautatawa.

Ayoyin nan suna nuni da irin waɗanda Manzon Allah (S) ya yi sulhu da su, amma a kai a kai suke karya yarjejeniyar, su taimaki maƙiyan Musulmai, su shiga yaƙi a bayyane ko a ɓoye.

A cikin tafsirin Al-Meezan na Allama Tabataba’i ya bayyana cewa: wannan irin rashin gaskiya da karya alkawari yana daga siffofin ɗabi’ar Yahudawa a tarihi, kuma wannan aya tana umarni ga Musulmi su kasance masu wayo wajen ma'amala da irin waɗannan mutane, su rika kula da amintaka da tsaro.

DARASI: Kada Musulmi ya yarda da wanda ya saba karya yarjejeniya, musamman idan addini da rayuwar al’umma na cikin haɗari. Tun kafa haramtacciyar Isra'ila ba'a taba yarjejeniya da ita ko sulhu batareda ta karyashi ba.

Allah yasa mu hankalta yakuma cigaba da bama Jamhuriyyar Musulunci ta Iran kariya yakuma shiga Al'amarinta tareda dubun kariya ga Jagoranta Sayyid Ali Khamena'i (H).

21/06/2025

صباح الخير 🤍❤️🤍

Al'ummar Najeriya mudauki Darasi daga Amfanin samarda hukuma Islamiyya _Faruk Sidi Attahiru A ka'ida ta hankali da yan a...
18/06/2025

Al'ummar Najeriya mudauki Darasi daga Amfanin samarda hukuma Islamiyya

_Faruk Sidi Attahiru

A ka'ida ta hankali da yan adamtaka babu wani mutum da yakeson rayuwar Bauta, wato yazama bawan wani Wanda ba abinda yake bautama ba. Amma Amurka ta dage sai ta karyar wanann ka'idar, Amurka da karuwanta su inmadai kazama bawansu kosu kasheka basu yarda akwai dama ta uku ba shiyasa kullum suke barazanar kisa.

Wannan karfi da muke ta gani Muna jinjinawa Daular Musulunci ta Iran, ta samo Asali ne daga amsawar Al'ummar Iran ga Imam Ruhullah Almusawi Al-Khomeini (QS) dakuma kangarewa Azzalumai da zalunci na danniyar turawa da fada ga yada fasadi da bayyana fasikanci.

Irin wannan Kiran ne fa da neman samun matsayi da daukaka da yanci Maulana Sayyid Ibraheem Alzakzaky (H) yakeyi shekara da shekaru, duk wanann zaluncinda kukaga anayi masa da yunkurin bata masa suna da son ganin an baje da'awar sa da kisan mabiyansa Dan kar ya samarda karfi ne Irin na Iran.

Ya kuke gani idan muka dafawa Sayyid Zakzaky (H)?

1. Zamu tsira daga kangin Bauta da danniya, mu samu tsari mafi girma da dacewa ga rayuwar Dan Adam wato (Musulunci)

2. Zamu tsayu da kafafunmu da karfafa masana'antu da kirkira, saboda rashin Dogaro da kasashen waje na iya tilastawa najeriya ta inganta masana'antu, Noma da fasaha, Kuma haka zai habaka local production da rage shigo da kaya

3. Zamu tsira da rayukanmu da dukiyoyinmu daga hannun Amurka da Isra'ila wurin kaucewa hare haren kungiyoyin ta'addanci da kabilanci da s**a kakaba mana

4. Arzikinmu ya zama namu, zamu hanasu satarda suke mana Kuma su kira mu da matalauta, karshe su shigo da sunan kawo tallafi sai su kirkiri kungiyoyin ta'addanci domin dauke hankali daga sata da bannarda suke

5. Zamu samu zaman lafiya da karfin Tattalin arziki, saboda munada Arzikin Mai da Noma sannan Munada Ruwa

6. Munada ma'adanai masu daraja da zamu iya mallakar kowane Irin makamin yaki domin kariyar Kai fiye sauran kasashen duniya

7. Zamu samarda Ingantaccen tsarin Ilimi da fasahar bincike zamu daina sayen kaya daga kasashen Turai saboda Najeriya zata daina Dogaro da manhajojin waje, ta kirkiri tsarin ilimin da ya dace da rayuwar yan kasarta da Al'adunta da tarbiyyar yayanta

8. Karfafa ikon Najeriya da zatafi Dogaro da kanta wajen yanke shawara a Siyasa da Tattalin arziki dakuma karancin shiga cikin gwamnati daga kasashen waje

9. Zamu rage tasirin Al'adu da Addinan waje, wannan Kuma zai haifarda karfafawa da girmama Al'adu da Ɗabi'unmu na gida

10. Zamu Bunkasa Siyasa Mai cikakken yanci, baza'a dinga ganin matsin Lamba daga manyan kasashe ba a zaben shugabanni ko tsarin Mulki, Kuma munada damar yin Alaka da kasarda mukaga dama

Dan haka najeriya na iya samun ƙarfi da cikakken yanci idan Al'ummarta ta shirya da gaske ta gina masana'antu, tsaro, ilimi, da shugabanci nagari. Amma hakan na bukatar shiri, haɗin kai, da shugaba mai hangen nesa, Mai jin tsoron Allah, Wanda ba Dan maula ba, Kuma Wanda ba yaron yan Siyasa ba irin Sayyid Zakzaky (H)

Muyi nazari sosai Kuma mu farka mu dafawa wannan Bawan Allah wurin tsamo kasarmu da Al'ummar mu daga tarkon makiyanmu Kuma makiya Addininmu da kasarmu.

Allah yasa mudace.......

YAKAMATA KASAN KAI WANENE KUMA MENENE WAZIFARKA_ Faruk Sidi Attahiru Dan Allah kowa ya tsaya Matsayin sa wurin Ɗauko Lab...
16/06/2025

YAKAMATA KASAN KAI WANENE KUMA MENENE WAZIFARKA

_ Faruk Sidi Attahiru

Dan Allah kowa ya tsaya Matsayin sa wurin Ɗauko Labarai da kawosu shafuka da zaurukan sada zumunta.

A ƴan kwanakin nan anata gwabza yaki tsakinin Rundunar Allah (Daular Musulunci ta Iran) da ta Shaiɗan (Israel da Iyayen gidanta), sai dai Abin mamaki kowa yakoma Dan jarida harda Malamai.

Malami da yak**ata ya rika kawo tarihi da nasarorin wadanda s**a riki Allah da yadda Allah yake taimakon Raunana dakuma kawo Ayoyi da Hadisai dake nuna nasara ta Muminai ce, Amma Shafukansu sunkoma na kawo Labarai, labaran nan da kowa zai iya daukowa ya kawo.

Maganar gaskiya kowa da inda yafi kwarewa, Kuma rashin kawo Labarai ga Malami ba nakasu bane saboda ba fanninshi bane, Sai kaga Malami yana Ɗora video na (AI) a shafinsa da sunan Musulunci yayi nasara, nasan da yasan wannan AI ne da bai Dora ba, Wannan Kuma yasamo Asali da shiga ayyukan wasu da barin tasa wazifar da Dan Media bazai iya ba.

Wannan hali da muke ciki Babu Wanda bazai iya bada gudumawa a fannin da yake ba, karka yarda kace zakayi aikin wani, kowa yayi nasa sai Allah ya taimakemu gaba daya.

Wannan shawarace garemu gaba daya

Allah yasa mudace.......

13/06/2025

Abubuwan da ke faruwa a Iran Dan Allah a bar masana suyi magana, Kuma a guji ɗauko Labarai barkatai daga shafukan maƙiya dake raunata Muminai...

SHI ZAMAN AURE A KO INA ANA YINSA NE DAN ALLAH_Faruk Sidi Attahiru Al'amarin zaman aure ya takaitu ne ga zaɓi da ra'ayi ...
01/06/2025

SHI ZAMAN AURE A KO INA ANA YINSA NE DAN ALLAH

_Faruk Sidi Attahiru

Al'amarin zaman aure ya takaitu ne ga zaɓi da ra'ayi da Kuma yarjewa ta mutum biyu (Miji da Mata).

Idan Anyarda da tarbiyya da Addinin Mai nema a bashi ba tareda la'akari da Ina yake rayuwa ba, saboda Babu inda zama yake permanent koda a kasarku ne ballanta wata kasa da Babu dangin iya ballantana na Baba.

Yau ko a Arewa kake rayuwa kaje kudu aiki ko kasuwanci bana tsammanin zaka k**a hayar gida irin na garinku Kuma kayi rayuwa irinta gidanku ballanata kasarda ba taka ba

Wanda yaje neman Ilimi me ya haɗashi da zama babban gida a ƙasar waje? Shida yazo ya zauna ya ƙara gaba? Da har zaizama abin habaici gareshi da matarshi ko yazama abin cin zarafi garesu?

Wanda nidai iya sani na bansan wani Ɗalibi da yake cikin wahala ta zamantakewa ba, sai inshi ya dauko abinda yafi karfinsa yaki ya tsaya inda Allah ya ajiyeshi

YAKAMATA KUSAN WAƊANNAN ABUBUWAN

1. Ɗalibai anan Karbala da ita na sani matansu suna zuwa Asibitinda duk faɗin Arewa bansan Asibitinda takeda Facilities irin nasu ba.
2. Sannan suna rayuwa a muhallinda yafi kowane muhalli Aminci da tsaro,
3. Sanann Dukansu suna zuwa makaranta.
4. Bansan kalar wani Abinci da ake ci a gidan Mai kuɗi a najeriya da matan Ɗalibai basa ci ba, bal ma Abinci mafi daraja da tsada a Iraqi da ko balarabe yasan na masu kudi ne shi suke ci.
5. Majority ɗinsu suna kasuwanci, mazajensu basu tauyesu ba
6. Matan Ɗalibai suna saka sutura wacce Itace mafi tsadar sutura har a wurin balarabe ballanta bahaushe.

To Dan Allah inma Dan jin dadin duniya ne menene abin ayi wata gori anan? Ko in anga wata zata aure wani saboda baƙin ciki sai a fara ƙananun maganganu da kushe mijin da cewa wai Babu walwala a Iraqi kullum ana harami, Alhali Haramin nan shine mafi darajar Muhalli a Iraqi k**ar yadda waɗanda suke tafiya Aikin hajji ko Umara basuda wurin ɗaukar Hoto sai Masallacin Ka'aba da Masallacin Madina haka ma A Iraqi Babu Muhalli abin girmamawa da yakai na Imamai.

Sannan inbanda shirme me ya dameka ko ya dameki da Muhallinda wata take kwana da mijinta tunda ba'a kan t**i ko saman kanku suke kwana ba..

Yanada kyau ku Fahimci zaman Aure Dan Allah akeyinsa badan Muhalli, ko arzikinsa ba saboda Abubuwane da duka za'a iya rasawa Kuma za'a iya samu in Allah yaga dama

Kusani wallahi zama na Farinciki da soyayya da ƙauna da kulawa acikin kango yafi zama cikin Masarauta Amma cikin kaskanci da tozarci.

Allah yasa mudace

Shikenan Kaninmu yazama yayanmu 😂😂Malam Ahmad Aliyu Tangaza ya zama Ango, Allah ya sanya Alkhairi ya bada zaman lafiya d...
30/05/2025

Shikenan Kaninmu yazama yayanmu 😂😂

Malam Ahmad Aliyu Tangaza ya zama Ango, Allah ya sanya Alkhairi ya bada zaman lafiya da zuri'a Mai Albarka

11/05/2025

Banida Hanyar samarda Visa ta karatu kota ziyara A Iraqi, Amma dai kuyi taka tsan tsan da duk Wanda zaku bama kudinku neman visa zuwa tattaki.

WATA SHUBUHA DA TAKE YAWO DAGA WASU ƊALIBAI_ Faruk Sidi Attahiru Dalilin wannan rubutun shine na fahimci ana amfani da s...
10/05/2025

WATA SHUBUHA DA TAKE YAWO DAGA WASU ƊALIBAI

_ Faruk Sidi Attahiru

Dalilin wannan rubutun shine na fahimci ana amfani da salon rauninmu sai a ƙara raunata mu da cewa wai bazamu iya kafa gwamnatin Musulunci ba saboda bamuda kudi ko babu abinda mukayiwa Al'umma na azo agani.

1. TATTALIN ARZIKI: Sau da yawa nakejin labari Dan ni bantaba gani ko ji ba ace in ka hadu da Larabawa ko Iraniyawa wai abinda suke fara tambayarka shine Tattalin Arzikin Harka Islamiyya, Na'am bance bazaiyu ba Dan tayu akwai wadanda s**a tambaya ba, Amma inma sun tambaya to baizama Ma'auni ba, dalili kuwa shine Ana cewa wai suna tambayar yan'uwa Kamfani (company) nawa kuke dashi? Ko ace sunce Kuna da manyan gine gine k**ar nawa? Ko ace sunce wai Gwamnati tana lissafi daku a tsarin kasuwanci? Ko ace wai acikinku mutum nawa yake da karfin fada aji acikin Al'amarin kasuwanci?

To Tambaya: Dama ita wannan Da'awar ta Sayyid Zakzaky (H) ta komawa ga Addini ce ko ta kafa kasuwanci? Ko Hadafinta ya koma ne bude Kamfanuka? Ko yin Manyan gine gine? Ko aikinta shine samarda Manyan masu kudi a kasuwa ?

Abin nufi shine suna so s**e idan bamu mallaki wadannan Abubuwan ba bazamu iya kafa gwamnatin Musulunci ba saboda mu matalauta ne, Dama cewa s**ayi Babu tafiyarda bata bukatar Tattalin arziki sai Ince Maka hakane, Amma ba zaizama Ma'aunin nasara ko rashin nasara ba, Kuma bai k**ata yazama hanyar kara raunata zuciyar yan'uwa ba adaidai wannan lokacinda muke kallon nasara ba.

A yanzu Muna lokacin fata ne, lokaci ne da ake da bukatar yan'uwa su kara fahimtar inda aka dosa Kuma su cigaba da da'awa, Na'am ana bukatar kudi a da'awa, Amma a karfafi yan'uwa cewa ko bamuda kudi zamu iya, tunda duk kudinka gwamnati ta fika kudi Kuma zata iya rusa duk abinda ka mallaka Amma bazata iya rusa ingantacciyar fikirarka ba, Kuma bazata iya tsayarda isarda sako zuwa ga sauran Al'umma ba.

Yanada gayar muhimmanci mu daina shigowa da maganganu da suke nunawa Al'umma ce tafiyar nan akwai sauran aiki, irin cewa ai ba'ama k**a hanya ba, saboda duk Wanda yaji ance tafiya sai da Kamfanuka da gine gine da shiga kasuwa zaiga cewa ai bamu ma k**a hanya ba, sai a raunatarda Mai karfi shikuma Mai rauni sai a ƙara raunata shi.

Amma ai Mu Muna koyi da Da'awar Imam Khomeini (QS) ne, Lokacinda Malam Zakzaky (H) yazo Iraq a tattakin Bara 2024 ya gana da Ɗalibai a Karbala, cikin jawabinsa a gabana yake cewa: Masu cewa yak**ata a shiga gwamnati su kawo mishi inda Imam Khomeini (QS) yaje gidan gwamnati Shima yanzun nan zai hada kayanshi ya tafi, in hakane kenan Da'awar Imam Khomeini (QS) Ma'auni ce a wurinmu.

To yanada kyau Masu Jefa SHUBUHA su amsa Maka wadannan tambayoyin:

1. Shin lokacin Imam Khomeini (QS) a dai dai da'awarsa akwai Manyan Kamfanuka da suke aiki a karkashin Ikon Imam?

2. Shin lokacin Da'awar Imam Khomeini (QS) akwai wani Jirgi da yake tashi na kasuwa da Izinin Imam Khomeini (QS) ?

3. Shin da wace Miza ake gane Almajiran Imam Kuma dame wace Alama s**ayi suna? Kasuwanci ne ko ba kasuwanci ba?

4. Jami'a nawa ce Aka Gina bisa Ikon Imam Khomeini (QS) kafin ya kafa gwamnatin Musulunci?

5. Manyan Asibitoci nawane aka Gina a Iran da sunan yunkurin juyi kafin zuwan Imam Khomeini (QS)?

6. Tituna nawa aka ginawa Al'umma da sunan Da'awar Imam?

7. Makarantu nawa aka Samar da sunan yunkurin juyi?

2. HEZBOLLAH: Da yawan ISHKALIN da ake bugama yan'uwa shine Hezbollah, bansani ba kodan wani yaje Lebonon ko Iran ko Iraq ne sai yazo yayita baje kolin labarai ba Oho, ko ma menene ana yawan bada misali da Hezbollah.

Yanada kyau ku sani masu kawo labaran nan basu iya banbance Hadafin Harka da Hadafinda yasa aka kirkiri Hezbollah.

Akwai wani Malamin mu a makaranta yake cewa bari inyi muku na Mahaukaci "Duk Africa da kasashen Larabawa Babu kasarda take da kayan yakinda Hezbollah take dashi" Kuma wannan Gaskiya ne, ka Kalli Abokanan Karawarta kagani

Ko ba'a ce Maka Hezbollah akwai kasarda take goyon bayan ta ba to matsayinka na Mai hankali yak**ata ka gane da kanka, Tunda kake ka taba ganin wata kungiyar Soji da ba Karkashin gwamnatin kasa take ba Kuma tayi tayi Irin yakin 2006 da kasa irin Isra'ila tayi nasara? Kuma yanzu take kan Fafatawa da Isra'ilar harda Amurka Amma taki yin rauni kataba ji ko a tarihi?

Saboda haka maganar a rika kwatanta Da'awar Harka Islamiyya da Motsin Soji na Hezbollah baiyi ba, saboda Hadafin su ba guda ba, Dan kawai yan Hezbollah sunada fikira irin tamu bashi ya nuna Uslubinmu guda dasu ba.

Wanda a bayyane yake Hezbollah a salon jagorancinta tanada matakai kusan goma daga wannan sai wannan, Wanda mu bamu da wannan jagora Daya muke dashi sai tarin Almajirai, kowa kagani Almajiri ne ko waye shi.

Sannan Hezbollah majalisar shura take dashi, mu Kuma bamu dashi, bugu da Kari Hezbollah Structure take dashi mukuma Alzakzaky (H) kadai ne, Amma saboda ansamu kauyawa cikin masu zuwa karatu to duk wani Abu da s**a ga ya burgesu basu tambaya ya akayi aka Samar dashi? Kuma menene Dalilin Samar dashi kawai zasuyi hukuncin ai munfi yan Hezbollah yawa Amma mu kullum mune koma baya, daga nan a fara Zagin Malam wane da Forum Kaza akan cewa su s**a kawo ci baya.

Na'am bance Babu matsaloli ba, Amma yadda ake nuna cewa mune koma baya sannan Harka tafi shekara 40 Amma Babu inda taje, sannan bamuda Tattalin arziki, k**ata ma yayi ace zuwa yanzu ma munada manyan Asibitoci da Manyan makarantu da Manyan store na ajiye Abinci.

Ni da cewa akayi Mu'assasoshinmu da forums sunda rauni yak**ata mu gyara sai Ince na gamsu ko ace ya za'ayi Harisawa ko yan Jasaz suyi karfin Hezbollah, Amma badai Harka Islamiyya ba, Amma duk Wanda ya tashi bazaizo da maganar da ke karfafa mutane ba sai dai ace mu Kaza, mu bamuda Kaza, Dan kawai yaje Iran ko Iraq ko Lebonon? Majority din wadannan da suke bada wadannan labaran Mutanen saman t**i ne suke haduwa dasu, saboda su suke kallon gangar jikin harka Amma masu hankalinsu Ruhinta suke kallo.

3. WAI KO ANBAMU KASAR BAZAMU IYA RIKEWA BA: Duk wannan salo ne na dankwafe muminai na ganin cewa bazasu iya ba, akwai ma Wanda ya taba cewa ko Ministry Daya bazamu iya rikewa ba saboda angama saka mishi virus a kwakwalwa, saboda a lissafinsu yanda suke tunani to haka harkar take kokuma Hakan zata zauna, Akwai wata magana da Malam Zakzaky (H) yana yawan bada Misali da ita, cewa "Idan a Garinku akwai teku Kuma Kuna kamun kifi a wurin sai wani yazo yace zai kwashe wannan ruwan ya hanaku k**a kifi me zaku ce masa? Sai malam yace ai sai kuce ya bada karfi saboda bazai iya ba" sai Malam (H) su wadannan Azzaluman sun san zamu iya shiyasa suke jin tsoro.

Shiko Wanda ya tsallaka yabar najeriya ya tafi karatu indai ba Allah ya tsareshi ba to kullum kallon yake wadannan da aka Tara fa jahilai ne, gwamnatin Musulunci ce za'a kafa a haka? To wazai jagorance ta?

Lallai wannan kalubale ne ga Ɗaliban Ilimi da su rika karfafar yan'uwa da kalamai masu karfafawa ba raunata su ba.

MULAHAZA: Ni ban Kore cewa ayi Kasuwanci kuma ban Kore cewa munada bukatar kafa Tattalin arziki Amma Ina cewa baik**ata A rika kwatanta Da'awar Harka Islamiyya da sauran Yan muqawama ba Dan kawai suna kan Fikirar Imam Khomeini (QS) ba, Kuma bai k**ata ana amfani da kalmomi na nuna cewa harka tanada raunin kasuwanci ba, Dan bashi ne asasi ba. Saboda da irin wadannan lissafe lissafen ake canzawa masu raunin Imani tunani cewa ya za'ayi A kafa gwamnatin Musulunci kuda bakuda komai Kuma baku mallake komai ba Kuma kunqi shiga Gwamnati.

Kuma bai k**ata a rika tsoratarda mutune cewa Babu Hope (Fata) ba, saboda cewa wai bamuda Mu'assasoshin Taimakon Al'umma bamuda manyan Kamfanuka, bamuda manyan Asibitoci da Mak**antansu.

Allah yasa mu dace ....

Duk acikin Hidimar Bikin Auren Ɗan'uwanmu Kuma Abokin karatunmu Sidi Ammar Ubale     Allah ya sanya Alkhairi ya bada zam...
10/05/2025

Duk acikin Hidimar Bikin Auren Ɗan'uwanmu Kuma Abokin karatunmu Sidi Ammar Ubale

Allah ya sanya Alkhairi ya bada zaman lafiya da zuri'a Mai Albarka.

Address

Sokoto

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Faruk Sidi Attahiru posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Faruk Sidi Attahiru:

Share