12/08/2026
Kamfanin Talla na FATSAM Advertising and Media Limited ta ƙaddamar da wani shiri na haɗin gwiwa da ALU TV Nigeria, da nufin faɗaɗa damar talla tare da ƙarfafa hulɗa da ’yan kasuwa, ƙungiyoyin kamfanoni da sauran masu ruwa da tsaki.
A yayin ziyarar ban girma da s**a kai ALU TV Nigeria, Manajan Darakta naFATSAM, Abdulfatai Abdusalam, ya ce haɗin gwiwar da ake shirin kafawa zai taimaka wa ’yan kasuwa da ƙungiyoyi wajen tallata kamfanoninsu, kayayyaki, ayyuka da shirye-shiryensu ga dimbin masu kallo ta kafafen watsa shirye-shiryen ALU TV.
Ya jaddada muhimmancin ingantaccen talla wajen gina martabar kamfani, faɗaɗa kasuwa da kuma haɗa ƙungiyoyi da masu kallo da sauraro.
Da yake karɓar tawagar, Babban Manajan ALU TV Nigeria, Bashar Abubakar, ya yi maraba da wannan shiri, tare da bayyana shirye-shiryen tashar na yin aiki tare da FATSAM wajen samar da ingantattun hanyoyin talla da tallata hajojin abokan hulɗa.
Ya kuma bayyana shirin ƙaddamar da wani shirin talabijin mai amfani da harsuna da dama, wanda zai ƙunshi Hausa, Yarbanci da Igbo, da nufin tallata ’yan kasuwa da kamfanoni, tare da inganta haɗin kan ƙasa, fahimtar al’adu da zaman lafiya tsakanin al’umma.
A yayin ziyarar, Bashir Rabe Mani ya gabatar da jawabi cikin Hausa, Mustapha Olatunde cikin Yarbanci, yayin da Sandra Ogechi Nwabueze ta gabatar cikin Igbo. Wannan ya nuna irin damar da shirye-shiryen harsuna da dama ke da wajen haɗa masu talla da al’umma masu bambancin harsuna a faɗin Najeriya.
Ana sa ran haɗin gwiwar zai ƙara faɗaɗa damar talla, bunƙasa kasuwannitare da ƙarfafa hulɗar kasuwanci tsakanin kafafen yaɗa labarai da ’yan kasuwa.
Ku kasance tare da ALU TV Nigeria Domin Haɗa ’Yan Kasuwa, Kamfanoni da Masu Kallo da Sauraro.
Talata, 11/8/2026