Hon. Kabir Wada Mawashi

Hon. Kabir Wada Mawashi Labarun gida da na waje

Tarihin Mustapha Muhammad InuwaMustapha Muhammad Inuwa ɗaya ne daga cikin fitattun ’yan siyasa kuma masu ilimi na Jihar ...
22/07/2025

Tarihin Mustapha Muhammad Inuwa

Mustapha Muhammad Inuwa ɗaya ne daga cikin fitattun ’yan siyasa kuma masu ilimi na Jihar Katsina. An haife shi a cikin garin Danja, kuma ya taso cikin gida mai ɗabi’a da ƙaunar ilimi. Bayan ya kammala karatunsa, ya samu damar shiga aikin koyarwa a manyan makarantu.

Tun daga shekarar 1984 har zuwa 1997, Mustapha Inuwa ya yi aiki a matsayin malami a Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo dake Sakkwato, inda ya koyar da ɗalibai tare da bayar da gudunmawa wajen gina ƙwararru a fannin ilimi. Wannan aiki na koyarwa ya ba shi kwarewa da gogewa a harkar ilimi da shugabanci.

A shekarar 2003, gwamnan jihar Katsina na wancan lokaci ya naɗa shi Kwamishinan Ilimi, inda ya jagoranci harkokin ilimi na jihar har zuwa 2006. A cikin wannan lokaci, ya yi ƙoƙari wajen inganta tsarin ilimi da ƙarfafa manufofin da s**a shafi ci gaban makarantu da walwalar malamai.

Daga 2006 zuwa 2007, an naɗa shi Sakataren Musamman (Special Secretary) na Gwamnatin Jihar Katsina, inda ya ci gaba da bayar da gudunmawa ga ci gaban jihar.

Bayan haka kuma, Mustapha Muhammad Inuwa ya hau babban matsayi a matsayin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina (SSG), inda ya rike wannan mukami na tsawon lokaci kafin ya ajiye shi domin ya shiga siyasa sosai.

A lokacin zaben gwamna na 2023, Mustapha Inuwa ya ajiye mukaminsa na SSG domin ya tsaya takarar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC). Sai dai kuma bai samu nasara ba, domin Dikko Umar Radda ne ya lashe zaben. Bayan haka, Mustapha Inuwa ya nuna kishin kasa da ɗabi’ar siyasa mai kyau, inda ya bayyana goyon bayansa ga Dikko Umar Radda tare da fatan alheri a mulkinsa.

Mustapha Muhammad Inuwa mutum ne da ke da kwarewa a harkokin gwamnati, ilimi, da siyasa, kuma ya kasance gwarzon da ake girmamawa a jihar Katsina da Najeriya gaba ɗaya.

Ta wannan fuskar.
15/04/2025

Ta wannan fuskar.

08/04/2025

Labari mai taɓa zuciya, labarin Jaycee Dogard.

Yarinyar da aka sace tu tana shekara 11.

Labarin gaske ne.

EFCC ta sake k**a Sirajo Muhammad Jaja, babban accountant na Jihar Bauchi, tare da wasu biyu, Aliyu Abubakar da Sunusi I...
08/04/2025

EFCC ta sake k**a Sirajo Muhammad Jaja, babban accountant na Jihar Bauchi, tare da wasu biyu, Aliyu Abubakar da Sunusi Ibrahim Sambo, bisa zargin yin safarar kuɗi da kuma ɗaukar Naira biliyan 70 daga kuɗaɗen gwamnati.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta musanta k**a su, tana cewa wannan lamari yana da alaƙa da siyasa kuma ana ƙoƙarin lalata shugabancin Gwamna Bala Mohammed.

Kungiyoyi k**ar Bauchi Accountability and Truth Awareness Front (BATA) ma sun yi s**a ga EFCC bisa zargin cewa suna yin binciken saboda siyasa. Duk da wannan, EFCC ta ce binciken da take yi yana cikin ƙoƙarin yaƙar cin hanci da rashawa da tabbatar da gaskiya a gwamnati.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Legas ta gano wata cibiyar haihuwar jarirai ba bisa ka’ida ba a yankin Ijegun na jihar.Bayan ...
08/04/2025

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Legas ta gano wata cibiyar haihuwar jarirai ba bisa ka’ida ba a yankin Ijegun na jihar.

Bayan samun bayanan sirri, jami’an ‘yan sanda sun kai samame a wurin a ranar 5 ga Afrilu, 2025, inda s**a k**a mai gudanar da wajen, Mariam Vincent mai shekara 35, da wasu mataimakanta biyu: Orie Ruth mai shekara 23 da Ujunwa Ifeanyi mai shekara 18.

A yayin wannan samame, ‘yan sanda sun ceto mata bakwai da aka sace, waɗanda s**a haɗa da: Precious (24), Magdalene (25), Adaobi (23), Princess (22), Ifeanyi (25), da Amaka (26), tare da yara uku: Destiny (yaro mai shekara 7), Miracle (yarinya mai shekara 5), da Success (yarinya mai shekara 2).

Waɗanda ake zargin sun amsa laifin sace mutanen daga sassa daban-daban na Jihar Legas domin gudanar da wannan cibiya ta haihuwar jarirai.

Gwamnatin jihar Kogi karkashin jagorancin Usman Ododo tare da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, sun mayar da...
07/04/2025

Gwamnatin jihar Kogi karkashin jagorancin Usman Ododo tare da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, sun mayar da martani mai zafi kan wani iƙirari da Natasha Akpoti ta yi game da wani boyayye shiri na kashe ta.

An daɗe dai ana cacar baki tsakanin shugaban majalisa Godwill Akpabio da Sanata Natasha.

Wasu ƴan bindiga daɗi da ba a san ko su waye ba, sun kashe eani ɗan ƙasar China da ƙarin wani ɗansanda.Kisan ya faru ne ...
07/04/2025

Wasu ƴan bindiga daɗi da ba a san ko su waye ba, sun kashe eani ɗan ƙasar China da ƙarin wani ɗansanda.

Kisan ya faru ne a Jihar Abia, har yanzu dai ƴansanda na binciken maharan.

Ƴanbindiga sun yi garkuwa da da mutum Hamsin a Jihar Katsina.Al'ummar ƙaramar hukumar Funtua ta jihar Katsina sun ce ƴan...
07/04/2025

Ƴanbindiga sun yi garkuwa da da mutum Hamsin a Jihar Katsina.

Al'ummar ƙaramar hukumar Funtua ta jihar Katsina sun ce ƴanbindiga sun shiga wasu ƙauyukanƙauyuka, inda s**a sace sama da mutum hamsin waɗanda s**a haɗa da mata da ƙananan yara.

Barayin sun kashe wasu ƙarin mutum shidda, bayan sun kai wani sabon hari a ƙaramar hukumar Dandume.

Address

Sokoto

Telephone

+2349075676327

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hon. Kabir Wada Mawashi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hon. Kabir Wada Mawashi:

Share