Iconic FM Nigeria

Iconic FM Nigeria Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Iconic FM Nigeria, Broadcasting & media production company, 1B After Miyetti Allah Roundabout, Sokoto.
(4)

08/06/2026

SHIRIN FASSARAR MAFARKI 08=06=2026

08/06/2026

FB-122212541492550796-0-Ab4cXi1O6ehECgZuw4wuGM4s

08/06/2026

Takaitattun Labaran Iconic tare da Zarah Abdullahi Marafa 8/6/2026

08/06/2026

ICONIC ENGLISH NEWS 08=06=2026

An yi garkuwa da dattawa 50 daga ƙauyen Magamin Diddi da ke gundumar Magami/Faru a ƙaramar hukumar Maradun yayin da suke...
08/06/2026

An yi garkuwa da dattawa 50 daga ƙauyen Magamin Diddi da ke gundumar Magami/Faru a ƙaramar hukumar Maradun yayin da suke kan hanyar gudanar da wani yunƙurin sulhu da 'yan bindiga.

Rahotanni sun ce Jammo, shugaban 'yan bindiga da ke iko da dajin Muntsira a ƙaramar hukumar Maradun ta jihar Zamfara, shi ne ya yi garkuwa da su.

Shugaban ƙaramar hukumar Maradun, Hon. Bello Dosara, ya tabbatar wa Daily Trust da faruwar lamarin, amma ya ce mutanen sun yanke shawarar ganawa da shugaban 'yan bindigar ba tare da amincewar gwamnati ba.

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su daina danganta laifuffuka da wa...
08/06/2026

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su daina danganta laifuffuka da wata ƙabila daya, yana mai cewa hakan na haifar da ƙiyayya tare da barazana ga haɗin kan ƙasa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, Obi ya ce mutane da dama a Najeriya sun sha fuskantar wariya da tsangwama saboda asalinsu na ƙabila.

Ya bayyana cewa a matsayinsa na ɗan kabilar Igbo, ya sha fuskantar hukunci da lakabi saboda ƙabilarsa, yana mai cewa irin wannan matsala ba ta Igbo kaɗai ba ce, domin yawancin ‘yan Najeriya sun taɓa fuskantar hakan.

Obi ya ce yana fahimtar halin da talakawan Fulani ke ciki, inda ake yawan kallon su a matsayin masu laifi saboda ayyukan wasu ‘yan ta’adda da masu aikata laifuffuka da ba su da alaƙa da su.

Ya jaddada cewa laifi ba shi da ƙabila, yana mai cewa barawo barawo ne, ɗan ta’adda ɗan ta’adda ne, sannan mai garkuwa da mutane ma mai laifi ne, ba wakilin wata ƙabila ba.

Tsohon gwamnan jihar Anambra ya buƙaci hukumomi su riƙa k**a tare da gurfanar da masu laifi gaban kuliya bisa doka, maimakon ɗora laifinsu kan daukacin wata ƙabila.

Obi ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su rungumi bambancin al’adu da ke cikin ƙasar tare da gujewa son zuciya da ra’ayoyin wariya da wasu ‘yan siyasa ke amfani da su domin cimma muradunsu.

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar ficewa daga jam’iyyar NDC bayan da jam’iyyar ta maye gu...
08/06/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar ficewa daga jam’iyyar NDC bayan da jam’iyyar ta maye gurbin wasu daga cikin ‘yan takarar ɓangaren Kwankwasiyya a Kano domin aiwatar da tsarin rabon kujeru na kashi 60/40 da aka amince da shi tun da farko, inda aka ware wa ɓangarensa kashi 60 cikin 100.

Rahotanni sun bayyana cewa NDC ta sauya wasu daga cikin sunayen ‘yan takarar da ɓangaren Kwankwasiyya ya gabatar a jihar Kano bisa zargin karya yarjejeniyar rabon muƙaman.

Wannan na kunshe ne a cikin wani rahoto da Daily Post ta wallafa bayan ta ga wata takarda da shugaban NDC na jihar Kano, Hon. Hussaini Isah Mairiga, ya sanya wa hannu.

Mairiga ya bayyana cewa an yi waɗannan sauye-sauyen ne domin tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma tun farko kan yadda za a raba muk**an jam’iyya da kuma tikitin takarar zaɓe tsakanin tsohon tsarin NDC da kuma ɓangaren Kwankwasiyya.

An kuma aika kwafin takardar zuwa ga jagoran jam’iyyar adawa ta NDC na ƙasa, Seriake Dickson, da Kwankwaso, tare da shugaban shiyyar Arewa maso Yamma na jam’iyyar NDC.

Gwamnatin jihar Zamfara ta bai wa rundunar ’yan sanda motoci masu sulke guda biyar don ƙarfafa ayyukan tsaro da yaƙi da ...
08/06/2026

Gwamnatin jihar Zamfara ta bai wa rundunar ’yan sanda motoci masu sulke guda biyar don ƙarfafa ayyukan tsaro da yaƙi da matsalar ’yan bindiga a faɗin jihar.

An miƙa motocin ne a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Gusau a madadin Gwamna Dauda Lawal ta hannun Mataimakin shugaban ma'aikata na fadar Gwamnati, Alhaji Nura Almajiri.

Yayin da yake karɓar motocin, Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Ahmad Muhammad Bello, ya bayyana cewa kayan aikin za su ƙara ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi wajen yaƙi da ayyukan laifuka tare da inganta tsaro a al’ummomin da matsalar ta shafa.

Gwamnatin jihar ta ce tura motocin zai taimaka wa hukumomin tsaro wajen ƙara kaimi a hare-haren da suke kai wa ƙungiyoyin masu ɗauke da mak**ai, tare da samar da yanayi mai aminci da zai ba manoma damar komawa gonakinsu cikin kwanciyar hankali.

Kwamishinan ’yan sandan ya kuma tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar tana nan daram wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma, inda ya ƙara da cewa hukumomin tsaro za su ci gaba da aiki tare domin fuskantar duk wata barazana ta tsaro da ka iya tasowa.

Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimakawa ƙoƙarin da ake yi na kawo ƙarshen ayyukan ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka.

Shugaban Majalisar Dattawa ta kasa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa yawaitar sace-sacen mutane, ayyukan ta’addanci da ...
08/06/2026

Shugaban Majalisar Dattawa ta kasa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa yawaitar sace-sacen mutane, ayyukan ta’addanci da kashe-kashe a lokacin da yake gwamnan Jihar Akwa Ibom ne s**a sa ya fara shirya zaman addu’o’i na kowane wata domin tunkarar matsalolin tsaro.

Akpabio ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi yayin wani taron ibadar cocin haɗin gwiwa na mabiya ɗariku daban-daban da aka gudanar a Cibiyar Kiristoci ta Kasa da ke Abuja, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta bana.

Yayin da yake waiwaye kan shekarunsa na mulki a matsayin gwamna, Shugaban Majalisar Dattawan ya ce sau da yawa yana tambayar kansa yadda al’amura za su kasance da ba a ci gaba da yin addu’o’i ba.

Ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya da kada su yanke ƙauna duk da ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta a halin yanzu.

Jam’iyyar NDC ta ƙaddamar da Kwamitin Sulhu na Ƙasa domin magance koke-koke da rashin jin daɗin da s**a biyo bayan zaɓen...
08/06/2026

Jam’iyyar NDC ta ƙaddamar da Kwamitin Sulhu na Ƙasa domin magance koke-koke da rashin jin daɗin da s**a biyo bayan zaɓen fidda gwani na baya-bayan nan da jam’iyyar ta gudanar.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Osa Director, ya fitar, ya bayyana cewa matakin na daga cikin muhimman shawarwarin da aka cimma bayan taro na biyu na Kwamitin Zartarwa na Ƙasa na jam’iyyar.

Sanarwar ta jaddada cewa jam’iyyar na ci gaba da sauya salonta zuwa cikakkiyar cibiyar siyasa mai ɗorewa, maimakon kasancewa wata jam’iyya da aka kafa na ɗan lokaci kawai domin cimma wata manufa ta siyasa.

An ɗora wa sabon Kwamitin Sulhu na Ƙasa alhakin ganowa da kuma sasanta mambobin da suke jin an nuna musu wariya ko kuma an tauye musu haƙƙoƙinsu a lokacin zaɓen fidda gwani. A lokuta da dama, irin waɗannan rikice-rikice na cikin gida kan haddasa rabuwar kai a jam’iyyu, don haka shugabannin NDC s**a gaggauta ɗaukar matakan tabbatar da haɗin kai a tsakanin mambobinsu.

Domin yaƙi da cin hanci da rashawa tare da tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da kuɗaɗen jam’iyya, NDC ta kuma sanar da fara sa ido mai tsauri kan kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe.

Address

1B After Miyetti Allah Roundabout
Sokoto
840101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Iconic FM Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share