10/09/2026
Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, ya ce idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasar Najeriya a 2027, zai yi hutun Sallah tare da Sarkin Musulmi, Sultan na Sokoto.
Obi ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Arise TV, inda ya soki Shugaba Bola Tinubu kan yadda yake gudanar da hutun Sallah a Legas.
Ya ce a matsayinsa na shugaban ƙasa, zai yi amfani da lokacin Sallah wajen haɗa kan ’yan Najeriya, musamman a arewacin ƙasar.
"Sallah da komai, shi (Tinubu) yana yin sa ne a Legas. Musulmi ne. Ni zan je Sokoto in yi Sallah tare da Sultan, mu haɗa kowa wuri guda, mu tattauna makomar ƙasar. Zan je Kano,” in ji Obi.
A wani ɓangare na hirar, Obi ya ce NDC za ta kafa wani tsarin da zai ba ta damar tura sakamakon zaɓe daga rumfunan zaɓe kai tsaye zuwa cibiyar tattara bayanai ta jam’iyyar a babban zaɓen 2027.