11/08/2025
BABBAN CIN AMANA: KIRA GA GWAMNATIN JIHAR SOKOTO
An samu rahoton cewa matasa uku ‘yan gida daya — Muazu Malam Shehu, Faruku Malam Shehu, da Malami Malam Shehu — ‘ya’yan Malam Shehu Bangi, wani dattijo mai shekaru 80 kuma malamin addinin Musulunci daga garin Rafi, karamar hukumar Bodinga, jihar Sokoto, sun gamu da mummunan zalunci.
A ranar Alhamis da yamma, wani jami’in tsaro mai suna Sama’ila daga Bodinga ya je gidansu domin k**a wani ɗan’uwansu da ake zargi da laifi. Bai same shi ba, sai ya nemi tafiya da Malam Shehu dattijo a matsayin madadin ɗan. Duk da bayanin dattijon cewa ɗan ya tafi gona, jami’in ya nace, har ya fara zagin shi. Matasan uku s**a yi masa kashedi kada ya ci gaba da zagin mahaifinsu.
Daga nan jami’in tsaron ya kira abokan aikinsa s**a iso da bindigogi, s**a shiga gidan, rikici ya barke, sai s**a bude wuta. Harbin ya ji wa matasan uku mummunar rauni, daya ma har a kansa. Yanzu suna Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo (UDUTH) Sokoto, yayin da aka dauke dattijon domin tsare lafiyarsa.
Wannan lamari babbar rashin adalci ce da kuma tsantsar zalunci. Muna kira ga Gwamnatin Jihar Sokoto, shugabanni masu tasiri, da malamai, su sa baki wajen ganin an kwatowa waɗannan bayin Allah hakkinsu tare da hukunta duk jami’in tsaro da ya aikata wannan aika-aika.
Ga wanda zai iya taimakawa, za a iya tuntubar Malam Ibrahim Ruwa ta 08038096278. Allah Ya isar musu.