20/05/2026
Babban Kwamitin da uwar jam’iyyar African Democratic Congress ta ƙasa ta tura ya kammala tantance ‘dan takarar majalisa na jaha inda ya amince da Hon. Muzammilu Almu Alkanchi ɗan majalisar jiha daga karamar hukumar Sakkwato ta Arewa ta 2.
Tantancewar na zuwa ne a matsayin wani muhimmin mataki na shirye-shiryen jam’iyyar gabanin zaɓe, wanda ke nuni da yadda ADC ke ƙoƙarin tabbatar da sahihanci da bin ka’idoji wajen fitar da ‘yan takara