16/08/2026
AKWAI KURA: GWAMNONIN JAM'IYYAR APC SU SHAFA WA KANSU RUWA
Babban darasi daga zaben kujeran Gwamnan jihar Osun da ya gudana jiya asabar
Ana dab da kammala kirga kuri'un zaben kujeran Gwamnan jihar Osun da aka yi jiya, sakamakon zabe na karamar hukuma daya ne kadai ya rage zuwa yanzu da nake rubutu
Ga sakamakon zaben:
👇
Accord: 487,553
APC: 420,164
ADC: 16,525
Jam'iyyar Accord Party ta bawa jam'iyyar APC mai mulkin Kasa ratar kuri'u 67,389, wanda hakan na nufin jam'iyyar APC ta fadi zaben jihar Osun
Gwamna mai ci Ademola Adeleke ya sake neman tazarce a jam'iyyar Accord Party, ya hadu da manyan kalubale kasancewar ba a jam'iyyar APC mai mulkin Kasa yake ba
Kafin a kai ga gudanar da zaben anyi ta samun manyan rikici na siyasa a jihar musamman tsakanin jam'iyyar Accord da APC da take son kwace mulkin
Akwai wani sanannen mawaki dan uwan Gwamna Adeleke da ake kira Davido, har karan Gwamnatin tarayya ya kai zuwa gaban Shugaban Amurka domin kar ayi amfani da karfin gwamnatin tarayya a murda zaben jihar Osun
Kusan Gwamnonin jam'iyyar APC gaba daya sai da s**a je jihar Osun shekaran jiya domin su bada gudunmawa wajen kwace kujeran mulki, har da Dr Abdullahi Umar Ganduje ya je, an tsaurara dukkan matakai na tsaro
To amma a karshe Allah Ya bawa Gwamna Adeleke nasara duk da karfin da jam'iyyar APC take da shi, zata iya murda zaben, amma ta bari akayi zabe na gaskiya, abinda ba'a yi zato ba
Magana ta gaskiya Gwamnonin jam'iyyar APC su shiga taitayinsu, su shafa wa kansu ruwa, kar su yi tsammanin zasu ci bulus a babban zaben 2027, murdiyan zabe zai zama tarihi, muna digital era ne, komai a fili yake
Duk Gwamnan da ya san bai taimaki talaka ba, bai yi aikin da ya kamata ba, to ya shafa wa kansa ruwa, zaben 2027 iya ruwa ne fidda kai, shima Shugaba Tinubu ta kansa yake a zaben 2027 mai zuwa, pressure ya masa yawa, ana ta kai karansa zuwa Amurka
Zaben jihar Osun babban sako ne da fadakarwa zuwa ga Gwamnonin jam'iyyar APC wadanda suke ganin zasu ci bulus, su sani karfin iko, tururuwan shiga jam'iyyar APC mai mulkin Kasa da yin taron dangi, ba zai basu mulki ba, su yi abinda zai gamsar da talakawa masu zabe kafin lokaci ya kure shine kadai mafitarsu
Muna rokon Allah Ya haramta wa maciya amana nasaran da suke nema a siyasar Nigeria
Daga Datti Assalafy
Ku cigaba da following TrendPost Hausa domin sanin halin da duniya ke ciki