Gaskiya Daya

Gaskiya Daya Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gaskiya Daya, Digital creator, sabon wuse Tafa LGA, Suleja.

GASKIYA DAYA TV UPDATESAPC ZA TA GUDANAR DA ZABEN FIDDA GWANI NA KAI TSAYE A JIHOHI 36 DA FCT ABUJA… Ta ce babu batun ts...
27/04/2026

GASKIYA DAYA TV UPDATES
APC ZA TA GUDANAR DA ZABEN FIDDA GWANI NA KAI TSAYE A JIHOHI 36 DA FCT ABUJA
… Ta ce babu batun tsayar da dan takara ta hanyar sulhu!
Shugabancin kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya sanar da Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da dukkan mambobin jam’iyyar cewa za a gudanar da zaben fidda gwani na kai tsaye a dukkan jihohi 36 na Najeriya da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja.
Haka kuma, an fitar da jadawalin zaben fidda gwani kamar haka:
ZABEN FIDDA GWANI NA SHUGABAN KASA:
Jumma’a 15 ga Mayu zuwa Asabar 16 ga Mayu, 2026
ZABEN FIDDA GWANI NA ‘YAN MAJALISAR WAKILAI:
Litinin 18 ga Mayu, 2026
ZABEN FIDDA GWANI NA SANATA:
Laraba 20 ga Mayu, 2026
ZABEN FIDDA GWANI NA MAJALISAR JIHA:
Alhamis 21 ga Mayu, 2026
ZABEN FIDDA GWANI NA GWAMNA:
Asabar 23 ga Mayu, 2026
Shugabancin jam’iyyar ya kuma bayyana karara cewa ba za a amince da tsarin tsayar da dan takara ta hanyar sulhu ba a wannan zabe na fidda gwani a duk fadin jihohi 36 da Abuja, tare da tabbatar wa duk masu neman takara cewa za a ba kowa dama iri daya.
SIYASA HARKA CE TA KASA (GRASSROOT).
Don haka, ana kira ga duk masu neman takara da su koma mazabunsu, su ci gaba da hulda da jama’a tare da karfafa goyon bayan kasa, su kuma tallafa wa jama’a ta fuskar kudi da sauran hanyoyi, domin samun nasara a zaben fidda gwani na APC.

20/04/2026

Visitation of jagaba to tafa local government apc party secretariat to declare his interest for contesting house of representative.
REPRESENTING TAFA SULEJA AND GURARA

‎GASKIYA DAYA TV NEWS REPORT‎Hon. Umar Isha Baba Jagaba Declares Interest for House of Representatives Seat, Tours Tafa ...
20/04/2026

‎GASKIYA DAYA TV NEWS REPORT
‎Hon. Umar Isha Baba Jagaba Declares Interest for House of Representatives Seat, Tours Tafa LG Wards.

‎Honourable Umar Isha Baba Jagaba has officially declared his intention to contest for the House of Representatives seat representing Suleja, Tafa, and Gurara Federal Constituency.

‎The declaration took place during his visit to the Tafa Local Government Party Secretariat, where he was warmly received by party executives, stakeholders, and supporters. In his address, Hon. Umar Isha Baba Jagaba expressed his commitment to serving the people with dedication, transparency, and effective representation.

‎Following the official declaration, the aspirant embarked on a strategic tour across the ten wards of Tafa Local Government Area to engage with grassroots supporters and seek their backing. The wards visited include:
‎Wuse East
‎Wuse West
‎Dogon Kurmi
‎Garam
‎Sabon Wuse
‎Ija Koro
‎Ija Gwari
‎Iku
‎Zuma East
‎Zuma West.

‎During the ward visits, Hon. Umar Isha Baba Jagaba met with community leaders, party members, and residents, where he outlined his vision for development, unity, and progress across the constituency. He emphasized the importance of inclusive leadership and pledged to prioritize the needs of the people if elected.

‎Party members and supporters in the various wards expressed their confidence in his leadership qualities and assured him of their full support in the forthcoming elections.

‎GASKIYA DAYA TV reports that the declaration and subsequent ward consultations mark a significant step in Hon. Umar Isha Baba Jagaba’s political journey, as he continues to build momentum towards securing the party ticket and representing the constituency at the national level.

‎Reporting by GASKIYA DAYA TV.

‎GASKIYA DAYA TV 🎤 LABARAI‎AHMAD IBRAHIM “PRESIDO” YA NEMI ALBARKA A GIDAN SARKIN IJA GWARI , YA SAMU GOYON BAYA A IJA G...
11/04/2026

‎GASKIYA DAYA TV 🎤 LABARAI
‎AHMAD IBRAHIM “PRESIDO” YA NEMI ALBARKA A GIDAN SARKIN IJA GWARI , YA SAMU GOYON BAYA A IJA GWARI WARD

‎Ɗaya daga cikin masu neman takarar ɗan majalisar jiha mai wakiltar Tafa, Ahmad Ibrahim wanda aka fi sani da Presido, ya fara rangadin tuntuba da neman goyon baya gabanin zaɓe mai zuwa.

‎A wannan tafiya, ya kai ziyara garinsu na asali inda ya gana da shugaban ƙauye (Head of Village) domin neman albarka da addu’a kan kudirinsa na tsayawa takara. Shugaban ƙauyen ya yi masa fatan alheri tare da ƙarfafa masa gwiwa a tafiyarsa ta siyasa.

‎Bayan haka, Ahmad Ibrahim Presido ya ziyarci shugabannin jam’iyya na Ija gwari Ward, inda ya gana da ‘yan kwamitin zartarwa na ward ɗin. A yayin ganawar, shugabannin sun bayyana cikakken goyon bayansu tare da amincewa da shi a matsayin ɗan takarar da s**a fi so ya wakilce su a majalisar jiha.

‎Jama,a Sun yaba da ƙwarewarsa da kuma kudirinsa na kawo ci gaba ga al’umma, tare da tabbatar masa da cewa za su mara masa baya a dukkan matakan zaɓe.
‎Daga bisani, ya ci gaba da ziyartar ofishin jam’iyya na ƙaramar hukumar Tafa domin ci gaba da tuntuba da ƙarfafa alaƙa da shugabanni.

‎Wannan mataki na nuna yadda yake samun karɓuwa daga matakin tushe zuwa ƙaramar hukuma, yayin da siyasa ke ƙara ɗaukar zafi a yankin.

‎GASKIYA DAYA TV 🎤 — Muryar Gaskiya

GASKIYA DAYA TV 🎤 TA’AZIYYACikin alhini da jimami ne GASKIYA DAYA TV 🎤 ke mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar daya daga ci...
11/04/2026

GASKIYA DAYA TV 🎤 TA’AZIYYA
Cikin alhini da jimami ne GASKIYA DAYA TV 🎤 ke mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar daya daga cikin fitattun ‘yan siyasa a karamar hukumar mu, wanda rasuwarsa ta girgiza al’umma baki daya.
Marigayin ya kasance jajirtaccen jagora, mai kishin al’umma da sadaukar da kai wajen cigaban karamar hukumar mu. Ya bayar da gagarumar gudummawa wajen bunkasa siyasa da walwalar jama’a, tare da zama abin koyi ga matasa da manya.
Wannan babban rashi ne ba ga iyalansa kadai ba, har ma ga daukacin al’ummar karamar hukumar mu. Hakika mun yi rashin gwarzo kuma ginshiki a fagen siyasa.
Muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa.
Haka kuma muna addu’ar Allah Ya ba iyalansa, abokan arziki da daukacin al’umma hakurin jure wannan babban rashi.
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.
— GASKIYA DAYA TV 🎤

INNALILLAHI WAINNA'ILAHI ILAIHI RAJI'UN: Kakakin Majalissar Dokokin Jihar Kebbi, Hon. Usman Mohammed Ankwai ya rasu ciki...
06/04/2026

INNALILLAHI WAINNA'ILAHI ILAIHI RAJI'UN: Kakakin Majalissar Dokokin Jihar Kebbi, Hon. Usman Mohammed Ankwai ya rasu cikin daren nan.

05/04/2026
GASKIYA DAYA TV 🎤 NA GABATARWAZUMA EAST WARD TA YI TARIHI — TA GOYI BAYAN HON. ZULKIFILU SHUAIBUYau, 5 ga watan Afrilu, ...
05/04/2026

GASKIYA DAYA TV 🎤 NA GABATARWA
ZUMA EAST WARD TA YI TARIHI — TA GOYI BAYAN HON. ZULKIFILU SHUAIBU
Yau, 5 ga watan Afrilu, 2026, ya zama rana mai muhimmanci a tarihin siyasar Karamar Hukumar Tafa, inda al’ummar Zuma East Ward s**a hadu gaba daya s**a amince da Hon. Zulkifilu Shuaibu a matsayin zababben dan takararsu na Majalisar Dokokin Jihar Neja, mai wakiltar mazabar Tafa.
Yayin da ake wannan goyon baya, shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki sun bayyana cewa lokaci ya yi da ya kamata a bai wa Zuma East Ward dama ta gaskiya da adalci domin ta tsaya takara tare da wakiltar al’umma. Sun ce tsawon lokaci wannan yanki na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar zabe, amma ba a taba ba shi damar jagoranci ba.
Zuma East Ward na daga cikin ginshikan siyasa mafi karfi a Karamar Hukumar Tafa, inda a kullum take bayar da kuri’u masu yawa a lokutan zabe. Amincinsu, karfinsu da jajircewarsu ga jam’iyya da tsarin dimokuradiyya abu ne da ba za a iya watsi da shi ba.
Yayin da yake jawabi ga taron jama’a, Hon. Haruna Liberia, daya daga cikin manyan masu ruwa da tsaki a yankin, ya ce:
“Wannan goyon baya ba kawai sanarwar siyasa ba ce — kira ne na adalci, daidaito da kuma girmama gudunmawar da aka bayar.”
Sakon ya fito karara: Zuma East ta cika hakkinta. Zuma East ta cancanci wakilci.
Al’umma sun yi magana da murya guda.
GASKIYA DAYA TV ✊

🎤 GASKIYA DAYA TV — LABARAN DA ƊUMI-ƊUMIDa ɗumi-ɗumi: Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, na shirin ficewa daga PDP zuwa APCR...
04/04/2026

🎤 GASKIYA DAYA TV — LABARAN DA ƊUMI-ƊUMI
Da ɗumi-ɗumi: Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, na shirin ficewa daga PDP zuwa APC
Rahotanni da ke shigowa yanzu sun nuna cewa Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, na dab da sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Wannan mataki na zuwa ne a wani lokaci da ake ganin zai iya girgiza siyasar Najeriya baki ɗaya, musamman a yankin Arewa, inda ake sa ran zai haifar da sabbin lissafi da sauye-sauye a harkokin siyasa.
Ku ci gaba da kasancewa tare da GASKIYA DAYA TV domin samun cikakkun bayanai nan gaba.

Address

Sabon Wuse Tafa LGA
Suleja
5425

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gaskiya Daya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share