ATJ &CO

ATJ &CO RAHMATUL LIL ALAMEEN (SAW)

Matashin Jigawa Ya Bayyana: Ismail Muhammad Adam Ya Lashe Miliyan 10 A Gasar Fasaha Ta AfirkaWani matashi ɗan asalin jih...
20/09/2025

Matashin Jigawa Ya Bayyana: Ismail Muhammad Adam Ya Lashe Miliyan 10 A Gasar Fasaha Ta Afirka

Wani matashi ɗan asalin jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam, ya yi abin alfahari ga Arewa bayan ya zama na uku (2nd Runner-Up) a gasar fasaha mafi girma a Afirka – Digital for All Challenge.

Gasar, wacce Tech4Dev ta shirya tare da haɗin gwiwar Foreign, Commonwealth & Development Office (FCDO), NITDA da UK-International Development Tech Hub, ta tanadi wani dandali na gwada ƙwarewa a fannin fasaha da koyon yadda ake amfani da ita a aikace.

Ismail, wanda ya wakilci Yankin Arewa maso Yamma, ya fito kan gaba a rukuni na matasa (Youth Intermediate Category) wanda shi ne mafi girma a gasar.

A matsayin lada, Ismail Muhammad Adam ya samu ₦10,000,000 tare da takardar shaidar ƙwararren mai haɓaka manhajar kwamfuta (Certified Software Developer) – babban ci gaba a rayuwar aikinsa.

Abin da ya ƙara jan hankali shi ne Ismail shi kaɗai ne ɗan takara da jami’an gwamnatin Jigawa s**a raka zuwa gasar, alamar jajircewar gwamnatin jihar wajen bunƙasa ilimin fasaha da ƙarfafa matasa. Sabon Daraktan Hukumar ICT da Tattalin Arzikin Dijital ta jihar ya kasance tare da shi har zuwa ƙarshen gasar, yana bayar da muhimmin tallafi.

Taƙaitaccen Saƙo:
Matashin ɗan Jigawa ya kafa tarihi a gasar fasaha ta Afirka, ya lashe miliyan 10, kuma ya samu takardar shaidar ƙwarewa a fannin haɓaka manhajar kwamfuta.

DA ƊUMI ƊUMI: A karon farko Iran ta kaddamar da sabbin motoci 201 masu Amfani da Wutar lantarki na Zamani, a Birnin Tehr...
20/09/2025

DA ƊUMI ƊUMI: A karon farko Iran ta kaddamar da sabbin motoci 201 masu Amfani da Wutar lantarki na Zamani, a Birnin Tehran.

TIRKASHI: Tinubu Na Iya Fara Neman Bashin Kuɗi Daga Opay Da Moniepoint – Inji Dino MelayeTsohon Sanata Dino Melaye ya so...
09/09/2025

TIRKASHI: Tinubu Na Iya Fara Neman Bashin Kuɗi Daga Opay Da Moniepoint – Inji Dino Melaye

Tsohon Sanata Dino Melaye ya soki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, inda ya ce tana iya kaiwa ga neman rance daga kamfanoni irin su Opay da Moniepoint saboda yawan rance da take nema.

Melaye ya bayyana hakan ne a hirar da aka yi da shi a tashar ARISE Television a ranar Litinin, inda ya ce duk da makudan kudaden rance da gwamnati ta samu, ƙasar na fama da yunwa.

Ya tambayi dalilin da yasa gwamnati ke ci gaba da ciyo bashin kudade daga ƙasashen waje duk da cewa ana ikirarin ana samun ƙarin kuɗaɗen shiga.

Melaye ya kuma zargi gwamnatin Tinubu da yin sakaci, yana mai cewa shugabannin da s**a gabata ba su taɓa yin rance da yawa irin wannan ba. Ya ce maimakon rage kashe-kashe marasa amfani, gwamnati ta sayi ruwan shaƙatawa na shugaban ƙasa, wanda bai taɓa amfani da shi wajen kare ƙasar ba, sai dai ya ke zagayawa ƙasashen waje.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta yi gargadin cewa yawan rancen da gwamnati ke ci gaba da ɗauka zai iya kai bashin Najeriya sama da Naira tiriliyan 200 kafin ƙarshen shekarar 2025.

Mawloudin Nabiy Somalia 1500Raƙumi Dubu ɗaya da ɗari biyar (1500) aka tanada don ciyar da Muhammadawa a garin Somalia do...
04/09/2025

Mawloudin Nabiy Somalia 1500
Raƙumi Dubu ɗaya da ɗari biyar (1500) aka tanada don ciyar da Muhammadawa a garin Somalia domin taron Mawloudin Annabi Muhammad SAWW. Wannan ya yi dai-dai da kasancewar shekarar Manzon Allah SAWW 1500 da haihuwa a wannan duniya.

LABARI MAI DAƊI: Wani Babban Fàšťò ya gina katafaren Masallaci Ya Bawa Musulmai domin a dinga yin Sallah a garin Osogbo ...
04/09/2025

LABARI MAI DAƊI: Wani Babban Fàšťò ya gina katafaren Masallaci Ya Bawa Musulmai domin a dinga yin Sallah a garin Osogbo a Oja Oba,

Muna So Saƙon Nan ya isa Zuwa ga Al'ummar Musulmai domin Suyi Masa godiya Sannan Suyi Masa Addu'a allah Yasa ya karbi Kalmar Shahada Ku tura Zuwa group group

Babban Fàšťòn ya bayyana dalilin da yasa ya gina masallacin da cewa, "Duk lokacin da babana ya zalunci mahaifiyata idan ta masa laifi sa'ilin muna ƙanana haka baba zai kori majaifiyata a gida ba inda za'a bamu mafaka ko a taimaka mana sai masallaci.

Ni da mahaifiyata mun sha kwana a Masallaci, bayan rasuwar mahaifiyata sai Yan uwan mamana su daukeni su mayar dani wajensu, bayan dogon lokaci nayi karatu na sami kudi naga da cewar nazo na sakawa mutanen dake taimakawa mahaifiyata da wajen kwana.

Na tarar masallacin ya rushe ya lalace, sai na dauki nauyin na sabunta musu sabon gini na zamani. Allahu Akbar Allah ya karawa Annabi Daraja.

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Wakiliya 👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa Shugaban Mulkin Sojin NijarJanar Abdoulramane Tchiani ya tallafa wa jarumin Kannywood Malam Na Ta...
02/09/2025

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa

Shugaban Mulkin Sojin NijarJanar Abdoulramane Tchiani ya tallafa wa jarumin Kannywood Malam Na Tala'ala wanda ke kwance a gadon asibiti.

Jarumin wanda ya tabbatar da hakan a wani bidiyo da ya fitar, ya ce Shugaban Ƙasar ya ƙirashi a waya kuma ya tura masa da kuɗaden da ya ce adadinsu ba zai faɗu ba a yanzu.

Ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro ya mayar da martani ne kan zargin da tsohon gwamnan jihar Kaduna ...
01/09/2025

Ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro ya mayar da martani ne kan zargin da tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya yi cewa gwamnati na ta'azzara matsalolin tsaro maimakon ƙoƙarin kawo ƙarshen matsalar a ƙasar.

Ƙarin bayani - https://bbc.in/4lSVOiA

Da ya daga cikin matasan daliban Sheikh ABDULJABBAR  ya kalubalanci malaman da s**a hada kai lokacin Case ɗin Abduljabba...
01/09/2025

Da ya daga cikin matasan daliban Sheikh ABDULJABBAR ya kalubalanci malaman da s**a hada kai lokacin Case ɗin Abduljabbar amma yanzu sun kasa hada kai saboda Annabi.

Ya ce daman akan Abduljabbar ne kawai za su iya hada kai, Ba akan Allah da Manzon Allah ba.

Me Za ku ce?

Saura kaɗan a  kammala aikin Masallacin jumua na dariqar Qadiriyyah dake Abuja Nigeria da shugaban dariqar Qadiriyyah na...
27/08/2025

Saura kaɗan a kammala aikin Masallacin jumua na dariqar Qadiriyyah dake Abuja Nigeria da shugaban dariqar Qadiriyyah na Africa sheik Dr Qaribullahi ake ginawa.

Cikin yardar Allah nan gaba kadan zaa gabatar da bikin bude shi dan fara ibada cikin sa, muna adduar Allah ya saka masa da alkhair tare da duk wanda s**a taimaka masa.

15/08/2025

I got over 40 reactions on one of my posts last week! Thanks everyone for your support! 🎉

LABARI MAI DAƊI ZUWA AL'UMMAR MUSULMAI: Babban Malamin Musulunci A Duniya Dr. Zakir Naik Ya Yi Wa Musulmi Bushara Cewa M...
11/08/2025

LABARI MAI DAƊI ZUWA AL'UMMAR MUSULMAI: Babban Malamin Musulunci A Duniya Dr. Zakir Naik Ya Yi Wa Musulmi Bushara Cewa Musulunci Ya Kusa Mamaye Duniya.

Allah ya Ɗaukaka Addinin Muslunci da Musulmai, Ku nuna mana Farin Cikinku ta Hanyar yin Sharing Zuwa Group Group

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Wakiliya 👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Address

Yola Road Anguwan Dakatsalle
Takum

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ATJ &CO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share