
21/04/2025
GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 11
π»π»π»π»π»π»π»π»π»π»π»π»
Abdullahi dayyabu tamburawa
[email protected] 08069592193
nan take kura ta tashi ta turnuke sararin samaniya,
A can kuwa fadar gimbiya luzwatu koda ta sallami kowa ta shiga gida sai ta kasa zaune ta kasa tsaye domin ganin wannan abun take k**ar a mafarki,
Can kuma a karkashin zuciyar ta sai taji cewa lallai tana so ta kara ganin sa domin ji takeyi k**ar akwai wata alaka tsakanin su, nan take ta ayyana a ranta cewa lallai gobe da safe zata hada mahaya su tare da ita su fita neman sadauki SHARDAS a duk inda yake a fadin wannan gari,
Da sassafe kuwa gimbiya luzwatu ko karyawa bata bari tayi ba ta fito kai tsaye ta durfafi barga dawaki ta dare doki ta fita a sukwane dakaru dubu s**a take mata baya
Duk inda ta keta sai dai kaga mutane suna zubewa kasa suna kwasar gaisuwar ban girma
Ko kallon su batayi ita kawai hankalin ta yana kan kauyen su sadauki SHARDAS, aikuwa tafi dakika dari uku ce ta kaisu kauyen da sadauki SHARDAS ya ke,
Da zuwa kuwa ko burki batayi ba a ko Ina sai gidan wakilin ta a kauyen,
Cikin azama ya fito daga cikin gida ya zube gaban gimbiya ya ce ya shugaba ta na rantse da karagar mulkin ki ko kare ki ka aiko ba dan aike ba kinsani ni mai biyayya ne amma basai kinzo ba
Nan take tayi murmushi ta ce yake gulamu kayi sani cewa hakika lamarin da ya kawo ni garin nan babbane,
Kayi sani cewa a wannan unguwar taku akwai wani saurayi da yaje har fada ta ya kashemin dakaru dubu shi kadai a cikin abun da bai wuce dakika dari sittin ba,
Narantse da jinin baba na idan ba ka nemomin shi ba sai na tsige gashin gemun ka da daidai sannan nasa a tsiremin kai
Koda jin haka sai gulamu ya mike cikin rawar jiki da nufin shiga gari sai ta daka masa tsawa ta ce
Yakai gulamu shin kasan wazaje nema ne da katafi ban sanar dakai komai akan sa ba,
Sai ya dawo jikinsa na rawa yace ki gafarce ni ya shugaba ta.....