Jami'in sirri

Jami'in sirri Hausa Adventures books (Novelist.)

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 11πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»Abdullahi dayyabu tamburawa    jamiinsirri@gmail.com 08069592193  nan take kura ta...
21/04/2025

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 11

πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»
Abdullahi dayyabu tamburawa
[email protected] 08069592193

nan take kura ta tashi ta turnuke sararin samaniya,

A can kuwa fadar gimbiya luzwatu koda ta sallami kowa ta shiga gida sai ta kasa zaune ta kasa tsaye domin ganin wannan abun take k**ar a mafarki,

Can kuma a karkashin zuciyar ta sai taji cewa lallai tana so ta kara ganin sa domin ji takeyi k**ar akwai wata alaka tsakanin su, nan take ta ayyana a ranta cewa lallai gobe da safe zata hada mahaya su tare da ita su fita neman sadauki SHARDAS a duk inda yake a fadin wannan gari,
Da sassafe kuwa gimbiya luzwatu ko karyawa bata bari tayi ba ta fito kai tsaye ta durfafi barga dawaki ta dare doki ta fita a sukwane dakaru dubu s**a take mata baya

Duk inda ta keta sai dai kaga mutane suna zubewa kasa suna kwasar gaisuwar ban girma

Ko kallon su batayi ita kawai hankalin ta yana kan kauyen su sadauki SHARDAS, aikuwa tafi dakika dari uku ce ta kaisu kauyen da sadauki SHARDAS ya ke,

Da zuwa kuwa ko burki batayi ba a ko Ina sai gidan wakilin ta a kauyen,

Cikin azama ya fito daga cikin gida ya zube gaban gimbiya ya ce ya shugaba ta na rantse da karagar mulkin ki ko kare ki ka aiko ba dan aike ba kinsani ni mai biyayya ne amma basai kinzo ba
Nan take tayi murmushi ta ce yake gulamu kayi sani cewa hakika lamarin da ya kawo ni garin nan babbane,
Kayi sani cewa a wannan unguwar taku akwai wani saurayi da yaje har fada ta ya kashemin dakaru dubu shi kadai a cikin abun da bai wuce dakika dari sittin ba,
Narantse da jinin baba na idan ba ka nemomin shi ba sai na tsige gashin gemun ka da daidai sannan nasa a tsiremin kai
Koda jin haka sai gulamu ya mike cikin rawar jiki da nufin shiga gari sai ta daka masa tsawa ta ce
Yakai gulamu shin kasan wazaje nema ne da katafi ban sanar dakai komai akan sa ba,
Sai ya dawo jikinsa na rawa yace ki gafarce ni ya shugaba ta.....

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 10πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»  abdullahi dayyabu tamburawa          Lokacin da yayi taku uku kacal da nufin ya bar daji...
21/04/2025

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 10
πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»

abdullahi dayyabu tamburawa



Lokacin da yayi taku uku kacal da nufin ya bar dajin sai yaji wani irin huci yana dukan bayan sa nan take yayi wata irin muguwar juyawa da nufin ganin abun dake biye da shi
Lokacin da sadauki SHARDAS ya waigo da nufin ganin bala'in da ke bayan sa,

Sai yayi arba da shugan wadannan aljanun a gaban sa, cikin wata irin mummunar siffa,

Kafin sadauki SHARDAS yayi wani yunkuri tuni wannan aljanin ya damki wuyan sa yai sama da shi yana kokarin dannasa a baki,

Cikin tsananin karfin damtse da zafin nama ya dunkule hannun sa ya gabxa masa naushi a hakora, ba shiri ya sake shi ya fado kasa sa,
Nan take ya kunna kai daji yana kuruwa, aikuwa sadauki SHARDAS ya bi bayan sa da nufin ya kure masa gudu ya kashe sa, nan take s**a cikin daji suna wani irin gudu na mamaki,

Shi dai wannan aljanin bai ma san ya wannan gudun ba, sabo da bala'i da yake ji,

Shi kuma sadauki SHARDAS yana so ne ya yanko kansa domin ya kaiwa gimbiya luzwatu, aikuwa bisa mamaki sai sadauki SHARDAS ya ga wannan aljani ya tsaya cak ya juya da kallon sa ga sadauki SHARDAS da yake tunkaro sa, ba shiri shima sadauki SHARDAS ya ci burki yana tunanin Anya kuwa wannan aljanin bai shirya masa wani Abu ba kuwa,
Kafin ya kara wani tunani tuni wannan aljanin ya mika hannu ya jijjige wata bishiya da ke kusa da shi yayo kan sadauki SHARDAS da nufin ya yi masa bugun damin hatsi, amma da yake babu tsoro a zuciyar sa ko kadan sai shima ya tasowa aljanin da nufin su hadu a tsakiya,

suna haduwa wannan aljani ya kawo wa sadauki SHARDAS wani irin wawan duka da bishiyar da ya xaro, cikin bakin zafin nama SHARDAS ya goce tare da zare takobin sa,

Nanfa s**a ja da baya kowa yana kallon abokin gwabzawar sa kai kace kadan garu,
k**ar hadun baki sai sika yunkuro a lokaci daya s**a ruguntsime da azababben yakin da ya haddasawa jejen girgizar dole
Kuyi follow din wannan account..

GIMBIYA   RUDDA'U   EPISODE    111______________________________    Abdullahi dayyabu tamburawa    jamiinsirri@gmail.com...
18/12/2024

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 111
______________________________
Abdullahi dayyabu tamburawa
[email protected] 08069592193

sannan ta wani bangaren wasu suna murnar canja sarki shardas domin haraji yayi yawa, gashi Kuma ko Ina yankawa yakeyi Yana sayarwa, baruwan Sa da Nan kasuwa ce, ko makabarta, ko wajen bauta, shi kawai ya samu kudi,
Lokacin da gimbiya luzwatu tayi sati Akan karagar mulkin ta, bayan dare yayi sun tafi daki da gimbiya rudda'u, sai taga gimbiya rudda'u tana shirye shirye da Kuma gyare gyare, Kai da gani kasan Shirin tafiya ne, gimbiya luzwatu ta kalle ta cikin rashin fashimta sannan tace ya ke wannan jaruma shin ban fashimci Shirin ki ba, badai tafiya Zaki yi ba? Gimbiya rudda'u ta kalle ta fuskarta cike da fara'a sannan tace Daman ai alkawarin sati daya mukayi dake, Dan haka Babu fashi gobe zanyi harama domin akwai sauran aiki a gaba na, Amma ki sani da zarar na cika buri na Zan dawo wajen ki mu Kara sancewa tare na wani lokaci, Amma dai yanzu tabbas gobe da sassafe kafin kowa ya farka daga bacci mu munbar wannan nashiyar, gimbiya luzwatu ta dire kasa bisa guiwowin ta, tana Mai zubar da hawayen takaici sannan takalli gimbiya rudda'u tace lallai zanfi kowa jin Dadi idan burinki na mallakar duniya ya cika, Amma babban bakin ciki na ta yanda Zaki tafi ki barni tsawon wannan lokaci, gimbiya rudda'u ta bushe da Dari sannan tace lallai kin cika sokuwa Dan kawai Zan tafi k**e kuka, to kenan idan na mutu fa a wannan tafiyar? Da sauri gimbiya luzwatu ta mike sannan tace aikuwa tunda Kika kawo zancen mutuwa na rantse da girman rawanin Kaka na na sittin da shida sarki Arbas, wannan tafiyar da ni za ayi ta domin yanda Kika ceci rayuwata Nima yazama dole na taimaka wajen cikar burin ki, gimbiya rudda'u ta turbune fuska k**ar an Aiko mata da sakon mutuwa, sannan ta kalli luzwatu tace, shin kin rasa hankalin ki ne? Idan Kika bi ni waye zai kular Miki da kasar? Ki cire wannan zancen da ga ranki domin ma bazai yuwu ba........

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 10πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»  abdullahi dayyabu tamburawa          Lokacin da yayi taku uku kacal da nufin ya bar daji...
16/12/2024

GIMBIYA RUDDA'U EPISODE 10
πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»

abdullahi dayyabu tamburawa



Lokacin da yayi taku uku kacal da nufin ya bar dajin sai yaji wani irin huci yana dukan bayan sa nan take yayi wata irin muguwar juyawa da nufin ganin abun dake biye da shi
Lokacin da sadauki SHARDAS ya waigo da nufin ganin bala'in da ke bayan sa,

Sai yayi arba da shugan wadannan aljanun a gaban sa, cikin wata irin mummunar siffa,

Kafin sadauki SHARDAS yayi wani yunkuri tuni wannan aljanin ya damki wuyan sa yai sama da shi yana kokarin dannasa a baki,

Cikin tsananin karfin damtse da zafin nama ya dunkule hannun sa ya gabxa masa naushi a hakora, ba shiri ya sake shi ya fado kasa sa,
Nan take ya kunna kai daji yana kuruwa, aikuwa sadauki SHARDAS ya bi bayan sa da nufin ya kure masa gudu ya kashe sa, nan take s**a cikin daji suna wani irin gudu na mamaki,

Shi dai wannan aljanin bai ma san ya wannan gudun ba, sabo da bala'i da yake ji,

Shi kuma sadauki SHARDAS yana so ne ya yanko kansa domin ya kaiwa gimbiya luzwatu, aikuwa bisa mamaki sai sadauki SHARDAS ya ga wannan aljani ya tsaya cak ya juya da kallon sa ga sadauki SHARDAS da yake tunkaro sa, ba shiri shima sadauki SHARDAS ya ci burki yana tunanin Anya kuwa wannan aljanin bai shirya masa wani Abu ba kuwa,
Kafin ya kara wani tunani tuni wannan aljanin ya mika hannu ya jijjige wata bishiya da ke kusa da shi yayo kan sadauki SHARDAS da nufin ya yi masa bugun damin hatsi, amma da yake babu tsoro a zuciyar sa ko kadan sai shima ya tasowa aljanin da nufin su hadu a tsakiya,

suna haduwa wannan aljani ya kawo wa sadauki SHARDAS wani irin wawan duka da bishiyar da ya xaro, cikin bakin zafin nama SHARDAS ya goce tare da zare takobin sa,

Nanfa s**a ja da baya kowa yana kallon abokin gwabzawar sa kai kace kadan garu,
k**ar hadun baki sai sika yunkuro a lokaci daya s**a ruguntsime da azababben yakin da ya haddasawa jejen girgizar dole
Kuyi follow din wannan account Don Ci gaba da sauraren mu

GIMBIYA RUDDA'U episode 3Abdullahi dayyabu Tamburawa πŸ”»πŸ”»πŸ”»     tashiga bangaren ta  a fusace,  tana zuwa kuwa dakinta ko z...
16/12/2024

GIMBIYA RUDDA'U episode 3
Abdullahi dayyabu Tamburawa

πŸ”»πŸ”»πŸ”»
tashiga bangaren ta a fusace, tana zuwa kuwa dakinta ko zama batayi ba jawo madubin tsafin ta ta gogesa nan take sai ga hotan wani dankaramin aljani ya fito ya tsaya gaban ta ya rusuna yace ya shugaba ta gani gareki,
Nan take tai a jiyar zuciya tace yakai FUDDAR inaso zanje na yaki duniya domin nazama gagara badau, amma ina so kaimin wani aiki
Cikin girmamawa aljani FUDDAR yace angama ya shugabata,
Cikin ixxa da tak**a tace inaso ka tashi yanxu ka zagaya duniya kaf dinta kadawo nan da sa'a uku kasanar dani sarkin da yafi kowanne sarki mulki a duniyar nan, kasanar da ni kasar da tafi kowacce kasa girma, kasanar dani bokan da yafi kowa tsafi a duniya, kasanar da ni, sadaukin da yafi kowanne sadauki sadaukantaka a duniya, narantse da girman tsafin banana boka burradu sai na mulki duniya.
Cikin tsananin tsoro aljani FUDDAR yace ya shugaba ta angama, nantake yayi wata girgiza yazama hayaki cikin dakika daya ya bace bat, koda ganin haka sai gimbiya RUDDA'U ta kyalkyale da mahaukaciyar Dariya mai k**a da kukan bijimin sa, daga baya kuma ta murtuke fuska ta ce koda kuwa zan rasa raina gobe zan dira a masaratar da tafi kowacce masarauta a duniya kuma na murkushe su sannan na Kamo bokan da yafi kowanne hatsabibanci aduniya, sannan na Kamo jarumin da yafi kowa jarumta a duniya, narantse da darajar tsafi sai na hada masarautar da Ba a taba halittatta ba a duniya,
Kafin ta gama rufe baki sai ga aljani FUDDAR ya bayyana a gaban ta cikin razana da karaya ya ce ya shugaba ta na zagaya duniya kaf kuma naxo miki da labarin da zai tayar miki da hankali, kafin ya gama rufe baki tuni gimbiya ta daka masa wata irin tsawa mai k**a da saukar aradu sannan ta ce sanar da ni abun da na ai ke ka,
Cikin tsoro FUDDAR ya ce ki gafarce ni ya shugaba ta,
Yanxu kuwa zan sanar dake..
Domin samun cigaban labarin kuyi following din wannan page din zaku samu labarin dukka sa...

GIMBIYA RUDDA'U episode 2     Daga marubuciAbdullahi dayyabu tamburawa   (Jamiinsirri@gmail.com) πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»duk abun da...
16/12/2024

GIMBIYA RUDDA'U episode 2
Daga marubuci
Abdullahi dayyabu tamburawa
([email protected])

πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»πŸ”»
duk abun da aka koya mata, aikuwa kafin ya Ankara GIMBIYA RUDDA'U ta zama gawurtacciyar jaruma, domin kuwa tun tana yar shekara bakwai tana iya karyawa da maza goma kuma ta kaisu kasa cikin yan dakiku, lokacin kuwa da GIMBIYA ta cika shekara ashirin a duniya sai yazamana duk duniya babu mutumin da ya isa ya tunkareta da maganar ya ki, hatta babanta sai dai ya nuna mata karfin tsafi, koda sarki ya fashin ci hakan sai tsananin farin ciki ya k**asa matuka, inda har yaji cewa ya k**ata ya fara koya mata harkokin tsafi, aikuwa nan danan itama ta fara karantar tsafi har takai da ta fara gagarar kananan bokayen garin,
Wannan ce tasa sarki buraddu ya hadata da wata sihirtacciyar tsuntsuwa wacce zata dunga bata kariya da abun da yafi karfinta a aharkar tsafi,
Ita dai wannan tsuntsuwa Ana kiranta da suna uyum,
Shi kansa sarki gadarta yayi a wajen babansa,
Lokacin da GIMBIYA RUDDA'U ta kai matuka gaya a kan harkar tsafi sai taje tace da baban ta lallai tana so ya bata dama ta shiga duniya domin taga yanda duniya take, nan ta ke hankalin sarki kuwa yai matukar tashi domin kuwa gani yake tamkar ranar rabuwa da yarsa tazo'
Domin ya taba gani a madubin tsafin sa cewa GIMBIYA RUDDA'U zata yi wata tafiya wacce zata dade bata dawo ba, kuma duk ranar da ta dawo ranar ita ce xata zama sarki a wannan gari,
Abun da ya kasa ganewa shin yarsa ce zata kashe shi a gasar sarauta ko kuwa wani ne zai kashehi ya hau karagar mulkin kafin yarsa ta dawo, shin amsar da ya kasa samu, har ixuwa yanxu sarki buraddu ya kasa binkito wannan al'amari,
Wannan cema yasa ya hakura ya zubawa sarautar Allah ido.
Sabo da haka hankalin sa ya tashi da jin cewa zatayi wannan tafiya, nan take yashige gida yabarta nan a tsugune batare da yace mata uffan ba,
Kuyi follow Don samun cigaban sa

GIMBIYA RUDDA'U episode 1Abdullahi dayyabu tamburawa ......... Kimanin shekara dubu sittin da shida   kafin zuwan samuda...
16/12/2024

GIMBIYA RUDDA'U episode 1
Abdullahi dayyabu tamburawa .........

Kimanin shekara dubu sittin da shida kafin zuwan samudawa, anyi wata kasa a gabashin duniya da ake ce mata daulatul hayat,
Ita dai wannan kasa cike take da hatsabiban mutane, tare da mashahuran matsafa wanda duniya take ji da su a fagen tsafi,
Wannan gari na daulatul hayat birni ne wanda babu wanda ya isa ya mulkesa face ya zama cikakken jarumi mai karfin damtse, mai karfin sihiri da tsafi,
A ka idar wannan gari shekara goma ake canja sarki domin akawo wanda ya fi sa hatsabiban ci,
Yanda kuwa ake canjawar kuwa shi ne duk me sha'awar zama sarki zai fitone su gwabza yaki da sarki da yake kan mulki, Idan yayi nasara akansa to shi ne sarki, Idan kuma anyi nasara akansa to sai sarki ya ci gaba da mulki har tsawon wata shekara goma.
Yanzu haka wani hatsabibin bokane akan mulkin wannan kasa tsawon zango takwas kenan yana cin gasar darewa kan wannan kujera ta sarautar kasar daulatul hayat,
Wannan boka kuwa Ana kiransa da suna sarki burradu, sarki buraddu matsafi ne na gaske domin duk wani matsafi da ke nashiyar yana tsoran sa, haka ma sadauki ne mai dakawa maxa kashi a hannu, sau bakwai yana zuwa ya tarwatsa kashe shi kadai ya dawo,
Duk duniya duk inda aka ambaci sunansa take ake firgicewa sabo da tsananin zaluncin sa
Amma babban tashin hankalin sarki shi ne bashi da da namiji, sai dai ya mace guda daya tal Ana cewa da ita GIMBIYA RUDDA'U kuma yayi Binkice a halar tsafin sa antabbatar masa cewa har abada baxai taba kara haihuwa ba,
Wannan ce tasa sarki buraddu ya sha alwashin GIMBIYA RUDDA'U sai ta zama tamkar shi a fagen lalata sadaukantar sadaukai, da kuma binne tarihin hatsabibin bokaya,
Wannan ce tasa ya fara bata horan yaki a boye batare da kowa yasani ba,
Babban abun da yake matukar bashi mamaki shi ne cikin kankanin lokaci GIMBIYA RUDDA'U take daukar duk abun da ya koya mata..
Kuyi following dina

16/12/2024

Zan fara karanta muku littafi GIMBIYA RUDDA'U, kullum zaku samu episodes Goma Insha Allah
Kuyi follow din wannan account

BIRNIN MARIDAI  EPISODE 1   ♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️    Abdullahi dayyabu tamburawa     08069592193 Kimanin shekara dubu...
16/12/2024

BIRNIN MARIDAI EPISODE 1

♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️♨️
Abdullahi dayyabu tamburawa
08069592193

Kimanin shekara dubu ashirin baya kafin zuwan sarki fir'auna na kasar misira anyi wasu kasashe guda biyu daga cikin kasashen aljanu
Kasa ta farko ana ce mata GAIRUL DAUWAB kasa ta biyu ana ce mata DARUL MAJNUN,

Kasar GAIRUL DAUWAB kasance ta ifiritan aljanu,
Kasace wacce take karkashin mulkin wani hatsabibin ifiritu ana cewa da shi sarki husnul auwab
Su ifiritan aljanu ba a samun matsafa a cikin su saidai tsagwaron karfin damtse da Zafin nama da ayyukan al'ajabi k**ar su bacewa farat daya ko kuma gudu na fitar hankali, inda aljani zai iya zuwa acikin shekara uku ya dawo idan ka samu ifiritan aljanu to a awa uku zasuje su dawo, wannan ce tasa a duk kabilar jinsin aljanu babu k**ar ifiritan aljanu,
Sarki husnul auwab gagarumin sadauki ne na gaban kwatance Domin akaf nashiyar babu k**ar sa kuma adalin sarki ne mai matukar jin tausayin talakawan sa,
Sarki husnul auwab yana da ya mace guda daya ana ce mata gimbiya kausaratu, kausaratu ta taso da tsananin tsabagen tsagoron jarumta ta ban mamaki domin kowa ma gani yake saidai mahaifin ta yafita karfin gudu da naci amma ba zallar artabu ba,
Amma kuma inda matsalar take shi ne gimbiya kausaratu azzaluma ce ta gaban kwatance domin haka kawai idan zaluncin ta ya motsa sai ta bude fukafukan ta tayi wani bangaren na aljanu taje ta baje gari guda ta dawo,
Duk fadin kasar gairul dawab babu Wanda gimbiya kausaratu take dagawa kafa face kanin mahaifin ta waziri Rijusul awab, shima ba Dan Allah ta kyale sa ba,
Ta kyalesane domin sanin cewa aljani ba sa'an wuta ba ne, domin shi ne sarkin yakin kasar kuma mahaifin ta yana matukar daraja sa,
Tun Sarki husnul auwab da sarkin yaki Rijusul awab suna kanana s**a taso kansu a matukar hade kuma s**a taso da matukar jarumta ta ban al ajabi,
Kuyi following din wannan page din Dan samun cigaban wannan littafi

05/11/2024

Ni Abdullahi Dayyabu Tamburawa...
Da ga Yau na janye adawa ta ga tsohon kantoma.
Allah ka bamu ikon gane gaskiya da kanmu

Address

Tamburawa

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jami'in sirri posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share