Kitabu wassunnah

Kitabu wassunnah The purpose of this group is to enlightening people on Islam .

23/12/2024

_*🌒بسم الله الرحمن الرحيم🌒*
_*Darasinmu na yau, hadisin da ke da ala'ka da mumini 27 cikin 30.*_
°
°
_*Manzon Allaah (ﷺ.} ya ce; {WANDA YA YI 'KORAFI MARA GASKIYA AKAN MUMINI, ALLAAH ZAI ZAUNAR DA SHI A MUGUNYAR 'YAN WUTA, HAR SAI YA FITA DAGA LAIFIN.}*_
°
°
```[Sahihul Jami'i;6196]```
==
==
_Allaah Ya sa mu dace. Allaahu a'alam._
~~
~~
```Zaku samemu a shafukanmu na Facebook da whatapp ta adireshin da ke 'kasa👇```
"" ""
"" ""
https://www.facebook.com/sakonninmanzonallah/?referrer=whatsapp
==
==
https://whatsapp.com/channel/0029Vas7BYA4yltUazb8Ni0J
***
***

Mun bude wannan shafin ne domin saka (Hadisai) Sakonnin Manzon Allah SallalLaahu alayhi wa sallam.

23/12/2024

He phoned me a few days later telling me that his wife is having a hard time accepting it but that she is willing to meet me.

I was nervous the day of the meeting. I prayed a lot the day before and asked Allah to help me. When I met her, she was a person, a woman like me. A woman who loves her husband and fears losing him.

She took my hand and with tears

21/12/2024

NASIHA;
Manzon Allah (صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَآلِهِ وَسَلَّمَ), ya ce: IDAN ƊAYANKU YA GA MAFARKIN DA YA SO GANI, TO (ALBISHIR NE) DAGA ALLAH, SAI YA YI MA ALLAH GODIYA A KAI, KUMA YA (NA IYA) BA DA LABARINSA. [Sahīhul Bukhãri; 6584]

16/12/2024

Masha Allah

15/12/2024

_*🌒بسم الله الرحمن الرحيم🌒*
_*Darasinmu na yau, hadisin da ke da ala'ka da mumini 19 cikin 30.*_
°
°
_*Manzon Allaah (ﷺ.} ya ce; {DAGA CIKIN AL'UMMANA AKWAI JAMA'AN DA AKE BASU LADA IRIN LADAN MUTANEN FARKO, DON SUNA TSAWATARWA AKAN ABIN 'KI.}*_
°
°
```[Sahihul Jami'i;2224]```
==
==
_Allaah Ya sa mu dace. Allaahu a'alam._
~~
~~
```Zaku samemu a shafukanmu na Facebook da whatapp ta adireshin da ke 'kasa👇```
"" ""
"" ""
https://www.facebook.com/sakonninmanzonallah/?referrer=whatsapp
==
==
https://whatsapp.com/channel/0029Vas7BYA4yltUazb8Ni0J
***
***

Mun bude wannan shafin ne domin saka (Hadisai) Sakonnin Manzon Allah SallalLaahu alayhi wa sallam.

03/12/2024

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Kamaluddeen Umar, Usman Hamza, Ammy Muhd

25/08/2024

FADAR SUBHANALLAH YANA CIKA MA'AUNIN LADA

Daga cikin aiyka masu saurin kai mutum aljanna bayan imani da Allah babu kamar AMBATON ALLAH,wani sahabi ya tambayi Manzon Allah SAW ya fada masa abi mafi sauki da zai riƙe ya kai shi aljanna a cikin sauki, sai Manzon Allah SAW yace:
(Kada harshen ka ya gushe face yana ɗanye a cikin ambaton Allah)

Daga ambaton Allah babu kamar kalmomi guda hudu sun fi kowanne zikiri falala, sune:
* Subhanallah
* Walhamdulillah
* Laa ilaha iallah
* Allahu akbar

Fadar Alhamdulillahi da subhanallah suna sanyawa mizanin ladar ka ya cika, Manzon Allah SAW yana cewa:
*(Fadar alhamdulillahi yana cika mizani, fadar subhanallah walhamdulillah yana cika mizani guda biyu, ko ya cika tsakanin sama da kasa)*
@رواه مسلم

Mai zai hana mutum ba zai ribaci wannan falala ba ya yawaita gadar waɗan nan kalmomi sau 100 ko sau 10 ko sau 1 ne ma a wajan zamansa.

Ambaton da harshe yana cikin mafi sauki aiki mai yawa lada, babu wanda zai kasa ambaton Allah sai mafi kasawar mutane.

اللهم أَعِنّا على ذِكرك وشُكرك وحُسن عِبادتك.

Mustapha Musa Abu Aisha

22/08/2024

An article on ma********on written by Dr zainab check in comment section 👇👇👇👇👇

22/08/2024

Daga Abu Hurauirah Allah ya yarda da shi, ya ce, "Annabi tsira da amincin Allah sun tabbata a gareshi ya ce." "Alamar munafiki (musulmi mai boye kafirci a zuciyarsa) uku ne; kuma ko da yana Sallah, yana azumi, yana da'war shí musulmi ne, (Alamun sun ne).
ldan ya yi magana ya fadí karya: kuma idan ya yi alkawari ya saba; kuma idan aka ba shi amana ya yi yaudara." Bukari da Muslim sun rawaito shi.

02/08/2024

WANI DARASI AKAN KYAUTATAWA ALLAH ZATO

“Mahaifina (Imamul Sa’adiy, Allah ya ji ƙansa) yana saman masallaci yana gyara ɗaya daga cikin bututu (inda ruwa ke kwarara), kawai sai wani mutum mai wucewa yace masa, 'Gafarta Mallam, me ya sa kake wannan aikin?'

Sai mahaifina yace masa: "Ai gobe za mu fita Sallar Roƙon Ruwa ne."

- In ji Nūratu, ɗiyar Shaikh Abdurrahmān bn Nāsirus Sa'adiy, a shafinta na Twitter.

____

Allahu Akbar.

Malamai bayin Allah kenan. Ka ga Shaikh Abdurrahman Nasirus Sa’adiy kawai yana da yaƙinin Allah Yana karɓan addu'a ne. Kuma tunda dai ya san sun shirya fita Sallar Roƙon Ruwa gobe, to yana kyautata zaton Allah zai sauko da ruwan sama goben bayan sun roƙe Shi. Don haka yake shiryawa ruwan saman.

Allahu Akbar.

Cikin Hadithul Qudsiy, Allah Maɗaukakin Sarki yace:

‎أَنَا عِنْدَ ظَنِّ عَبْدِي بِي...

"Ina nan duk yadda bawana yake zato…”

Malamai masu sharhi s**a ce ma’anar wannan maganar ta Allah shine: Idan kana yiwa Allah zaton saukar maka da alheri, to hakan. Idan kuma kana maSa zaton saɓanin haka, to nan ma hakan! Don haka ya rage naka; kai ka san me kake ƙudurcewa gameda Ubangijinka.

Imamul Qurtubiy (Abul-Abbas kenan), cikin sharhinsa na Saheehu Muslim, mai suna “Al-Mufhimu limā Ashkala min Talkhīṣi Kitābi Muslimi” da ya zo sharhin hadisin nan sai yace:

“Ma’anar hadisin shine kayi zaton idan kayi addu'a, to Allah zai amsa. Kayi zaton idan ka tuba, to Allah zai karɓi tubanka. Kayi zaton idan kayi istighfari, to Allah zai gafarta maka. Kayi zaton idan kayi wata ibada bisa sharuɗɗanta, to Allah zai baka lada...."

Don haka ana son musulmi ya ringa kyautatawa Allah zato a cikin komai, cewa Allah zai iya mishi abu kaza. Kada ka munanawa Allah zato, kana cewa addu’ar dai muna yi ne kawai, amma da Allah zai amsa ai da tuntuni ya amsa. Ayya! Shi yasa har yanzu kuwa kuka ji shiru. Ai baku da yaƙinin Allah zai karɓa ne, shi Ya sa ya barku da rashin yaƙininku. Tunda kuna ganin Allah ba zai muku ba, to ku je a hakan- ba za a muku ba.

Amma ida

15/07/2024

Azumi ashura gobe

04/07/2024

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Arike Ade, Zaharadden Abdullahi, Aisha Muhammad

04/07/2024

_In The Name Of Allah The Beneficent The Merciful_

☆ *AL-QUR'ĀN ~ 10/19* ☆

```The Messenger of Allah ﷺ said,```

*_"Al-Qur'ān will beseech Allah in the Day of Judgement (in favour of its reciter); to be beautifully honoured and be given honourable dresses."_*
💎

[Sahih At-Tirmidhi: 2915]

https://www.facebook.com/The-Ultimate-Role-Model-445490502650777/

Our Prophet Muhammad...Our Proper Role Model

24/06/2024

Prof. Mansur Sokoto, mni
16th October,2014

AL-GHADIR: KALUBALE GA ‘YAN SHI’A
INGANTACCEN LABARIN GHADIR:
Ma’anar Ghadir:
Kalmar Ghadir a larabce, tana nufin wurin da ya tara ruwa da ciyawa.
“Ghadir Khum” sunan wani tafki ne da yake a yankin Juhfa, kilomita 15 daga Rabigh. Nisan sa daga Makka kilomita 160 ne.
Labarin Ghadir:
Annabi Sallallahu Alaihi wa Sallam ya aiki Khalid dan Walid a matsayin kwamandan rundunar da za ta yi yaki a kasar Yaman daf da fara aikin Hajjin shekara ta 10H, hajjin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da kansa ya jagoranta.
Bayan da rundunar musulmi ta ci nasara sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya aika Sayyidi Ali don ya kula da sha’anin Ganimar da aka samu.
Ali Radhiyallahu Anhu ya raba Ganima, kuma ya cire hakkin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam na Khumusi kamar yadda Alkur’ani ya zayyana. Daga ciki kuma ya cire ma kansa wata kuyanga da ta ba shi shawa.
Sayyidi Ali bai bata lokaci ba ya zarce zuwa Makka don ya riski maigidansa Sallallahu Alaihi wa Sallam a wurin aikin Hajji. Ya kuma wakilta wani daga cikin sojoji akan sauran aikin da ya rage.
Domin ya dadada ran sojojin, wakilin Sayyidi Ali ya raba ma su tufafi kyawawa daga cikin abin da aka ganimanto. Ya kuma yi ma su izini kowa ya hau rakumin da yake so daga cikin kayan Ganima. Kafin haka, sojoji sun gabatar da bukatar haka ga Sayyidi Ali amma bai amince ba. Sai ya ce ma su, rabonku sai an je Madina.
Sojojin wannan runduna sun hadu da Sayyidi Ali tare da Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam a kan hanyar su ta dawowa bayan gama aikin Hajji. Sayyidi Ali ya nuna rashin jin dadinsa a kan wannan rabo da aka yi kafin lokacin yinsa. Nan take ya yi umurni duk su sauka daga rakuman, s**a kuma mayar da tufafin da aka raba masu. Rayukansu sun baci matuka a kan haka kuma sun kai karar sa ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam suna zargin sa da cewa ya kuntata masu.
Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya iso Ghadir Khum, kuma ya lura da fushi a fuskar wadan

14/06/2024

Get ready and set alarm for Sahoor of tomorrow's fasting. The Prophet (ﷺ) said there's blessing in taking Sahoor.

11/06/2024

Wa Ya Fara Haramta Azumin Nafila a Ranar Asabat?

Wasu cikin Manazarta s**a ce: ba su san wanda ya fara haramta Azumin Nafila a ranar Asabat ba kafin Shaikh Muhammad Nasiruddeen al-Albaniy. Shi Shaikh Albaniy ya dogara ne a kan Hadisin Abdullahi bn Busr (ra), daga ‘yar’uwarsa al-Samma’u (ra). Alhali Hadisi ne da manyan Malaman Hadisi s**a illata shi.
- Imamu Zuhriy yana s**arsa.
- Imamu Malik ya ce: Hadisin karya ne.
- Yahya al-Qattan yana kaffa-kaffa da shi.
- Abu Dawud ya ce: an soke Hadisi (Mansukhi).
- Imamu Nasa’iy ya ce: Hadisi ne birkitacce.
- Ibnu Taimiyya ya ce: Hadisi ne “Shazzi”.
- Haka Ibnul Qayyim ma ya fada.
- Ibnu Hajar ma ya ce: Hadisi ne birkitacce.

To ka ga idan aka dauki maganar Malaman da s**a raunana Hadisin, to dole a jefar da shi. In kuma aka lura da maganar wadanda s**a kyautata Isnadinsa, to Hadisi ne “Shazzi”, ya saba wa Hadisai Mutawatirai.

Almajirin Imam Ahmad, Abubakar al-Athram ya ambaci Hadisin sai ya ce:
"فجاء هذا الحديث بما خالف الأحاديث كلها".
ناسخ الحديث ومنسوخه للأثرم (ص: 201)

“Sai wannan Hadisin ya zo da abin da ya saba wa dukkan Hadisai”.

Sai kuma ya ambaci Hadisan da ya saba musu, daga ciki:
Hadisin Azumin watan al-Muharram gaba dayansa. Alhali akwai ranakun Asabat fiye da daya a cikin watan.
Haka Hadisin Azumtar watan Sha’aban.
Hadisin Sittu Shawwal.
Hadisin Ashura.
Hadisin Arafah.
Hadisin Azumi na tsakiyan kowane wata.
Duka wadannan Azumi dole ana samu suna dacewa da ranar Asabat.

A takaice, Haramta Azumin Nafila a ranar Asabat ya saba wa Ijma’i, kamar yadda Shaikhul Islam ya ce:
"إن ظاهر الحديث خلاف الإجماع".
شرح العمدة لابن تيمية - كتاب الصيام (2/ 653)

Saboda haka asali ra’ayoyi biyu ake da shi a mas’alar; ra’ayin Jumhur na karhanta ware ranar Asabat da yin Azumin Nafila, da kuma ra’ayin su Imamu Malik da Ibnu Taimiyya na halasci a sake ba kaidi. Alhali a ka’ida; idan aka yi sabani zuwa ra’ayoyi biyu a kan mas’ala, to bai kamata daga baya a kirkiri ra’ayi na uku ba.

Saboda haka kar ka yarda wani ya hana ka yin Azumi

Address

Bauchi To Jos Road
Tilden Fulani

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kitabu wassunnah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kitabu wassunnah:

Share

Category