Tijjaniyya youth social media

Tijjaniyya youth social media With remembrance of Allah our hearts 💕 feel calm ❤️

Amirul Mumineen!❤️🥰
14/06/2025

Amirul Mumineen!
❤️🥰

Alhamdllh 'Yan Izala sun amsa kiran da Sheikh Tahir Usman Bauchi yayi na cewa don Allah mu daina kafurta juna haka, mu k...
31/05/2025

Alhamdllh 'Yan Izala sun amsa kiran da Sheikh Tahir Usman Bauchi yayi na cewa don Allah mu daina kafurta juna haka, mu koma bin sallar juna, abin ya isa haka, kuzo mu hadu a kalmar data haɗa mu sauran duka siyasar addini ne kowa ya sani don haka kowa ya rike fahimta sa manyan ginshikan musulunci sun haɗa mu, abubuwan da s**a raba mu kananane , kada mu bari al'ummar manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam taci gaba da zama a wargaje.

Allah ya ƙara hada kan musulmi.

108 shine Adadin Haruffan Salatil fatih, kuma shine Adadin Sunan Allah (AL-HAQQU), Salatil fatih Al'amari ne daga Allah....
17/05/2025

108 shine Adadin Haruffan Salatil fatih, kuma shine Adadin Sunan Allah (AL-HAQQU), Salatil fatih Al'amari ne daga Allah. Adadin Kalmomin shi 24 ne wanda yai Daidai da Adadin Haruffan La'ilahaillallhu Muhammadurrasulullah (24) kuma yayi daidai da adadin haruffan fatiha.

Salatil Fatih yana da martabobi uku, martabar zahiri da ta Baɗini da ta Baɗinul baɗini. Kuma yana ɗauke da tajallin Halarorin Allah guda biyar.

Salatil Fatih Mabuɗi ne na shiga Halarar Allah da Manzon Allah SAW, Mai Karatun shi Zai rabbanta da Asrarai da Haqa'iqu da yawa, Salatil fatih Kofar Ma'arifar zatin Allah ne.
Sharif Umar Haidara.

21/04/2025

Da bawa yasan wane ne Arrahmanu idan yaga musifa dariya zaiyi, domin Abin da zai biyo baya mai dadi ne.

~Shehu Ibrahim inyass

15/04/2025

Sau nawa kasan ka taɓa kiran kungiyoyin Musulmi da ba naka ba mushrikai? Shin Annabi ne yace kayi haka ko IBN taimiyya?

Tunda da Tarbiyya ake amfani wajan samar da 'yan haƙiƙa domin bata ɗarika Ni a tawa Fahimtar ma, ya kamata a sanya Ka'id...
14/04/2025

Tunda da Tarbiyya ake amfani wajan samar da 'yan haƙiƙa domin bata ɗarika Ni a tawa Fahimtar ma, ya kamata a sanya Ka'idar cewa ba''a bada Tarbiyya sai ga wadda ya kai Shekaru arbain...(40)

Da haka zaa dakile matsalolin dake cikin Darika a Yanzu...

Mace kuma sai ta kai Shekaru Sittin (60) to lallai za'a samu gyara.

Amma wallahi Matsalolin sunyi yawa.

Daga Kabiru AdamuSpecial

Ziyarar Malam Ibrahim Mai Ashafa Zuwa Raudhar Alqadhi iyad Marubucin Littafin Ashshifa R.A
11/04/2025

Ziyarar Malam Ibrahim Mai Ashafa Zuwa Raudhar Alqadhi iyad Marubucin Littafin Ashshifa R.A

Kai yanzu ka kalli wannan yaron da malamin nasa wai kace sune masu yin asalin ɗarika ba su maulana Sheikh Sherif saleh M...
10/04/2025

Kai yanzu ka kalli wannan yaron da malamin nasa wai kace sune masu yin asalin ɗarika ba su maulana Sheikh Sherif saleh Maiduguri dasu maulana Sheikh Tahir Usman Bauchi ba ai kasan an ajiye Gaskiya an tafi siyasar addini , shi wancan da IZALA s**a kira malami da ake kira dan anti haka IZALA s**ai ta yayaɗa cewa yace azo ayi muƙabala da yan Ɗarika wai muna guduwa, s**ance ma tsoron sa muke ji , alhalin duk wani malamin ɗarika kallon mahaukaci mai dauke da wahabiyanci cikin ɗarika yake kallon sa, da s**a zuga shi, ya fito yana faɗa da kansa nan nake Sheikh Aminu Under 17 ya amsa yakuma yi wasan kura' dashi saboda dama ba ilimin ne dashi ba, ƴan siyasa tafi sallah dake dama ba ilimin gare su ba, sune suke daukar sa malami, sai gashi yana cewa Duk abubuwan da suke yi ba Sheikh Ibrahim inyass ne yace su yi ba , sune s**a zabi hakan bayan da aka titsiye shi cewa sai ya nuna wajan ya kuma kasa jama'a ga muƙabalar ku kalla zai fi kyau ku sauke ta awa hudu ce.

👇👇👇👇👇
https://www.facebook.com/rasulunameenun/videos/551418864269996/?app=fbl

Hoto guda biyu masu dauke da darusa.Hoton farko Sayyadi Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi ke tura mahaifinsa a keke saboda gi...
10/04/2025

Hoto guda biyu masu dauke da darusa.

Hoton farko Sayyadi Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi ke tura mahaifinsa a keke saboda girman jiki..

Hoto na biyu Malam Mukhtar dan Sayyadi Ibrahim ke tura nashi mahaifin a keke..

Allah baya saba alkawari mutukar Ka kyautata ga iyayenka sai yayanka sun kyautata maka, Allah bamu ikon kyautawa iyayenmu 🙏

Naga wani malami yana cewa muna rokon wanin Allah. Wannan maganar kawai siyasar addini ne. Mu ba mu taɓa cewa a roki wan...
09/04/2025

Naga wani malami yana cewa muna rokon wanin Allah. Wannan maganar kawai siyasar addini ne. Mu ba mu taɓa cewa a roki wani da ba Allah ba; illa iyaka dai mun yarda ayyukan mu ba su kai mu roki Allah mu kaɗai ba tare da mun yi kamin kafa da amintaccen saba, wato Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam). Shi yasa zaka ji muna cewa: "Ya Allah, kabiya mana buƙatun mu albarkacin Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam)."

Sannan mun ga wata magana da wasu ke yadawa a ƙoƙarin su na fassara wannan aya: "Iyyaka na’budu wa iyyaka nasta’in," sai suke yi wa Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) rashin ɗa’a, suna cewa ko taimakon sa ne ba sa bukata. Ya kamata masu irin wannan su sani cewa za su iya rasa imanin su ba tare da sun sani ba. Domin kuwa ba ya halatta ka yi wa Manzon Allah rashin ɗa’a da sunan tabbatar da tauhidi. Saboda ai shi ɗin da kace ko nashi ɗin ne ba ka bukata, shine wanda Allah ya aiko da ita wannan ayar. Bayan ya zo maka da Islam, kuma ya yi gwagwarmaya domin tabbatar da addinin da shi da abokaninsa, har da wasu baffaninsa da sauran Sahabbai, sai da s**a taimake ka, s**a sadaukar da rayukan su, kafin ita wannan aya ta iso zuwa gare ka.

Ba mu taɓa jin inda ake irin wannan karatun ba na rashin ɗa’a ga Annabi, sai a arewacin Najeriya. Allah ya kyauta.

1. Tawassuli da neman albarka ta wurin Manzon Allah (SAW)

“Ya Allah, kabiya mana buƙatun mu albarkacin Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam).” irin Wannan ana kiransa Tawassuli ne a ilimin addinin musulunci bawai wanin Allah ake roƙa ba,, kuma yana da asali daga Alƙur’ani da Hadisi.

Alƙur’ani – Surah Al-Mā'idah 5:35

Arabic:
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اتَّقُوا اللَّهَ وَابْتَغُوا إِلَيْهِ الْوَسِيلَةَ وَجَاهِدُوا فِي سَبِيلِهِ لَعَلَّكُمْ تُفْلِحُونَ

“Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku ji tsoron Allah, ku nemi hanyar kusanci zuwa gare Shi, ku yi jihadi a tafarkinSa, domin ku rabauta.”

Sharhi:
Wasīlah a nan tana nufin hanyar kusanci ga Allah, kamar yadda malaman tafsiri s**a ce itace ayyukan alheri, addu'a da kuma ta wurin wasu bayi nagari irin su Annabi (SAW).

Alƙur’ani – Surah An-Nisā’ 4:64

Arabic:
وَلَوْ أَنَّهُمْ إِذْ ظَّلَمُوا أَنْفُسَهُمْ جَاؤُوكَ فَاسْتَغْفَرُوا اللَّهَ وَاسْتَغْفَرَ لَهُمُ الرَّسُولُ لَوَجَدُوا اللَّهَ تَوَّابًا رَحِيمًا

“Da idan s**a yi wa kansu laifi, sun zo wurinka (Ya Muhammad), s**a nemi gafarar Allah, kai kuma ka roƙa musu, da sun sami Allah Mai karɓar tuba, Mai jin ƙai.”

Sharhi:
Wannan hujja ce cewa zuwa wurin Annabi (SAW) don roƙon gafara wajan Allah yana daga cikin hanyoyin samun rahamar ALLAH cikin sauki.

2. Girmamawa da biyayya ga Manzon Allah (SAW)

Alƙur’ani – Surah Al-Ḥujurāt 49:1-2

يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا تُقَدِّمُوا بَيْنَ يَدَيِ اللَّهِ وَرَسُولِهِ ۖ وَاتَّقُوا اللَّهَ ۚ إِنَّ اللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٌ
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا تَرْفَعُوا أَصْوَاتَكُمْ فَوْقَ صَوْتِ النَّبِيِّ

“Ya ku waɗanda kuka yi imani! Kada ku yi rashin ɗa'a ko azarɓaɓi a gaban Allah da ManzonSa, ku ji tsoron Allah. Lalle Allah Mai jin magana ne, Masani.”
“Ya ku waɗanda kuka yi imani! Kada ku ɗaga muryarku a bisa muryar Annabi…” rashin ɗa'a

Wannan aya tana tabbatar da cewa ladabi da biyayya ga Annabi (SAW) wajibi ne, kuma yana daga cikin alamun imanin mutum.

Hadisi Sahih al-Bukhari (Hadisi 15, littafin Imani)

لَا يُؤْمِنُ أَحَدُكُمْ حَتَّى أَكُونَ أَحَبَّ إِلَيْهِ مِنْ وَالِدِهِ وَوَلَدِهِ وَالنَّاسِ أَجْمَعِينَ

“Babu wanda zai cika da imani har sai na fi soyuwa a gare shi fiye da mahaifinsa, ɗansa da dukkan mutane.”

3. Hadarin raina matsayin Annabi da sunan Tauhidi

Alƙur’ani – Surah At-Tawbah 9:65-66

وَلَئِن سَأَلْتَهُمْ لَيَقُولُنَّ إِنَّمَا كُنَّا نَخُوضُ وَنَلْعَبُ ۚ قُلْ أَبِاللَّهِ وَآيَاتِهِ وَرَسُولِهِ كُنتُمْ تَسْتَهْزِئُونَ
لَا تَعْتَذِرُوا قَدْ كَفَرْتُم بَعْدَ إِيمَانِكُمْ

“Idan ka tambaye su, sai su ce: ‘Ai muna wasa da raha ne.’ Ka ce: ‘Shin da Allah, da ayoyinSa, da ManzonSa kuke yin izgili?’ Kada ku ba da uzuri! Lalle kun kafirta bayan imanin ku.”

Wannan aya tana nuni da cewa raina Manzon Allah (SAW) da sunan wasa ko wani tsari yana iya sa mutum ya fita daga imani.

4. Matsayin Annabi matsayin rahama be ga dukkan duniya

Alƙur’ani – Surah Al-Anbiyā’ 21:107

Arabic:
وَمَا أَرْسَلْنَاكَ إِلَّا رَحْمَةً لِّلْعَالَمِينَ

Fassarar Hausa:
“Ba mu aiko ka ba (Ya Muhammad), sai dai rahama ga dukan talikai.”

5. Shafa’ah Taimakon Annabi (SAW) a Lahira

Hadisi Tirmidhi (3613), Sahihul Jami’:

فَيَأْتُونَ إِلَىٰ مُحَمَّدٍ، فَيَقُولُ: أَنَا لَهَا، أَنَا لَهَا

“Sai mutane su je wurin Muhammad (SAW), sai ya ce: ‘Ni ne wanda zai iya yin ta, ni ne wanda zai yi ta (shafa’ah).’”

Tawassuli ta hanyar Annabi (SAW) ba haramun ba ne matuƙar an yi shi da sanin cewa Allah ne kaɗai Mai iko da amsa.

Girmamawa da biyayya ga Annabi (SAW) wajibi ne, kuma rashin yin hakan yana iya kai mutum ga barazanar rasa imani.

Annabi Muhammad (SAW) yana da matsayi na musamman wanda Allah da kansa ya girmama shi da shi.

Yakai ɗan uwa basai ka riƙa maimaita "Ko na Annabi ne baka buƙata ba" zaka tabbatar da Tauhidi domin kuwa furta irin wannan ka iya sakaka yin biyu babu.

Allah ya kare mu, Ya kare mana imanin mu albarkacin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam

09/04/2025

Innalillahi wa inna alaihi raji'un 🤔

Naga IZALA suna murna Atiku Abubakar yace wani ya daina rusuna masa domin girmamawa ya gaishe shine a tsaye, to ba tare ...
08/04/2025

Naga IZALA suna murna Atiku Abubakar yace wani ya daina rusuna masa domin girmamawa ya gaishe shine a tsaye, to ba tare da wani tawili ba kamar yadda baku yarda da tawili ba dama, ga saƙo zuwa gare ku:

عن معاوية بن أبي سفيان قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:

"من سرّه أن يتمثل له الناس قيامًا، فليتبوأ مقعده من النار."

“Duk wanda yake jin daɗin mutane su miƙe tsaye gare shi (don girmamawa), to ya tanadi matsuguninsa a wuta.”

1. Sunan Rawi: Mu'awiya ibn Abi Sufyan (RA)

2. Littafab da aka ruwaito shi:

Sunan Abu Dawud Hadisi no. 5229

Jami‘ at-Tirmidhi Hadisi no. 2755

Musnad Ahmad Musnad Mu’awiyah (RA), Hadisi no. 16896

Al-Albani malamin IZALA na Albania ya ce hadisin “Sahih” ne a cikin Silsilat al-Ahadeeth as-Saheehah (vol. 1, hadisi no. 357).

Ya IZALA sai ku daina gaisuwa a tsaye nan ma Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya hana.

Address

Yola

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tijjaniyya youth social media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share