Taskiya Reporters

Taskiya Reporters ingantattun labarai domin tunatarwa, fadakarwa da ilmantarwa

Allah Ya jiƙan tsohon shugaban kasar najeriya general Muhammadu Buhari da rahama.
14/07/2025

Allah Ya jiƙan tsohon shugaban kasar najeriya general Muhammadu Buhari da rahama.

INNAL'ILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!Allah Ya Yiwa Sarkin Sharifan Bauchi Sharif Alh. Nasir Muhammad Bello Wanda Ya Rasu...
30/06/2025

INNAL'ILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!

Allah Ya Yiwa Sarkin Sharifan Bauchi Sharif Alh. Nasir Muhammad Bello Wanda Ya Rasu A Yau Litinin 30th June 2025.

Za'a Gudanar Da Sallah Jana'iza Idan Allah Ya Kaimu Ranar Talata Da Karfe 10:00 na Safe A Fadan Mai Martaba Sarkin Bauchi

Muna Fatan Allah Ya kara Masa Kusanchi Da Kakan Sa Sallallahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam, Amiiiin Yaa ALLAH

Izala ta Kori Daya Daga Cikin Malaman ta Sheikh Nazir Abu Aisha Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Waikamatis Sunnah sun K...
29/06/2025

Izala ta Kori Daya Daga Cikin Malaman ta Sheikh Nazir Abu Aisha

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Waikamatis Sunnah sun Kore daya daga cikin jiga-jigan Malaman daga kungiyar su mai suna Sheikh Nazir Lawan Abu A'isha sakamakon Samun sa da wasu laifuka.

Ko ya kuke ganin wannan Koran?

YANZU-YANZU: Shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong-un, yayi tir da matakin Amurka akan Iran, tare da tura sakon gargadi ga ...
23/06/2025

YANZU-YANZU: Shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong-un, yayi tir da matakin Amurka akan Iran, tare da tura sakon gargadi ga Amurka akan dakatar da shiga yakin kai tsaye.

📸 — Abdul Journalist 1

INNAL'ILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN 😭 An yi wa Wasu Matafiya Ɗaurin Aure 12 Daga Zariya Kiisan Gilla, Wasu 11 na Kwance ...
22/06/2025

INNAL'ILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN 😭

An yi wa Wasu Matafiya Ɗaurin Aure 12 Daga Zariya Kiisan Gilla, Wasu 11 na Kwance Asibiti Bayan Wasu Mutane Sun Kai Musu Hari a Yankin Mangu Dake Jihar Filato.

Daga Cikin Waɗanda Aka Kashe Har da Mahaifin Ango da Ƙanin Ango. Dafatan Allah Yajiƙansu Yayi Musu Rahama.AMIIN🤲😭

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN!!!Mummunan hatsari ya faru a kan hanyar katsina zuwa Dutsinma, mutanen dake cikin m...
21/06/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN!!!

Mummunan hatsari ya faru a kan hanyar katsina zuwa Dutsinma, mutanen dake cikin motar duk sun ƙone, wanda yasan motar ga number din nan dan Allah ayi Sharing.

Allah ya jiƙansu da gafara. Ya sa sun huta mu kuma idan tamu tazo ka sanya mu cika da imani

21/06/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Allah ya yiwa Gwani Sharif Mash’hood dake Maradi a Jamhuriyar Niger rasuwa a jihar T...
16/06/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Allah ya yiwa Gwani Sharif Mash’hood dake Maradi a Jamhuriyar Niger rasuwa a jihar Taraba dake tarayyan Najeriya ranar Asabar 14/06/2025.

Gwani Mash'hood wanda Allah ya yiwa baiwar sanin Alkur'ani mai girma, kuma mai karantar da al'ummar musulmi.

Allah ubangiji madaukakin sarki ya jikan sa da rahma ya gafarta masa. AMIIN Ya Allahu.

Iyalai da Dangin Ƴan Tijjaniyya 12 Daga Kano da aka yi Garkuwa Dasu a Burkina Faso Sun Roƙi Tinubu da Ya kawo Musu Ɗauki...
14/06/2025

Iyalai da Dangin Ƴan Tijjaniyya 12 Daga Kano da aka yi Garkuwa Dasu a Burkina Faso Sun Roƙi Tinubu da Ya kawo Musu Ɗauki.

Iyalai da dangin wasu mabiya darikar Tijjaniyya guda 12 daga Jihar Kano, waɗanda ake zargin an yi garkuwa da su watanni tara da su ka gabata a ƙasar Burkina Faso, sun sake roƙon Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Abba Kabir Yusuf da su kawo musu ɗauki don ceto ƴan uwansu.

Iyalan waɗanda lamarin ya shafa sun kuma roƙi Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, da shugabannin darikar Tijjaniyya da su taimaka wajen kubutar da ‘yan uwansu.

Da ta ke magana da wakilin DAILY NIGERIAN a Kano, matar ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, wacce ta bayyana sunanta da Amina, ta bayyana cewa tun da mijinta ya ɓace, tana cikin damuwa da ƙuncin rayuwa.

Amina, wacce ba ta so ta yi doguwar magana saboda har yanzu tana cikin firgici da tashin hankali, ta ce tana da fatan mijinta zai dawo ba da jimawa ba.

A cewarta, ita ce tana da yara uku, kuma rayuwa ta yi tsanani tun bayan bacewar mijinta domin tana fama da wahala wajen ciyar da kanta da ‘ya’yanta.

Shi ma Bashir Tijjani, ɗa ga ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, ya ce i sun kasance cikin fargaba da rashin tabbas tun da lamarin ya faru.

Ya bayyana cewa duk da ƙoƙarin da s**a yi, ba su samu wani ci gaba mai amfani ba wajen ganin an sake su ko samun labarin inda suke.

Rahotanni sun bayayana cewa mutanen sun bar Zawiyyar Sheikh Malam Tijjani ‘Yan mota a ranar 7 ga Satumba, suna bi ta Jamhuriyar Nijar zuwa Burkina Faso a hanyarsu ta zuwa Senegal inda aka sace su.

Muna Roƙon Allah swt Yakuɓutar Dasu Cikin Aminci.AMIIN 😭😭🤲🤲

~ Daily Nigerian Hausa

Address

Tudun Wada

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskiya Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share