01/06/2026
Wike zai ƙaddamar da ayyuka tsawon kwana 31 a Abuja domin cika shekaru uku na mulkin Tinubu
Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa za a shafe kwanaki 31 ana kaddamar da manyan ayyukan raya kasa a Abuja domin bikin cikar shekaru uku na gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.
Wike ya bayyana hakan ne a wani taron siyasa da aka gudanar a Port Harcourt, jihar Rivers, inda ya ce nasarorin da aka samu a fannin ababen more rayuwa a Abuja sun samo asali ne daga goyon baya da hangen nesa na Shugaba Tinubu.
A cewarsa, ayyukan da za a kaddamar sun hada da manyan tituna, kayayyakin more rayuwa da kuma ayyukan sake fasalin birane. Ya jaddada cewa ba kananan ayyuka ba ne, yana mai kalubalantar duk wanda ke shakkar irin ci gaban da aka samu a Abuja.
Har ila yau, Wike ya sanar da cewa ya yafewa dukkan abokan adawarsa na siyasa, musamman a jihar Rivers, tare da yin kira gare su da su ajiye sabanin siyasa domin hadin kan jihar.
Ministan ya kuma gargadi masu kokarin tsoma baki a harkokin siyasar Rivers daga wasu jihohi, yana mai cewa sansaninsa na siyasa na nan daram kuma zai ci gaba da kasancewa mai karfi a jihar na shekaru masu zuwa.