Kanawa Post News

  • Home
  • Kanawa Post News

Kanawa Post News jaridar ta daya a arewa

Wike zai ƙaddamar da ayyuka tsawon kwana 31 a Abuja domin cika shekaru  uku na mulkin TinubuMinistan babban birnin taray...
01/06/2026

Wike zai ƙaddamar da ayyuka tsawon kwana 31 a Abuja domin cika shekaru uku na mulkin Tinubu

Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa za a shafe kwanaki 31 ana kaddamar da manyan ayyukan raya kasa a Abuja domin bikin cikar shekaru uku na gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.

Wike ya bayyana hakan ne a wani taron siyasa da aka gudanar a Port Harcourt, jihar Rivers, inda ya ce nasarorin da aka samu a fannin ababen more rayuwa a Abuja sun samo asali ne daga goyon baya da hangen nesa na Shugaba Tinubu.

A cewarsa, ayyukan da za a kaddamar sun hada da manyan tituna, kayayyakin more rayuwa da kuma ayyukan sake fasalin birane. Ya jaddada cewa ba kananan ayyuka ba ne, yana mai kalubalantar duk wanda ke shakkar irin ci gaban da aka samu a Abuja.

Har ila yau, Wike ya sanar da cewa ya yafewa dukkan abokan adawarsa na siyasa, musamman a jihar Rivers, tare da yin kira gare su da su ajiye sabanin siyasa domin hadin kan jihar.

Ministan ya kuma gargadi masu kokarin tsoma baki a harkokin siyasar Rivers daga wasu jihohi, yana mai cewa sansaninsa na siyasa na nan daram kuma zai ci gaba da kasancewa mai karfi a jihar na shekaru masu zuwa.

Bari Mugá Zaben 2027.
01/06/2026

Bari Mugá Zaben 2027.

Da ɗumi-ɗumi: Jaruma Radeeya Jibrin Ta bayyana tsananin yadda take son zaman aure ko don 'ya 'yan ta: Ta bayyana hakan n...
31/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: Jaruma Radeeya Jibrin Ta bayyana tsananin yadda take son zaman aure ko don 'ya 'yan ta: Ta bayyana hakan ne bayan an sake daura mata aure yau

A cikin wani sako da jarumar ta wallafa Ashafinta na Facebook tana mai cewa Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah

Allah kafi kowa sanin dalilina nason aure kuma nasan duk wata jarabawata akan aure kaine kake daura mun sannan kuma kaine kake kara kaddara mun yin aure a lokacin da kaso Allah nagode maka da wannan jarabawar taka a gareni.

Allah yinda nai tawassali dakai nayi imani dakai na yarda da wannan auren domin ka domin gobena domin yarana domin yan uwana domin mahaifina domin lahirata

Allah ubangiji ka bani ikon kare rayuwata a dakin mijina Allah ubangiji ina rokon ka Dan girman ka Dan tsarkinka Dan rahamar ka Dan darajar Fiyeyyen halinta manzo sallallahu alaihi wasallam

Allah ubangiji badon halina ba Allah yinda aka daura mun aure yau
Allah ubangiji kasa sai dai a fitar da gawata a dakin mijina

Bissalam

Super Eagles Ta Nijeriya Ta Ci Kofin Unity Bayan Ta Doke Kasar Jamaica Da Ci 3-0
31/05/2026

Super Eagles Ta Nijeriya Ta Ci Kofin Unity Bayan Ta Doke Kasar Jamaica Da Ci 3-0

YANZU-YANZU: Arsenal Ta Yi Asarar Kofin Zakarun Turai, Inda PSG Ta Ci Kofin
30/05/2026

YANZU-YANZU: Arsenal Ta Yi Asarar Kofin Zakarun Turai, Inda PSG Ta Ci Kofin

Nagodewa Allah Akan Arzikin Da Ya Yi Min Na Yawan 'Ya'ya, Kuma A Hakan Ma Babu Wasu A Cikinsu, Inji Jarumin Finafinan Ha...
30/05/2026

Nagodewa Allah Akan Arzikin Da Ya Yi Min Na Yawan 'Ya'ya, Kuma A Hakan Ma Babu Wasu A Cikinsu, Inji Jarumin Finafinan Hausa, Ali Rabi'u Ali (Daddy)

Masu Yi Min Sharrin Cewa Ciwona Na Ƙarya Ne, Wai Ina Shaye-Shaye Da Kuɗin Taimakon Da Ake Ba Ni, Na Bar Su Da Allah, Kum...
30/05/2026

Masu Yi Min Sharrin Cewa Ciwona Na Ƙarya Ne, Wai Ina Shaye-Shaye Da Kuɗin Taimakon Da Ake Ba Ni, Na Bar Su Da Allah, Kuma Duk Mai Shaƙƙun Ciwona Ya Zo Inda Nake Ya Ganewa Idonsa, Inji Jarumar Finafinan Hausa, Zee Diamond

Wani darasi ku dauka a labarin Jarumar Kannywood, Fati Karishima, ?Jarumar ta bayyana cewa kamfen ɗin shugaban ƙasa Tinu...
30/05/2026

Wani darasi ku dauka a labarin Jarumar Kannywood, Fati Karishima, ?

Jarumar ta bayyana cewa kamfen ɗin shugaban ƙasa Tinubu na 2023 shi ne abu mafi muni a rayuwata. Domin kuwa a shi ne ta haɗu da wani mutum wanda yanzu jami'i ne a gwamnatin ya aure ta ya kuma watsar da ita, k**ar yadda ya bayyana a cikin shirin Gabon Talk show.

A cewarta, tun bayan auren nasu, mijin bai taɓa zuwa inda take ba, haka kuma bai amince ta je inda yake ba, sai dai su yi bidiyo call. Amma kuma ya k**a mata gidan haya tare da tura mata kuɗin cefane lokaci bayan lokaci.

Karishima ta ce bayan wasu watanni da fara zaman auren, ta fara fama da wata matsalar rashin lafiya da ba a san kanta ba, inda ta ke zubar da jini daga jikinta tsawon watanni biyar. Ta bayyana cewa duk da gwaje-gwajen da aka yi mata a asibiti, likitoci ba su gano musabbabin matsalar ba. Baya da haka har dogon suma take.

Jarumar ta ƙara da cewa a daidai lokacin da take fama da wannan yanayi, mijin nata ya daina tuntuɓarta tare da katse duk wata kulawa da yake ba ta. Ta ce ya daina ɗaukar kiran wayarta tare da dakatar da tura mata kuɗaɗen cefane.

A cewarta, lamarin ya kai ga duk abin da take da shi sai da ya ƙare kuma kowa ya guje ta. Sannan kuma a lokacin da ta nemi ya sake ta, mutumin ya ce shi bai aure ta ba, kuma bai ma san ta ba.

"Daga ƙarshe, komai da nake da shi ya ƙare. Lokacin da na nemi ya sake ni, sai ya ce wai bai taɓa aure na ba ta ya zai saki abin da bai aura ba, kuma bai ma san ni ba kwata-kwata". In ji Fati.

Dan Takarar Gwamnan Gombe A Karkashin PDP, Sheik Pantami Da Dan Takarar Sanatan Gombe A Karkashin PDP, Sanata Dankwambo ...
29/05/2026

Dan Takarar Gwamnan Gombe A Karkashin PDP, Sheik Pantami Da Dan Takarar Sanatan Gombe A Karkashin PDP, Sanata Dankwambo A Yayin Sallar Juma'a A Yau

Address

Zoo Road

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kanawa Post News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kanawa Post News:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share