20/05/2026
TATTAUNAWA TA MUSAMMAN: “Lokaci Ya Yi da Matasan Najeriya Za Su Kwato Ƙasarsu” — Comrd. Yahaya M. Abdullahi, Shugaban Matasan AAC na Ƙasa
A wata tattaunawa ta musamman da jaridar Leadership Hausa ta yi da Shugaban Matasan Jam’iyyar African Action Congress (AAC) na ƙasa, Comrd. Yahaya M. Abdullahi, ya bayyana cewa lokaci ya yi da matasan Najeriya za su farka domin kwato makomar ƙasarsu ta hanyar shiga siyasa da kuma zaɓen shugabanni masu gaskiya da kishin talaka waɗanda ke da riƙon amana.
Kwamaret Yahaya ya ce jam’iyyar AAC ita ce jam’iyya ɗaya tilo mafi tsayawa kan gaskiya, adalci, da yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya, yana mai cewa dubban matasa daga sassa daban-daban na ƙasar nan na ci gaba da shiga jam’iyyar saboda sun gaji da tsohuwar siyasar yaudara da rashin adalci da tsoffin yan siyasar ƙasar s**a shafe tsawon shekaru suna gudanarwa, rayuwar talaka kullum yana cikin Ƙunci, tashin hankali, damuwa da sauransu kuma ba wanda ya isa ya fito yayi magana.
“Ina miƙa gaisuwa ta musamman ga dukkan matasan Najeriya da masu kishin ƙasa. Yau Najeriya na cikin mawuyacin hali saboda tsawon shekaru na gazawar shugabanci, rashin adalci, rashin aikin yi, da kuma danniyar talakawa. Amma muna da yakinin cewa matasa za su iya sauya wannan tarihi idan s**a haɗu s**a tsaya tsayin daka wajen kare ‘yancinsu, tare da faɗa da dukkan wani tsari na zalunci.”
Ya kara da cewa yayin ziyarce-ziyarcen da yake kaiwa jihohi daban-daban, ya gana da matasa, masu fafutuka, da shugabannin al’umma da dama da suke nuna sha’awar tsayawa takara a karkashin tutar jam'iyyar AAC.
“Abin farin ciki ne ganin yadda matasa ke ƙara fahimtar cewa siyasa ba mallakin attajirai ko masu mulki kadai ba ce. Najeriya tamu ce baki daya, kuma lokaci ya yi da matasa za su shiga gaba wajen ƙwato makomar ƙasarsu,” in ji shi.
Ya ce: “Ina kira ga duk wani matashi ko ɗan Najeriya mai kishin ƙasa da yake da burin kawo sauyi kada ya ji tsoro ko ya yi kasa a gwiwa. Ku zama dan gwagwarmayar kwato yancin Jama'a, ya shiga jam'iyyarmu ta AAC domin yaki da dukkan wani mummunan mulki a fadin Najeriya.
Comrd. Yahaya ya kuma bukaci matasan Najeriya su mara wa jagoran jam’iyyar AAC baya, wato Omoyele Sowore, yana mai cewa Sowore ya shafe shekaru yana gwagwarmayar kare hakkokin talakawa da yaki da zalunci ba tare da tsoro ba.
A cewarsa: “Matasan Najeriya dole su fahimci cewa idan suna son ‘yanci na gaskiya, shugabanci nagari, da kasar da za ta ba su dama, dole su fito su yi fada ta hanyar dimokuradiyya. Omoyele Sowore ya nuna jarumta da sadaukarwa wajen yaki da cin hanci, rashin adalci, da danniyar gwamnati. Lokaci ya yi da matasa za su hada kai su zabi shugabanni masu gaskiya maimakon waɗanda s**a jefa kasar nan cikin matsala.”
Ya kara da cewa AAC ba jam’iyyar siyasa ce ta anfani kawai ba, illa wata tafiya ce ta neman ‘yanci da adalci ga talakawan Najeriya.
“Sai mun haɗu tare ne za mu iya gina Najeriya mai adalci, inda matasa za su samu aiki, talaka zai samu kariya, kuma gwamnati za ta yi aiki domin jama’a ba domin masu karfi ba,” in ji shi.
Babban abunda ya fi tayar da hankalinmu a Arewacin Najeriya yanzu shine matsalar tsaro, wannan abu ne da ya addabi jama'ar Najeriya, musamman Arewacin Najeriya, a kwanakin baya Sowore yayi wata magana inda yake cewa a cikin mako biyu zai magance matsalar tsaro idan ya zama shugaban ƙasa, inda ya bayyana cewa masu kawo matsalar tsaro suna Abuja, su za'a magance idan aka magance su to an kammala da matsalar tsaro, amma matukar suna yawo to lallai matsalar zai ci gaba da hauhawa a fadin Najeriya.”
“Babban Burinmu a yau shine mu tabbatar da mun magance dukkan wani damuwa da zai addabi talaka a fadin Najeriya, abu na farko shine matsalar tsaro, Arewacin Najeriya da noma kawai zamu iya rike kanmu, Kasar 'Ukraine' bata wuce jihohi uku a fadin Najeriya ba amma abun kunya har lokacin da take yaƙi sai da ta bama Najeriya tallafin abinci wannan babbar abun kunya ne, a ƙasar da muke da komai na arziki tun daga filin noma har arzikin karkashin kasa duk Allah ya bamu amma saboda shugabannin Najeriya damuwarsu kawai su azurta kansu, kullum muna cikin fama da talauci.
Haka idan muka koma bangaren tattalin arzikin kasa, muna da masu Ilimin da zasu cire wa Najeriya kitse a cikin wuta, a kullum abunda Omoyele Sowore yake cewa shine zalunci ne ya dabaibaye Najeriya ba rashin abunda ya kamata ba, muna da wadanda zasu yi ayyuka a ƙasar nan tuƙuru domin ci gaban ƙasar, amma abun kunya har yanzu mafi ƙarancin albashi a Najeriya bai wuce dubu dari ba, wasu kasashen da ba'a aiki kamar Najeriya albashin ya zarce na Najeriya kusan kaso uku, kullum ma'aikata ke wahala a Najeriya.
Ya yi wa dukkan masu neman takara da magoya bayan jam’iyyar fatan alheri tare da jaddada cewa gwagwarmayar ceto Najeriya tana bukatar hadin kan matasa daga kowane bangare na kasa.