Abba aji TV

Abba aji TV This page is the reason why I created it, to create information, to educate, to enlighten and to ple

DA ƊUMI ƊUMI: Ɓata gari sun farmaki kantin Rufaida Yoghurt a Kano sun kwashe kaya. An zargi wasu masu Zanga-Zanga da shi...
01/08/2024

DA ƊUMI ƊUMI: Ɓata gari sun farmaki kantin Rufaida Yoghurt a Kano sun kwashe kaya.

An zargi wasu masu Zanga-Zanga da shiga cikin wani babban kanti na Rufaida Yoghurt Dake birnin Kano s**a kwashe maƙudan kuɗaɗe da komai daga cikin kanti...

“Mun ci gaba da samun rahoton daga majiyar mu kan haka daga wakilan mu cewa yadda wasu bata-gari s**a yi ta'annati a katin siyar da fura da nono na Rufaida da ke unguwar Hotoro a hanyar fita daga Kano.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sa hannu kan dokar albashi mafi ƙanƙanta (naira 70,000) ranar Litinin a Fadar gwamnatin...
30/07/2024

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sa hannu kan dokar albashi mafi ƙanƙanta (naira 70,000) ranar Litinin a Fadar gwamnatin ƙasar.

Wasu ƴan majalisar kamar Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya Sanata Godswill Akpabio da mataimakinsa Sanata Barau Jibrin sun halarci bikin sanya hannun.

Gwamnatin Najeriya ta ce ta karye farashin shinkafa da kusan kashi 50 wadda ta tanada da za a sayar a sassan kasar da nu...
30/07/2024

Gwamnatin Najeriya ta ce ta karye farashin shinkafa da kusan kashi 50 wadda ta tanada da za a sayar a sassan kasar da nufin samar da sauki ga ƴan kasa.

Me zaku ce ?

Kungiyoyin Fararen Hula Fiye Da Hamsin (50) Sun Janye Daga Shiga Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa A Jihar Neja Kungiyar ‘Conce...
29/07/2024

Kungiyoyin Fararen Hula Fiye Da Hamsin (50) Sun Janye Daga Shiga Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa A Jihar Neja

Kungiyar ‘Concerned Nigerlites Forum’ da kungiyoyin farar hula bayan wani taron gaggawa na kwamitin zartarwa na jiha, da shugabannin shiyyar, da daukacin shugabannin kananan hukumomi 25 da shugabannin manyan kungiyoyin farar hula na jihar sun nesanta dandalinsu da kungiyoyinsu daga shirin da aka tsara na “Nation wide”. Zanga-zangar". Tag: "Karshen Mulki mara kyau.

An cimma matsayar ne saboda nasarar da aka samu tare da masu ruwa da tsaki da sauran muhimman batutuwa kamar haka.

1. Taron masu ruwa da tsaki da gwamnatin jihar Neja ta shirya wanda dandalinmu da wasu kungiyoyi s**a halarta, Amirs, shugabannin al'umma, Limamai, Fastoci, Matasa, Dalibai da kungiyoyin mata inda al'amuran jihar da abin da gwamnati ke yi don magance matsalar. kawar da wahalhalun da talakawa ke ciki aka tattauna. Taron ya bai wa mahalarta taron damar tattaunawa da gwamnati kan batutuwan da s**a shafi kasa musamman, yunwa, tsadar rayuwa, gaskiya a bangaren gwamnati da sauran batutuwan da s**a shafi ‘yan Nijar.

Alkawarin da Gwamnan ya nuna na sakin kimanin tan dubu 50 na hatsi sun hada da shinkafa, gero, dawa da wake da za a sayar da su a kan rangwamen kashi 50% a fadin kananan hukumomi 25 na jihar Neja. Sakin karin takin Metrics 20 ga manoma da bayar da kyautar #20,000 ga kowane ma'aikatan jahohi da na kananan hukumomi a jihar, ba za a iya wuce gona da iri ba. Hakazalika, damar da ma’aikatan jihar ke da su na siyan buhu daya na kowane kayan masarufi a kan bashi, ta nuna tawali’u. Ƙuduri na ƙarshe na taron da duk masu ruwa da tsaki na kada su shiga zanga-zangar da aka shirya na ɗaya daga cikin dalilin wannan aikin. Wannan matsayi shine yabawa shuwagabannin mu musamman na Amir da malaman addini da s**a halarci taron tunane-tunane............h

‘Yan Nijeriya suna da ’Yancin Su Fito Su Yi Źanga-Źangar Ĺumana, Ďomin Su Ñunawa Ģwamnati Ba Su Ji Ďadin Abinda Ake Ýi B...
29/07/2024

‘Yan Nijeriya suna da ’Yancin Su Fito Su Yi Źanga-Źangar Ĺumana, Ďomin Su Ñunawa Ģwamnati Ba Su Ji Ďadin Abinda Ake Ýi Ba Domin A Ģyara, Saboda Dokar kasa Ta Ba Su dama,

Amma A Yi Taka-Tsantan Kada A Jefa Kasa Cikin Matsala, Inji Gwamna Dikko Radda Na Katsina

Me za ku ce?

TIRKASHI: An Cire Sarautar Sarkin Sarmari Saboda Zāngå-zāngå A Jihar Neja.Daga El-hajji awwerl minna. Hakimin Bosso dake...
29/07/2024

TIRKASHI: An Cire Sarautar Sarkin Sarmari Saboda Zāngå-zāngå A Jihar Neja.

Daga El-hajji awwerl minna.

Hakimin Bosso dake Jihar Neja Alhaji Mu'azu Laka ya cirewa Abdullahi Isah ( Biodun) sarautar sarkin samarin Bosso saboda ya nuna ra'ayin goyon bayan zanga zanga ta lumana

Da yake Magana da Limamin Tsalle Daya, Hakimin yace ba zasu lamunci duk wani nau'in da ka'iya haifar da rashin zaman lafiya ba.

JIHAR NEJA SUN FITO: Yanzu haka Matasa ƴan kishin ƙasa daga cikin garin Minna babban birnin jihar Niger State sun fito z...
29/07/2024

JIHAR NEJA SUN FITO: Yanzu haka Matasa ƴan kishin ƙasa daga cikin garin Minna babban birnin jihar Niger State sun fito zanga zanga ta lumana

ABIN MAMAKI: Wadanda S**a Jagoranci Yi Wa Gwamnatin Jonathan Zanga-Zànģa A 2012, Yanzu Kuma Sune Suke Kokarin Hana A Yi ...
25/07/2024

ABIN MAMAKI: Wadanda S**a Jagoranci Yi Wa Gwamnatin Jonathan Zanga-Zànģa A 2012, Yanzu Kuma Sune Suke Kokarin Hana A Yi Źanga-Źanga, Inji Atiku Abubakar

Me za ku ce?

DA ƊUMI ƊUMI: An Fitar Da Jadawalin Yadda Zanga-zanga Zai Kasance A Birnin Zariya.Ana sanar da al'ummar dake waɗannan  y...
25/07/2024

DA ƊUMI ƊUMI: An Fitar Da Jadawalin Yadda Zanga-zanga Zai Kasance A Birnin Zariya.

Ana sanar da al'ummar dake waɗannan yankunan na birnin Zariya Jihar Kaduna dasu kasance bisa wannan tsari kamar yadda ake gani.

(1)- Tsarin fitowarmu Zanga zanga" karfe 6:00Am na safe.

(2)- Alummar yankin Kofar Doka Ku rufe Titin Jos 60:00am na safe.

(3)- Alummar dake Dan Magaji Ku rufe hanyar zuwa Kano. 6:00am na safe.

(4)- Alummar dake Sabon Gari da Dogarawa Ku rufe hanyar Zuwa Sokoto 60:00am na safe.

(5)- Alummar dake Kofar Kuyanbana da Gwargwaje Ku rufe Hanyar Zuwa Kaduna 6:00 am na safe.

Daga nan zamuje gidan Mai Martaba Sarkin Zazzau da sauransu.

DOKA! DOKA!! DOKA!!!

(1)- Babu mākāmî. ⚠️
(2)- Babu taba kayan kowa ⚠️
(3)- Babu fada ku cin zarafin wani. ⚠️
(4)- kowa ya fito da rubutu na kokensa a jikin kwali ✅
(5)- idan da hali kowa yayi shigar farar riga da bakin wando, ko kuma duk shigar da kaga dama amma shiga mai ma'ana. ✅

TAIMAKO! TAIMAKO!! TAIMAKO!!!

(1)- masu halin cikinmu su dafo abinci. ✅
(2)- wasu su taimako da ruwan sha da kuma magani. ✅
(3)- mu taimaki duk wanda yake bukatar taimako ko wannne iri" uwa daya uba daya. ✅

Bamu daukewa kowa ba" daga kan Dan shekara 18 zuwa sama" matasa maza da mata" Dattijai da tsofaffi" kowa ya fito domin ceto kasar mu daga halin da shugabanni s**a jefata na tsananin yinwa da tsaradar rayuwa da kuma rashin tsaro.

ABINDA AKE BUƘATA GWAMNATI TA YI SHINE

(1)- A bude bodojin Arewa baki daya domin ashigo da abinci kamar yadda yake a baya da kuma kaiyade masa farashi.

(2)- A dawo da tallafin man Fetir ya dawo 200 duk lita.

(3)- Duk yan kunan dake fama da rashin tsaro a Arewa a dawo da zaman lafiyar yankin domin cigaba da noma da kiyo.

(4)- A dawo da tallafin karatu domin Dan Talaka ya yaki Jahilci.

(5)- A samarwa matasa maza da mata aiyukan dogaro dakai domin gujewar aikata munanan laifuka.

(6)- A dawo da tallafin wutar lantarki, domin karfafar masana'antu manya da kanana

Lokacin fitowa karfe 60:00Am na safe zuwa 6:00Pm n

Ba Za Mu Zuba Ido Mu Bar Masu Shirin Tada  Zaune Tsaye A Ƙasar Nan Da Sunan Źanga-Źanga Ba, Cewar Hafsan Sojin NijeriyaM...
25/07/2024

Ba Za Mu Zuba Ido Mu Bar Masu Shirin Tada Zaune Tsaye A Ƙasar Nan Da Sunan Źanga-Źanga Ba, Cewar Hafsan Sojin Nijeriya

Me za ku ce?

Ganduje Ya Roki ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Watsi Da Batun Zanga-Źangar Da S**a Shirya Gudanarwa Tare Da Baiwa Gwamnatin Shug...
25/07/2024

Ganduje Ya Roki ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Watsi Da Batun Zanga-Źangar Da S**a Shirya Gudanarwa Tare Da Baiwa Gwamnatin Shugaba Tinubu Goyon Baya Domin Samun Nasarori

Mutum uku sun mutu sakamakon rushewar gini a legas Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas ta tabbatar da mutuwar...
25/07/2024

Mutum uku sun mutu sakamakon rushewar gini a legas

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas ta tabbatar da mutuwar mutum uku a lokacin da wani gini ya rufta a rukunin gidajen Arowojobe da ke yankin Maryland a jihar.

Da yake tabbatar wa kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN, rushewar ginin, Babban sakataren hukumar, Dakta Olufemi Oke-Osanyintolu ya ce lamarin ya faru ne da tsakar daren ranar Alhamis.

Ya ce mutane ukun da s**a mutu a lokacin faruwar lamarin duka ma'aikatan gini ne.

“Bayan samun labarin faruwar lamarin, jami'an hukumarmu sun gazaya wurin tare da gaggauta fara aikin ceto, inda s**a zaƙulo gawarwakin mutum uku duka maza, da wasu mazan biyu da aka zaƙulo da ransu sai kuma wani mutum guda da ya maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan ginin da shi ma aka ceto shi'', in ji shi.

Ya kuma ƙara da cewa tuni aka garzaya da mutanen da aka ceto zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci.

Tuni aka kai manyan motocin tono domin faɗaɗa aikin ceton.

Rushewar gini wata matsala ce da ake yawan samu Najeriya. Ko a farkon wannan wata ma, an samu ruftawar ginin wata makaranta a jihar Filato da ke tsakiyar ƙasar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar yara fiye da 20, tare da raunata gommai.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abba aji TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abba aji TV:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share