Dillaliya

Dillaliya Dillaliya Jarida ce da aka samar dan cigaban harshen Hausa da kuma samar da sahihan labarai cikin s

Nigerian author says Israel could have been defeated by Iran in prolonged war (Video)
05/08/2025

Nigerian author says Israel could have been defeated by Iran in prolonged war (Video)

International Nigerian author says Israel could have been defeated by Iran in prolonged war (Video) By Salim Sani - August 5, 2025 0 99 FacebookTwitterPinterestWhatsApp Nigerian author says Israel could have been defeated by Iran in prolonged war (Video) The Nigerian author of a new book about the I...

04/08/2025

Publisher of Neptune Prime has blazed the trail!

Dr. Hassan Gimba, anipr, publisher and CEO of Neptune Prime newspaper has bought the digital copy of the book THE 12-DAY WAR on selar platform and turned it to a printed hard copy.

THE 12-DAY WAR by Abraham Moses. It’s not just a story—it’s a deep dive into the Israel-Iran conflict that shook the globe. You’ll uncover the secrets, the power plays, and the ancient rivalries that nearly changed history forever.

If you love real stories, expert analysis, and want to understand what the news missed, this book is for you. Don’t just watch history—understand it.

Grab your copy of THE 12-DAY WAR now also @ Amazon platform! Trust me, you won’t see the world the same way again.

You can now watch the full interview on the book The 12-DAY WAR below:
04/08/2025

You can now watch the full interview on the book The 12-DAY WAR below:

Nigerian author of the newly released book about the Israeli war on Iran, The 12-Day War, and Editor-in-Chief of Nigeria’s Almizan newspaper, Ibrahim Musa, said that had the Iran-Israel conflict endured for at least a month, the Zionist regime would have collapsed.

Nigerian Author Asserts Iran Could Have Defeated Israel in Prolonged Conflict
04/08/2025

Nigerian Author Asserts Iran Could Have Defeated Israel in Prolonged Conflict

Nigerian author of the newly released book about the Israeli war on Iran, The 12-Day War, and Editor-in-Chief of Nigeria’s Almizan newspaper, Ibrahim Musa, said that had the Iran-Israel conflict endured for at least a month, the Zionist regime would have collapsed.

An rantsar da sabbin Shugabannin Cibiyar ciniki, masana'antu, ma'adanai da aikin gona ta jihar Kano.Daga Ibrahim Muhamma...
31/07/2025

An rantsar da sabbin Shugabannin Cibiyar ciniki, masana'antu, ma'adanai da aikin gona ta jihar Kano.

Daga Ibrahim Muhammad

An rantsar da sabbin zababbun shugabannin Cibiyar cinikii, masana'antu, ma'adinai da aikin gona na jihar Kano da aka fi sani da "KACCIMA" a dakin taro na harabar filin baje koli na Aminu Dantata da ke kan titin gidan Zoo ranar Alhamis da taron ya sami halartar mutane da dama, ciki har da Kwamishinan ciniki na jihar Kano, Hon. Wada Sagagi.

Da yake jawabi bayan rantsar da su, sabon zaɓaɓɓen shugaban cibiyar ciniki da masana'antun, ma'adinai da aikin gona na jihar Kano, Ambasada Usman Hassan Darma ya bayyana cewa zaben da aka yi masa ba tare da hamayya ba, ya nuna hadin kai da fahimtar juna da nasara a tsakanin su.

Ya yi nuni da cewa wannan nasara ba tasu bace su kadai, domin alamar amincewar mambobin cibiyar ce gare shi da sabuwar tafiya da za a yi ta inganta harkokin ciniki da masana'antu a jihar Kano.da Arewa da ma kasa baki daya.

Ambasada Usman Hassan Darma ya gode wa kwamitin da s**a gudanar da zaben bisa yin zabe cikin gaskiya da adalci. Ya jinjina wa tsofaffin mambobin kwamitin gudanarwa a kan jajicewa da rikon amana da kuma godewa tsoffin shugabanin cibiyar akan irin kyawawan tubali da s**a aza da suke shirin cigaba da bunkasa shi.

Ya ce su ma ma'aikatan sakatariyar cibiyar tun daga Darakta Janar har zuwa masu gadi suna daga cikin ginshikai dake rike da cibiyar ya tabbatar da cikakken goyon bayan hadin kai daga wannan sabon shugabancin.

Ya gode wa Gwamnatin jihar Kano bisa goyon baya da take basu tare da cewa za su bude kofa don hadin gwuiwa tsakanin hukumomi da yan kasuwa don bunƙasa tattalin arzikin Kano da kara jawo saka hannun jari cikin al'umma.

Ya tabbatar wa daraktocin cibiyar za su cigaba da jagorantar cibiyar tare da yin aiki tare domin tsara sabuwar cibiyar mai cike da hadin kai ta kirkiro ingantattun manufofi.

Shugaban cibiyar ta ciniki, masana'antu, ma'adinai da aikin gona, Ambasada Usman Hassan Darma ya ce dukkan mambobin cibiyar wannan shugabanci nasu ne za su farfaɗo da ayyuka da karfafa hadin kai da mayar da cibiyar matsayin da ya dace da ita a kasa baki daya .

Shi ma a nasa jawabin tsohon shugaban riko na cibiyar, Alhaji Garba Imam ya bayyana irin matsaloli da s**a zo s**a sami cibiyar a ciki da irin matakai da s**a dauka na kawo gyara da sama mata kudin shiga da irin ayyuka da s**a gudanar da a yanzu haka suna da dimbin kudade da kadarori tare da yin alkawarin cigaba da bai wa sabon zubin sabbin shugabannin cibiyar goyon baya domin kai ga nasara.

Cikin shugabannin kungiyar da aka rantsar sun hada da Alhaji Abdulrahman Sabitu Muhammad a matsayin mataimakin shugaba na Daya. Alhaji Umar Haruna Isma'il mataimakin shugaba na Biyu. Nura Habib mataimakin shugaba na kasuwanci. Hajiya Samira Abubakar mataimakiyar shugaba mai kula da hulda da jama'a. Aliyu Mustapha mataimakin shugaba mai kula da kadarori da sauran muk**ai na matakai daban-daban.

25/07/2025

🔥 *HOT NEW BOOK – THE 12-DAY WAR!* 🔥

For 12 intense days, the world stood at the edge. Want the real story behind the Israel-Iran conflict? This book is loaded with suspense, secrets, and shocking truths they never show in the news!

Get your digital copy now for just N2000!
Pay with Opay or Moniepoint: 8037023343 (Ibrahim Musa).
After payment, send your proof to Ibrahim Musa on WhatsApp (08037023343) and receive your copy instantly.

Ready for a book that’ll blow your mind? 📚

Book overview of  The 12-Day War, now on AmazonFor twelve tense days, the world stared into the abyss as Israel and Iran...
24/07/2025

Book overview of The 12-Day War, now on Amazon

For twelve tense days, the world stared into the abyss as Israel and Iran clashed—threatening to ignite a conflict that could engulf the globe. *The 12-Day War* takes you inside the heart of this crisis, drawing on front-line reporting, expert analysis, and harrowing firsthand accounts. Discover how decades of rivalry, failed diplomacy, and prophetic expectations collided, bringing superpowers to the brink and everyday lives to a standstill.

Go behind the scenes with leaders like Netanyahu and Khamenei, witness hidden motives and surprise attacks, and explore the ancient beliefs that shaped decisions. This book doesn’t just recount the battlefield events—it unpacks the roots, the chaos, and the uneasy ceasefire that left the world wondering: Is the next war only a matter of time?

Perfect for readers of modern history, politics, or anyone fascinated by the fragile line between peace and war.
Are you prepared for what comes next?
Grab your copy of *THE 12-DAY WAR* now!
Click the link in the comment section.

Kabir Ɗahiru Sule, Ɗan majalisar Tarauni zai gina masallaci da Zauren jarabawa a makarantar Unguwar GanoDaga Ibrahim Muh...
24/07/2025

Kabir Ɗahiru Sule, Ɗan majalisar Tarauni zai gina masallaci da Zauren jarabawa a makarantar Unguwar Gano

Daga Ibrahim Muhammad

Ɗan Majalisar jiha mai wakiltar ƙaramar hukumar Tarauni, Hon. Kabiru Ɗahiru Sule ADS ya yi alƙawarin gina wa makarantar Sakandaren gwamnati ta Unguwar Gano Masallaci da zauren jarabawa a harabar makarantar kafin ƙarshen shekara.

Ya bayyana hakan ne da yake jawabi a yayin taron ranar bayar da kyautuka ga ɗalibai da aka gudanar a harabar makarantar ranar Laraba, bayan ya karɓi lambar yabo da makarantar ta karrama shi da ita

Ɗan Majalisar dai ya ƙara da ɗaukar nauyin biya wa ɗalibai masu hazaƙa guda 600 da za a sanya aji na musamman na makarantar kuɗin rijista da za a zaɓo su daga gidajen masu ƙaramin ƙarfi da ba za su iya biya ba a yankin ƙaramar hukumar, inda ya ba da kuɗin ₦300,000 nan take, tare da alƙawarin bayar da bencina na zaman ɗalibai guda 20 zai kuma yi ƙoƙarin kawo cibiyar yin jarabawar JAMB a makarantar.

Ya ce, ilimi shi ne ginshiƙin cigaban kowace al’umma da suke koyi da ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf ta ba shi goyon baya a tsarin da ya ɗauka na sanya dokar ta-ɓaci a kan ilimi duba da ilimi na kowa ne za su yi ƙoƙarin taimakawa daidai da ikonsa.

Hon. Kabiru Ɗahiru Sule ya bayyana irin ɗimbin ayyukan da ya gudanar a mazaɓun ƙaramar hukumar daban-daban k**a gina daga gina rukunin azuzuwa da kuma gyaran makarantu da gina masallatai da cibiyoyin addinin Musulunci.

Shi ma a jawabinsa tunda farko shugaban makarantar Sakandaren gwamnati na Unguwar Gano, Malam Auwalu Ali Yalwa ya bayyana taron da cewa shi ne na farko na raba kyautuka ga ɗalibai masu ƙwazo da aka yi a makarantar da ya sami halartar ɗan Majalisar jiha na Tarauni da kansilan mazaɓar Unguwar Gano wanda shi ne ya wakilci shugaban ƙaramar hukumar Tarauni Hon. Ahmad Sekure.Itama shugaban ƙungiyar shugabannin makarantun Sakandire na jihar Kano, Hajiya Uwani Ahmad Balarabe da mutane da dama sun halarta.

Ya ƙara da cewa zuwan sa a matsayin shugaban makarantar ya sami kyakkyawan haɗin kai daga malamai suna aiki tare don cigaban makarantar kuma shi ne ya bijiro da tsarin fara yin Sallar Azahar a jam’i ga ɗalibai a makarantar.

Sannan ta zama cibiya ta yin jarabawar WAEC da NECO da wasu makarantun ma za su zo su yi a nan.

Shugaban makarantar Sakandaren gwamnatin na Unguwar Gano ya ce, yanzu suna da ƙarancin ajujuwa da rashin zauren jarabawa da kuma abin zama da masallaci wanda sun ji daɗin ɗan majalisar jaha, Jon Kabiru Ɗahiru Sule ADS da ya halarci taron ya yi alƙawarin gina musu sannan tsohon shugaban ƙaramar hukumar Tarauni Habib Zakari shi ma ya yi alƙawarin kawo musu allo na zamani wanda wannan babban nasara ce a gare su suna kuma kira da a zo a samar musu rijiyar burtsatse saboda sai sun fita wajen makarantar suke samun ruwa.

Malam Auwal Ali Yalwa ya yaba da haɗin kai da iyaye suke ba su ta yin iya ƙoƙarinsu, musamman ta yadda suke tiritiri da ‘ya’yansu wajen zuwa makarantar, yana fata za su cigaba da juriya da ba da kulawa sosai, ya kuma nemi al’umma su cigaba da ba su haɗin kai.

A yayin taron makarantar sakandaren gwamnatin ta Unguwar Gano ta karrama mutane da dama da lambar yabo bisa gudummawa da suke bai wa bunƙasa cigaban ilimi, ciki har da shugaban ƙaramar hukumar Tarauni, Hon. Ahmad Sekure da Hon. Kabiru Ɗahiru Sule ɗan Majalisar jaha da shugabar ƙungiyar ANCOPSS ta jihar Kano da sauran masu ruwa da tsaki a harkar ilimi da Malaman makarantar masu hazaƙa.

AN YI YINKURIN KASHE NETANYAHU  -MAI-ZAFI: Hukumar tsaro ta Isra’ila, Shin Bet, ta k**a wata mata kan zargin kokarin kas...
23/07/2025

AN YI YINKURIN KASHE NETANYAHU

-MAI-ZAFI: Hukumar tsaro ta Isra’ila, Shin Bet, ta k**a wata mata kan zargin kokarin kashe Firayim Minista Benjamin Netanyahu – k**ar yadda tashar KAN ta ruwaito.

An k**a matar ne bisa laifin tsara harin kashe Netanyahu ta amfani da bam, kuma ana shirin gurfanar da ita gaban kotu kan laifin shirya aikata laifi da ta’addanci.

Ambasada Salga ya jagoranci taron ADC don ƙarfafa gwiwaDaga Ibrahim Muhammad KanoMatasan jam’iyyar ADC da Ƙungiyar Iyali...
21/07/2025

Ambasada Salga ya jagoranci taron ADC don ƙarfafa gwiwa

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Matasan jam’iyyar ADC da Ƙungiyar Iyali Ɗaya na jam’iyyar reshen ƙaramar hukumar Dala a jihar Kano, ta gudanar ta taron zaburarwa da ƙarfafa gwiwa ga ‘ya’yan jam’iyyar domin tunkarar samun nasara.

Taron an yi shi ne a ɗakin taro na Mumbayya ranar Lahadi ƙarƙashin jagorancin shugaban ADC Iyali Ɗaya na ƙasa, shugaban Inuwar ‘yan takarar Majalisar Tarayya da na jiha a PDP a zaɓen 2023 da yanzu s**a koma jam’iyyar ADC, Ambasada AbdulRahman Mainasara Salga.

A jawabinsa a wajen taron, ɗan takarar Gwamnan jihar Kano a zaɓen 2023 a jam’iyyar ADC, Malam Ibrahim Khalil ya ja hankalin mahalarta taron da cewa idan da gaske mutane suke za su yi canji, to a gani a aikace, kuma su riƙe amana, su zama masu jajircewa, “Domin haka ne matakin tabbatar da samun nasara,” in ji shi.

A nasa jawabin shugaban ADC Iyali ɗaya na ƙasa, AbdulRahman Mainasara Salga, ya gode wa mahalarta taron. Ya ce, dawowarsa Kano mako biyu da s**a gabata ya ga a kowace jiha ana cewa an karɓi ADC, amma sai ya ga ya k**ata a ga motsinta a nan Kano, shi ya sa s**a shirya wannan taro na ƙaramar Hukumar Dala.

Ya yi nuni da cewa akwai ban tsoro a tafiyar da ake a ƙasar nan a halin yanzu domin a matsayinsa na haifaffen ƙaramar hukumar Dala a Gwammaja ya bar Kano ya tafi Abuja da ₦1,500 kaɗai a matsayinsa na matashi don neman na kansa duk da iyayensa suna da hali, amma ya tafi ya kwana a masallaci da kasuwa a ƙoƙarin neman halal da yaƙinin Allah shi ne mai yin komai, kuma ya yi masa.

Ya ce ya ga haƙƙoƙin da ake saryarwa na al’umma da mutane da dama, za su iya amfana idan wakilansu da ake zaɓa suke zuwa Majalisar Tarayya Abuja suna yin abin da ya k**ata. Kuma ya yi ƙoƙarin nusar da wasu daga wakilan hanyoyin da za su bi su amfanar da al’ummarsu, amma sun yi wasarere da hakan, ba sa kulawa sai dai su zo su riƙa wasu abubuwa daban.

Ya ce, wannan kishin na ganin an sama wa al’umma dama ce tasa ya shiga siyasa domin ya taimaki al’umma, kuma idan ba wannan niyya ce a ransa ba kada Allah ya ba shi nasara.

Mainasara ya ce, lokacin da ya fito takarar Majalisar Tarayya a Dala ba shi da kowa a lokacin sai wasu jiga-jiran jam’iyyar s**a nuna ba sa yin sa, amma a haka ya tsaya ya dage ya shiga cikin takara da aka so a hana shi, amma ya karɓo ta a kotu saboda niyyarsa mai kyau ce.

Ya ce, a cikin jam’iyyar PDP sun samu mutane da yawa munafukai da yawa a cikinta sun sayar da jam’iyyar suna yi mata zangon ƙasa, ta hanyar amfani da Nyeson Wike don su riƙa haifar da matsala kar a sami nasara a jam’iyyar PDP, wanda idan da an tafi a hakan har zuwa zaɓen 2027 da Tinubu ya koma an gama zaɓe.

AbdulRahman Mainasara Salga ya ce, kasancewar suna yin siyasa ne don al’umma shi ya sa s**a dawo wannan tafiyar ta haɗakar ADC da suke goyon bayan tafiyar Atiku Abubakar.

Ya yi kira ga matasa su tashi su ƙwaci haƙƙin al’umma kar su bari a riƙa wulaƙanta su ko kuma a juyar da ƙwaƙwalwarsu.

Mainasara ya jaddada cewa sun dawo jam’iyyar ADC ne don tana da mutane jajirtattu, masu kishi da gaskiya, domin sai da APC s**a nemi su bai wa shugabannin ta kuɗi don su yi amfani da su don a haifar da rashin jituwa k**ar yadda s**a shiga PDP da SDP da sauran jam’iyyun adawa, amma s**a ƙi yarda.

Ya ce Atiku Abubakar yana son jam’iyyar PDP a ransa, su ma da suke tare da shi haka, amma saboda maƙiya da munafukai da aka ƙunsa a cikinta don hana ta zaman lafiya s**a ga cewa ba za a yi wa talakawa adalci ba, shi ya sa s**a fita, “Saboda maƙiya ba ba sa son al’umma, ana sayar da su. Domin me za mu sake zaɓen Tinubu? Ya k**ata mu tashi mu taimaki al’ummar mu ta hanyar bai wa ADC goyon baya,” in ji shi.

Shi ma a jawabinsa shugaban jam’iyyar ADC na jihar Kano, Hon. Musa Shu’aibu Ungogo ya ƙarfafa gwiwar matasa a kan su tashi su jajirce wajen nema wa al’umma mafita, domin shugabanni da s**a yi gwagwarmaya na baya domin samun ‘yancin ƙasar nan tun suna matasa s**a yi s**a kafa jam’iyyu irin su NEPU da NPC da s**a amfanawa al’umma da har yanzu ake tuna irin sadaukarwa da s**a yi.

A yayin taron an gabatar da muhimmiyar faɗakarwa a kan muhimmanci da tasirin amfanin kafar sadarwa na zamani wajen wayar da kan mutane don samun karɓuwa a harkar siyasa wanda Aminu Idris Tudun Wada ya gabatar.

The world held its breath for twelve days  What began as a long-simmering confrontation between Israel and Iran exploded...
17/07/2025

The world held its breath for twelve days

What began as a long-simmering confrontation between Israel and Iran exploded into open warfare with terrifying speed, bringing the Middle East—and the globe—to the edge of catastrophe. The 12-Day War was not merely another regional clash; it was a crisis that threatened to spiral into a wider conflagration, one that could have drawn in superpowers, disrupted global economies, and reshaped the geopolitical order. For nearly two weeks, the specter of World War III loomed as missiles arced across the skies, cities trembled under bombardment, and leaders weighed decisions that could alter history.

This book, THE 12-DAY WAR, is not just an account of those fateful days—it is an exploration of how we got there, why the conflict unfolded as it did, and what it means for the future. The war did not emerge from a vacuum. Decades of proxy battles, ideological hostility, and failed diplomacy set the stage for this eruption. In these pages, we will trace the origins of the Israel-Iran rivalry, from its roots in revolution and religious prophecy to the modern-day brinkmanship that brought the two nations to open war. We will examine the critical moments that defined the conflict—the surprise attacks, the failed ceasefires, the diplomatic scrambles—and the individuals who shaped its course, from Israeli Prime Minister Benjamin Netanyahu to Iran’s Supreme Leader Ayatollah Khamenei.

But this is also a story about perception and prophecy. In the Middle East, history is often viewed through the lens of divine promise and apocalyptic expectation. For some, the war was not just a political struggle but a fulfillment of ancient predictions—a belief that fueled both fear and fervor on all sides. We will explore how these narratives influenced decision-makers and ordinary citizens alike, and whether they offer any clues about what comes next.

The war’s aftermath left more questions than answers. The ceasefire, fragile and fraught with mistrust, did little to address the underlying grievances that ignited the conflict. Regional powers scrambled to adjust their strategies, global markets reeled from the shock, and ordinary people—from Tel Aviv to Tehran—were left wondering if this was truly the end or merely an intermission before a deadlier round of fighting.

Drawing on firsthand reporting from major media outlets like Al Jazeera, as well as speeches, intelligence assessments, and expert analysis, this book pieces together the full picture of the war—its causes, its consequences, and the alarming possibilities of what might follow. The stakes could not be higher. If another war comes, it may not last just twelve days. It may not end with a ceasefire at all.

As you turn these pages, consider this: Are we witnessing the beginning of a new, more dangerous era in the Middle East? Or was this conflict a warning—one that the world can still heed before it is too late?

The answers may determine whether the next war is merely a risk—or an inevitability.

ABRAHAM MOSES

'Yan takarar majalisun tarayya da na jiha  27 na PDP a Kano ƙarƙashin jagorancin AbdulRahman Salga sun koma ADC.Daga Ibr...
17/07/2025

'Yan takarar majalisun tarayya da na jiha 27 na PDP a Kano ƙarƙashin jagorancin AbdulRahman Salga sun koma ADC.

Daga Ibrahim Muhammad

Wasu daga 'yan takarar da s**a yi takarar majalisun tarayya da na jiha a ƙarƙashin jam'iyar PDP a zaɓen 2023 a jihar Kano guda 27 ƙarƙashin jagorancin Hon. AbdulRahman M Salga sun bayyana ficewarsu daga jam'iyyar zuwa jam'iyyar ADC.

Sun bayyana haka ne a wani taron manema labarai da s**a gudanar a Kano. AbdulRahman Salga, wanda shi ne tsohon shugaban PDP iyali daya, kuma wanda ya yi takarar majalisar tarayya na PDP a karamar hukumar Dala ya ce sun yanke shawarar barin jam'iyyar ne bayan sun tuntubi magoya baya, 'yan'uwa da abokan arziki.

Ya bayyana cewa daga cikin dalilansu na barin jam'iyyar PDP shi ne na yawan samun rigimar cikin gida da ta addabi jam'iyyar sak**akon akwai wanda s**a makale a cikin suke kunna wutar rikicin da suke cin gajiyar hakan saboda sun dauki hakan sana'a.

Hon. AbdulRahman M.Salga ya ce su a tafiyar su ta siyasa suna yi ne domin kishin nema wa al'umma mafita, musamman talakawa daga halin matsi da suke ciki, don haka a matsayin su na yan takara s**a amince su bar jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar ADC .

Mainasara ya ce, komawarsu ADC zai ba su damar gudanar da siyasa ta kishi da 'yanci ta nema wa al'ummar kasar nan mafita kuma nan gaba kadan akwai gagarumin gangamin jam'iyyar ADC da zasu gudanar a jihar Kano

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dillaliya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dillaliya:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share