HT Africa

Hotuna: Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau.Majlisar Malamai...
23/08/2025

Hotuna: Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau.

Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau a ofishinsa dake sakateriyar kungiyar dake babban birnin tarayya Abuja.

Malaman da s**a fito daga kungiyoyin addinin musulunci, sunce manufar ziyarar shine Hadinkai tsakanin musilmi, domin a samu fahimtar juna da hada karfi da karfe domin tunkarar maunfofin musulunci a dukkan lamura.

Jibwis Nigeria

Yadda aka gudanar da jana'izar mahaifin Bello Habib Galadinchi, Alhaji Habib Galadinchi Ubangiji ya jikansa ya masa raha...
07/08/2025

Yadda aka gudanar da jana'izar mahaifin Bello Habib Galadinchi, Alhaji Habib Galadinchi Ubangiji ya jikansa ya masa rahama amin.

Wani makusancin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya shaidawa jaridar Vanguard cewa tuni shirye shirye sun yi nisa ...
07/08/2025

Wani makusancin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya shaidawa jaridar Vanguard cewa tuni shirye shirye sun yi nisa wajen ganin jam'iyyar PDP ta tsayar da Jonathan a matsayin dan takararta na shugaban kasa a zaben 2027.

Jaridar ta kara da cewa yanzu haka tsohon shugaban kasa Jonathan ya maida hankali wajen nemo hanyoyin magance matsalolin da s**a dabaibaye Najeriya, musamman matsalar talauci da ƙuncin rayuwa.

Gidauniyar tsohon mataimakin shugabancin Nijeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya dauki nauyin karatun yaran nan guda ukku wad...
07/08/2025

Gidauniyar tsohon mataimakin shugabancin Nijeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya dauki nauyin karatun yaran nan guda ukku wadanda s**a lashe gasar turanci yan jihar yobe,
Nafisa Abdullahi, Rukayya Muhammad Fema, Khadija Khashim Kalli, tun daga ida kammala karatun sakandiri har zuwa kowace jami'a a ko'ina suke da Muradin zuwa a duniya.

Kwamishinan Sufuri na jihar Kano, Ibrahim Namadi Dala, ya ajiye mukaminsa sa’o’i kaɗan bayan gwamna Abba Kabir Yusuf ya ...
06/08/2025

Kwamishinan Sufuri na jihar Kano, Ibrahim Namadi Dala, ya ajiye mukaminsa sa’o’i kaɗan bayan gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin bincike da aka kafa don bincikar rawar da ya taka wajen karɓar belin wanda ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, Kwamishinan ya bayyana cewa ya yanke shawarar yin murabus ne saboda maslaha al'umma.

Matashiya daga Jihar Yobe, ta doke Kasashen Turawa 69 a Gasar Ingilishi Ta DuniyaƊaliba mai shekara 17 daga jihar Yobe, ...
05/08/2025

Matashiya daga Jihar Yobe, ta doke Kasashen Turawa 69 a Gasar Ingilishi Ta Duniya

Ɗaliba mai shekara 17 daga jihar Yobe, Nafisa Abdullah Aminu, ta kafa tarihi a gasar TeenEagle Global Finals 2025 da aka gudanar a birnin London ta ƙasar Birtaniya, inda ta lashe kambun gwarzuwar ɗaliba mafi ƙwarewa a harshen Turanci a duniya.

Nafisa, wadda ta wakilci Najeriya ƙarƙashin Nigerian Tulip International College (NTIC), Yobe, ta doke sama da dalibai 20,000 daga ƙasashe 69, ciki har da waɗanda ke magana da harshen Turanci a matsayin yaren uwa.

Wannan gagarumar nasara ta janyo yabo da farin ciki daga 'yan Najeriya da dama, musamman ganin yadda ɗalibar Najeriya daga arewa maso gabas wuri da ake fama da ƙalubalen ilimi amma ta yi fice a matakin duniya.

DAGA Abdul Journalist …

Tinubu Ya Gwangwaje 'Yan Super Falcons Da Kyautar Dala 100,000 Da Kuma Gida Kowannen SuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu y...
29/07/2025

Tinubu Ya Gwangwaje 'Yan Super Falcons Da Kyautar Dala 100,000 Da Kuma Gida Kowannen Su

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya karrama 'yan rundunar ƙwallon ƙafa ta mata ta Nijeriya, wato Super Falcons, da kyautar karramawa ta ƙasa da kuma kyautar kuɗi da ta gidan kwana saboda nasarar su a gasar.

Ya kuke ganin wanan kyautar a lokacin da aka gagara biyan tsofafin yan sanda kudaden aikinsu na tsawon shekaru 35 da s**a shafe suna aiki domin kare kasa da al'ummar ta.

29/07/2025

Upper na MTN Data 4GB a 1k kacal Amma ba kowa yake samu ba

*312*65*3 #

Anga watan ramadan a kasar saudiya a yau 28 Fabairun 2025
28/02/2025

Anga watan ramadan a kasar saudiya a yau 28 Fabairun 2025

Yanzu yanzu: Kotu Ta Bayar Da Belin Farfesa Yusuf Usman....Kotu ta 44 dake birnin tarayyar Najeriya Abuja ta bayar da be...
27/02/2025

Yanzu yanzu: Kotu Ta Bayar Da Belin Farfesa Yusuf Usman....

Kotu ta 44 dake birnin tarayyar Najeriya Abuja ta bayar da belin Farfesa Usman Yusuf bayan kimanin kwanaki Ashirin da Hudu 24 a hannun jami‘an tsaro bisa zargen-zargen aikata ba daidai ba a hukumar Inshorar lafiya ta ƙasa wanda hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ke masa.

Ladan Salihu yace ƙa'idar da aka bada wajen bada shi zasu iya cika ta cikin awa Guda.

Muhammad Aminu Kabir

Yanzu Yanzu: Wani Bawan Allah Ya Aiko Mani Da Wannan Bayanin Akan Brigadier Janaral Ahmed Muhammad Daku...Assalamu Alaik...
08/02/2025

Yanzu Yanzu: Wani Bawan Allah Ya Aiko Mani Da Wannan Bayanin Akan Brigadier Janaral Ahmed Muhammad Daku...

Assalamu Alaikum Barka da Asuba, naga rubutun da akayi a media kan Ahmad Daku, Ba gaskiya bane don shi bai ma ɗauka ba, b***e ya maida.

Ni nayi aiki da tsohuwar Matar shi da ya zauna Kano da Sokoto da ita, munyi firarshi sosai.

Wata rana tace zata zo Katsina kuma Personal Car ɗin shi bata iya zuwa, sai dai aka kai ta da Motar haya daga Sokoto zuwa Katsina.

Basu da wata motar gida banda Personal car ɗin shi, idan ya tashi Office baa ƙara hawan motar office sai lokacin aiki.

Ko lokacin aiki ba a Personal buƙatar wani ko ta gidan shi.

Tace min wata rana Mamarshi taje Kano yana Gwamna aka ɗauke ta da Motar Office, ya kori driver motar, yayi ta istigifari akan wannan kawai, tace kamar ma har azumi yayi na neman yafiyar Allah akan wannan, Abin nashi kam yana da yawa.

Kazalika naga Malam Ibrahim Sheme shima ya musanta wannan zargin a shafin shi harma ya bada labarin haɗuwar su a ƙasar Israel yayin da yaje rakiyar Alhazai kiristoci.

Muhammad Aminu Kabir

Ina kira ga Gwamnonin Arewa su guji yin Sasanci da Ɓarayin Daji" --Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr. Mustapha...
08/02/2025

Ina kira ga Gwamnonin Arewa su guji yin Sasanci da Ɓarayin Daji" --Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr. Mustapha Inuwa.

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina Dr. Mustapha Inuwa wanda ya kasance jigo a Jam'iyyar Adawa ta PDP a Jihar Katsina, ya yi kira ga Gwamnatocin arewa da su guji yin sulhu da ƴan ta'addan daji a cewar sa, hakan wata hanyar yaudara ce da ƴan ta'addan ke amfani da ita a duk shekara.

Kamar yadda ya bayyana, a duk shekara ƴan ta'addan na ɓullowa da yaudarar neman Sasanci da Gwamnati, sakamakon irin halin matsi da suke shiga a rayuwar Daji, saboda rashin abinci da kuma tsirrai a matsugunnan da suke ɓoye.

A cewar barayin dajin suna neman sulhu ne domin su samu damar shigowa cikin gari cin kasuwanni da kiwata dabbobinsu.

Katsina Reporters

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HT Africa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to HT Africa:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share