Kwankasiyya Nigeria

Kwankasiyya Nigeria Kwankwasiyya online Nigeria domin tabbatar da Akidar kwankwasiyya

08/04/2025
Kwamishinan yada labarai na Jahar Kano ya taya Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif Murnar Lashe lambar yabo ta gwamna mafi kwa...
08/04/2025

Kwamishinan yada labarai na Jahar Kano ya taya Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif Murnar Lashe lambar yabo ta gwamna mafi kwazo a fannin ilimi a Najeriya da Jaridar Leadership ta bashi.

Cikin wata wasika ta kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gidan Kwamaret Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar, tace “Wannan fitacciyar lambar yabo ce da ta dace ga jajircewar Maigirma Gwamna, jagoranci na kwarai, da kuma dawwamammiyar gudunmawa ga cigaban ilimi jihar Kano.

Wanda yace ta hanyar jagorancinsa Kano ta samu gagarumar nasara wajen tabbatar da samar da ingantaccen ilimi ga kowa da kowa.

Daga karshe sanarwar ta bayyana cewar Ma'aikatar yada labarai ta jaddada goyon bayanta da godiya ga irin namijin kokarin da Mai girma Gwamna ya yi wajen samar da kyakkyawar makoma ga jahar Kano jama'arta.

KWANKWASIYYA KENANCaptain Jibrin Nalado Aliyu na daya daga cikin yan Jihar Kano da Jagora Engr Dr Rabiu Musa Kwankwaso y...
08/04/2025

KWANKWASIYYA KENAN

Captain Jibrin Nalado Aliyu na daya daga cikin yan Jihar Kano da Jagora Engr Dr Rabiu Musa Kwankwaso ya dauki nauyin karatun su zuwa Kasar Jordan domin koyon tukin Jirgin sama. Yana daya daga cikin mutum 100 da s**a amfana inda a halin yanzu da yawan su suna aiki da kamfanoni daban daban.

Yanzu wannan bawan Allah shine shugaban karamar Hukumar Minjibir. Wannan ya nuna karara yadda Kwankwasiyya ke cicciba alummar Jihar Kano musamman matasa domin cimma burukan su na rayuwa.

Duk alummar da ta ci gaba, za ka samu wannan alumma ta bawa Ilimi muhimmanci ne. Wannan ce ta sanya a halin yanzu, Gwamanan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf, ya himmatu wajen ganin ya gyara komai daya shafi Ilimi domin Jihar Kano ta kere sauran Jihohi ta wannan fuska.

Kafin zuwan Jagora Engr Dr Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin Gwamna, matuka Jirgin sama basu fi guda 10 ba a Jihar Kano. Wannan ce ta sanya ya dauki nauyin matasa 100 a wannan bangare kadai kuma kwalliya ta biya kudin sabulu. Yanzu dole idan ana maganar yawan matuka Jirgin sama a Najeriya kuma kwararru, Jihar Kano dole na sahun gaba.

Da dumi'dumi: Ya zama Gwamna Mafi kyautatawa al'umma.Gwamna Abba K. Yusuf Ya lashe lambar Yabo na Jaridar leadership Ama...
08/04/2025

Da dumi'dumi: Ya zama Gwamna Mafi kyautatawa al'umma.

Gwamna Abba K. Yusuf Ya lashe lambar Yabo na Jaridar leadership Amatsayin Gwamna Mafi bayarwa da gudunmawa ga al'ummar da yake Mulka tare wanda Yanzu haka Yake gudana A Abuja gwamna Abba yana halartar taron manema labarai da bayar da kyaututtuka karo na 17 da aka yi a Old Banquet Hall dake State House.

Gwamna ya shirya don karbar lambar yabo ta ‘Gwamnan Shekara 2024 bisa la’akari da irin jagoranci da gudunmawar da ya bayar wajen gudanar da mulki a Jihar Kano tun bayan zaben sa a 2023.

Mai Girma Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya karbi bakwancin takwaransa na jihar katsina Gwamna Umar Dikko ra...
07/04/2025

Mai Girma Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya karbi bakwancin takwaransa na jihar katsina Gwamna Umar Dikko radda a fadar Gwamnatin jihar kano.

Inda Gwamnan na jihar katsinan yakawo wannan ziyara jihar kano domin mika sakon ta’aziyyarsa da Gwamnatinsa da Al’umar jihar katsina, ga Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa babban rashin na uba agaremu Marigayi Galadiman kano,Alhaji Abbas Sunusi wanda Allah yaiwa rasuwa acikin wannan sati da muke ban kwana dashi.

Gwamnan jihar na katsina yayi Addu’a ga Marigayin Dafatan Allah ubangiji yajikansa yaimasa Rahama Ameen summa Ameen.

Alhamdulillah, bayan Kammala taron Shugaban Yaran Mai Taken Kwankwasiyya Gida-Gida New Generation Mutane 4 zasu Rabauta ...
06/04/2025

Alhamdulillah, bayan Kammala taron Shugaban Yaran Mai Taken Kwankwasiyya Gida-Gida New Generation Mutane 4 zasu Rabauta da Kujerar Hajji daga Gwamnatin Kano, wanda s**a hadar da

1-Shugaban Yara Abdulbasi Aminu

2. Mai Kwaikwayon Madugu-Amb.Khalil Rabiu

3.Mai kwaikwayo Gwamna-Imam Abdurrahman Lawan

4. Mai kwaikwayon Sarkin Kano- Ibrahim Bashir Waziri

Congratulations all 🙏

Wanda ya kafa bankin Stanbic IBTC ya caccaki rundunar ƴansanda ta ƙasa kan gayyatar Sarki Sanusi Atedo Peterside, wanda ...
06/04/2025

Wanda ya kafa bankin Stanbic IBTC ya caccaki rundunar ƴansanda ta ƙasa kan gayyatar Sarki Sanusi

Atedo Peterside, wanda ya kafa Bankin Stanbic IBTC , ya soki gayyatar da Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi wa Muhammadu Sanusi, Sarkin Kano, zuwa hedikwatar rundunar da ke Abuja.

An gayyaci Sanusi domin amsa tambayoyi kan kisan da aka yi a lokacin da Sarkin ke komawa gida bayan kammala sallar idi a ranar Lahadi da ta gabata.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na kafar X a yau Lahadi, Peterside ya ce rundunar ‘yansandan Kano ce ya fi da cewa ta gayyaci Sarkin.

“Mene ne Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ke kokarin mai da kasar nan? Najeriya ta zama kasa karkashin ikon ‘yan sanda ne? Shin akwai wata tambaya da Kwamishinan ‘Yan Sanda ba zai iya yi wa Sarkin Kano ba a cikin Kano a madadin manyansa da ke Abuja?” in ji shi.

Peterside ya kara da cewa gayyatar mutane daga jihohi daban-daban na nuni da “cin zarafi” ne kuma ya kamata a dakile irin wannan dabi’a.

Daily Nigeria ✍🏻

TUNA BAYA: RAYUWA A SIYASA.Ranar Asabar 17/5/2014 da karfe 11:39 na dare a cikin Makarantar Gwale Sakandire (Coalition C...
30/12/2024

TUNA BAYA: RAYUWA A SIYASA.

Ranar Asabar 17/5/2014 da karfe 11:39 na dare a cikin Makarantar Gwale Sakandire (Coalition Centre) yayin tattara sakamakon zabe ba kananan hukumomi mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf shida Abdullahi Abbas sune masu karbo zabe a Karamar Hukumar Gwale. Jiya ba yauba.

Gwamnan ya bayyana haka ne a wajen rufe bitar sanin makamar aiki da aka shiryawa kwamishinoni da manyan sakatarorin gwam...
22/12/2024

Gwamnan ya bayyana haka ne a wajen rufe bitar sanin makamar aiki da aka shiryawa kwamishinoni da manyan sakatarorin gwamnatin jihar Kano a garin Kaduna.

Address

Kano

Telephone

+2349064456328

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kwankasiyya Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kwankasiyya Nigeria:

Share