Sokoto Plain

Sokoto Plain To Bring Positive Changes to our Society.

12/08/2025

Comrade Bello Shuwa ya Bayyana cewa "Shugaba Tinubu bazai Kara cin Zabe ba a 2027".

27/07/2025

Kowa ya Debo da Zafi.....Tare da Yusuf Bunga

Minene Abin Aibatawa a Wannan Hoton, na Jaruma Ummey Nuhu?Mutane Na Cyber bullying na Wannan baiwar Allah kan Hoton da a...
25/07/2025

Minene Abin Aibatawa a Wannan Hoton, na Jaruma Ummey Nuhu?

Mutane Na Cyber bullying na Wannan baiwar Allah kan Hoton da aka Tsakure shi daga Zauren Tattaunawa na Gabon Talkshow.

Abin Mamaki ga Mutane shin kuna Tsammani ku ganta ne Yanda yake Shekaru Kusan 20 da S**a Wuce? Ai Ko ba komai Shekaru ba Karya ne ba, in kana musu Ka Duba daga kanka.

Wannan Abin bai Kyauta ba, Muna Rokon a kiyaye Sanya Mutun Cikin Damuwa ta Wannan Hanyar, Inda zai ji ya tsargu saboda Yanda ake Kokarin Nuna shi, Kamar wani Mummunan Abu ya same shi.

23/07/2025

Kasar Mu A Yau! Tare da Prof Ghazali Bello. Akan Mutuwar Shugaba Buhari da Kuma Zanga Zangar Pension Yan Sanda.

TARIHIN TSHOHON SHUGABAN NIGERIA JANAR MUHAMMADU BUHARI (RTD)HAIHUWA:An haifi Muhammadu Buhari a ranar 17 ga Disamba, 19...
13/07/2025

TARIHIN TSHOHON SHUGABAN NIGERIA JANAR MUHAMMADU BUHARI (RTD)

HAIHUWA:

An haifi Muhammadu Buhari a ranar 17 ga Disamba, 1942, a garin Daura, Jihar Katsina. Ya fito daga iyalin Musulmi kuma Fulani. Mahaifinsa, Mallam Hardo Adamu, manomi ne kuma Malami; mahaifiyarsa kuma Hajiya Zulaihat, ta fito daga Zaria.

ILIMI:

Ya fara makarantar Primary School ta Daura, daga nan ya wuce Middle School Katsina.

Daga baya ya samu gurbin karatu a Katsina Provincial Secondary School (wanda aka fi sani da Government College Katsina).

Bayan kammala sakandare, ya shiga Nigerian Military Training College (NMTC) a Kaduna a shekarar 1962.

Daga nan sai ya je Mons Officer Cadet School a Aldershot, Ingila, sannan ya karɓi horo a India, USSR (Rasha) da America.

RAYUWAR SOJA DA SHUGABANCI NA MULKIN SOJA (1983–1985)

Ya shiga soja a shekarar 1961.

Ya taka rawa a yakin basasar Najeriya (1967–1970), ya rike mukamai da dama kamar Haka;

Gwamnan Jihar Arewa-Maso-Yamma (1975–1976).

Kwamandan rundunar soja ta 3.

Kwamishinan man fetur a lokacin mulkin Janar Murtala Mohammed.

A ranar 31 ga Disamba, 1983, ya jagoranci juyin mulki da ya kifar da gwamnatin Shehu Shagari, sannan ya zama shugaban kasa na mulkin soja daga 1983 zuwa 1985.

An kifar da shi ta hanyar juyin mulki a shekarar 1985, a lokacin Janar Ibrahim Babangida.

RAYUWAR BAYAN MULKIN SOJA:

Bayan kifar da mulkinsa, an tsare shi har tsawon shekaru fiye da biyu ba tare da tuhuma ba.

Ya zama daya daga cikin jagororin da s**a nemi a tsaftace Najeriya daga rashawa da almundahana.

GWAGWARMAYA TA SIYASA:

Ya tsaya takarar shugabancin ƙasa sau uku:

2003 (tare da ANPP) – ya fadi.

2007 (tare da ANPP) – ya fadi.

2011 (tare da CPC) – ya fadi.

A 2015 ya sake tsayawa takara a karkashin jam’iyyar APC bayan da CPC da wasu s**a hade.

A karo na hudu, sai ya samu nasara ya zama shugaban kasa a ranar 29 ga Mayu, 2015, ya sake lashe zabe a 2019, ya kammala mulkinsa a 29 ga Mayu, 2023.

MUHIMMAN AIKI DA CIGABA A LOKACIN SHUGABANCINSA

Ya ƙaddamar da yanayin yaki da rashawa (Anti-Corruption War).

Ya kafa N-Power da wasu shirye-shiryen tallafi ga matasa da marasa galihu.

Ya jagoranci gina layin dogo (Railway Projects) da tituna a sassan Najeriya.

Ya yaki kungiyar Boko Haram, duk da cewa har yanzu ta cigaba da kai hare-hare.

Ya ƙaddamar da naira re-design policy da kuma yaki da satar kudaden gwamnati.

ZARGI DA SUKAR MULKINSU:

A lokacin mulkinsa daga 2015 zuwa 2023, an zargi gwamnatin Buhari da abubuwa da dama, ciki har da:

1. Rashawa:

Duk da ya yi ikirarin yaki da cin hanci, an zargi wasu jami’ansa da karkatar da kudade.

Ana ambato batun Abba Kyari da wasu manyan gwamnati da s**a fuskanci zargi.

2. Tabarbarewar Tsaro:

An zargi mulkinsa da kasa magance matsalar tsaro, musamman a yankin Arewa maso yamma da arewa ta tsakiya (banditry da kidnapping).

Boko Haram da ISWAP sun ci gaba da kai hare-hare duk da kokarin gwamnati.

3. Matsin Tattalin Arziki:

Farashin kaya ya tashi, hauhawar farashi (inflation) ya yi muni sosai.

Kudin Naira ya ruguje sosai, matsalar kudaden kasashen waje (Forex) ta tsananta.

An shiga matsanancin matsin tattali bayan COVID-19 da kuma janye tallafin man fetur.

4. Rashin Jin Dadi ga Jama’a:

Talauci ya karu sosai a lokacin mulkinsa.

Ana zargin gwamnatinsa da rashin kulawa da bukatun talakawa, musamman ma a karkara.

An yawaita yajin aiki da gurguntar da fannin ilimi (har da ASUU Strike mai tsawo).

5. Rikicin Kabilanci da Addini:

Wasu sun zargi gwamnatin da nuna son kai (nepotism), musamman wajen nade-naden shugabanci da mukamai.

RAYUWA DA MUTUWARSA

Bayan kammala mulki a 2023, ya koma gidansa a Daura, Jihar Katsina.

Ya dauki hutu daga harkokin siyasa.

Ya rasu a shekarar 13-7-2025.

Da Minene Y’an Kasar nan zasu tuna da Shugaba Buhari?

Nasir Ibrahim Janbuzu 2025

Kwamitin Maida Alkhairi na gidauniyar Attahiru Bafarawa ya Bada Tallafin karatu na Shekara ukku ga Sama ga Dalibbai 100 ...
21/02/2025

Kwamitin Maida Alkhairi na gidauniyar Attahiru Bafarawa ya Bada Tallafin karatu na Shekara ukku ga Sama ga Dalibbai 100 a kananin Hukumomin jihar Sokoto....

A cigaba da aiwatar da Ayukkan Kwamitin ya gabatar da Tallafin kudin karatu ga Dalibban da s**a yi Nasarar karatu a Makarantun Jinya da unguzoma da sauran sassan lafiya, guda biyu da ke a cikin Garin Sakkwato Wadanda s**a hada da Gamji College of Nursing Sciences, da Kuma Al-huda College of Health Technology.

Tarukkan da akayi a Harabar makarantun sun samu halartar Mambobin Babban kwamitin da s**a hada da Shugaban Kwamitin da Mambobin shi, Shugabannin Makaratun da wadan da s**a Assasa Makarantun, dalibbai,Iyayen su da Maga isar su, Uwayen kasa,jamian Tsaro,Kungiyoyin Addinin Musulunci da sauran su.

A dukkan Makarantun an Rattaba hannu ga takardun yarjajjeniya tsakanin Kwamitin, Makarantun,Iyayen Dalibbai ,da Dalibban karkashin Jagorancin Lauyan Kwamitin Inda aka karanta Abubuwan da takardar ta kumsa ciki harda Alkawullan da Dalibban s**a yi na za su tsaya suyi karatun tsakanin da Allah batare da wasa ba, da sauran bayanai.

Haka Kuma an gabatar da Bangon katin Chakitin na kudin da aka biyawa Dalibban na Shekara ukku da zimmar kammala Karatun su cikin shekarrun. Shugaban Kwamitin ne Malam Muhammad Lawal Maidoki Sadaukin Sakkwato, da Sakataren kwamitin Hon. Sagir Attahiru Bafarawa sunyi bayanai na Ayukkan da kwamitin yayi na Bangarorin Bada Tallafin Abinci, Duba maras lafiya da basu magani kyauta, Duba maras lafiyar masu tabin hankali, da wasu da akayiwa Aiki.

Yanzu Haka ana Tantance wuraren da za'ayi Ayukkan gyara da Samar da Makabartu, Rijiyoyin Ruwa, Bohol, makarantu da sauran su da zaa soma badajimawa ba. sun Kuma yi bayanin yadda wannan tallafin yake bayan anzagaya cikin kananin Hukumomin 23 anyiwa Dalibbai jarabawar.

Sun Kuma yabawa Hukumomin Makarantun akan ba da na su Gudunmawar Kashi Hansin cikin Dari na miliyoyin da aka bada, sunyi kira ga dalibban da su yi kokari su yi karatun Dan kammala wa cikin Nasara kasancewar baza'a lamuncewa duk Wani sakacin rashin yin karatun ba.

Sun yabawa tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Dr Attahiru Dalhatu Bafarawa kan Wannan kokarin da yayi, sun kuma yabawa Gwamnatin Jihar Sokoto da majalisar mai Martaba Sarkin Musulmi akan kokarin da sukeyi na cigaban sha'anin Ilimi a Fadin jihar Sokoto, tare da godiya ga babban kwamitin da karamin kwamitin Ilimi da yayi dawainiyar ,tare da duk Mai hannu a cikin wannan lamarin.

A nasu jawaban wadan da ke da Makarantun, Sun yabawa Tsohon Gwamnan da tabbatar da cewa wannan aikin ya jima Yana yin shi.

Wasu da s**a zanta a gun sun hada da Uwayen, kasa, Jamian Tsaro, Ilimi,lafiya da kungiyoyin Addinin Musulunci.

A lokacin Taron an kaddamar da Rabawa Dalibbai Shaidar yar jajjjeniyar sanya hannun yin karatun da Bada Tallafin ga Wasu Dalibbai da maga isar su sunyi Godiya da Adduar Allah ya biya Wanda ya Bada Tallafin da duk Mai hannu a ciki.

Makarantar Gamji tana da Dalibbai 55 da Alhuda nada 53 da zasu karatun aikin Ji
jinya, Ungozoma da sauran sassan lafiya , baya da wasu da ke sassan daban daban a ciki da wajen jihar Sokoto.

Daga Mukhtar A Haliru TambuwalSokoto.

04/01/2025

Taron Manema Labarai Da Hon. Yusuf Dingyadi ya Jagoranta! Akan Matsalolin Nigeria.

12/09/2024

Shirin Kowa ya Debo da Zafi bakin sa zai Zo Muku Ranar Monday Mai zuwa!

28/08/2024

Sansanin Taurari

11/08/2024

Next project

11/03/2024

Kar Ka kalli dan Agajin nan Da Ya Tsinci Kudi ya Maisuwa Matsayin dan Izala ne, Ka dauke shi Musulmi, Kaima sai Kayi Murnar Wannan Kyakkyawan Abin da Yayi!
Please save us from issues of Sect and Ta’assubanci!

28/02/2024

By the current hardship, and catastrophic economic situation our nation has experiencing. I doubt if PBAT. has Intention to Rerun for his second tenure in 2027!!

Address


Telephone

+2349074564800

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sokoto Plain posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sokoto Plain:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share