Absu Hausa Reporters

  • Home
  • Absu Hausa Reporters

Absu Hausa Reporters Absu Hausa Reports news & information wannan shafi munyishi domin kawa ingantacce labari da Kuma talalace tallace na abubuwa dakala kala ko wanne iri sann

Ni mai hazaka ne, wadanda suke fatan na mutu ba za su tsira daga bala'i ba - ObasanjoTsohon shugaban kasa Olusegun Obasa...
28/11/2024

Ni mai hazaka ne, wadanda suke fatan na mutu ba za su tsira daga bala'i ba - Obasanjo

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya yi watsi da jita-jitar mutuwarsa.

Obasanjo ya yi magana ne a Osogbo a yayin kaddamar da tsohon titin Garage-Oke Fia, wanda gwamnan Osun, Ademola Adeleke ya sake ginawa.

Ya ce akwai rahotannin rasuwarsa a shafukan sada zumunta, inda ya ce masu son ya mutu ne ke yada jita-jitar.

"Wasu mutane ne s**a kira ni da sassafe, s**a ce in duba kafafen sada zumunta," in ji Obasanjo cikin harshen Yarbanci.

“Na yi mamaki lokacin da na ga jita-jitar da ake cewa na mutu a cikin dare."

Janar din mai ritaya ya ce nan take ya raba sakonnin ga iyalansa da makusantansa domin tabbatar musu da lafiyarsa.

“Waɗanda suke so na mutu, burinsu ke nan, amma har yanzu Allah ya raya ni. Amma masu irin wannan tunanin ba za su tsira daga bala'i da kansu ba," in ji shi.

Da dumi duminsa Yanzu haka Dantakarar Gwamnan jihar Kano karkashin inuwar jam'iyyar NNPP Engr Abba Kabir Yusif ya halarc...
30/08/2022

Da dumi duminsa

Yanzu haka Dantakarar Gwamnan jihar Kano karkashin inuwar jam'iyyar NNPP Engr Abba Kabir Yusif ya halarci kasuwar kantin kwari domin jajantawa Al'ummar kasuwar da ambaliyar ruwa ya shafa.

Sun Taru sun ha'da karfi da karfe duk domin bawa  kwankwaso matsala a zaben...Atiku Abubakar a Kano.Namadi sambo a Kano....
30/08/2022

Sun Taru sun ha'da karfi da karfe duk domin bawa kwankwaso matsala a zaben...

Atiku Abubakar a Kano.
Namadi sambo a Kano.
Gov Okowa a Kano.
Sule Lamido a Kano.
Makarfi a Kano.
Ibrahim shema a Kano.
Sanata Iyorchia Ayu a Kano.
Attahiru Bafarawa a Kano.
Rt Aminu Tambuwal a Kano.
Walid Jibrin a Kano.
Sanata Shehu Sani a Kano.
Gov Darius ishaku.
Sanata Dino Melaye.
Sanata Baba kaita.

Da daidai sauran manyan jiga-jigan jam'iyar PDP duk domin Yaki da Sanata kwankwaso shi ka'dai.

Kuma ku zuba Ido ku gani zaku ga irin jama'ar da kwankwaso zai Tara a Jihar Adamawa mahaifar Atiku a duk lokacin da zai ziyarci Jihar na tabbata sai ta ninka jama'ar da Atiku ya tara na zuwan sa jihar Kano.

Soyayyar dake Tsakanin talakawan Nageriya da kwankwaso Daga Allah ne Kuma idan kunji haushi kawai kuyi bindiga ku fashe mudai munce Nageriya sai Mai kishin Al'umma talakawa..

M Inuwa MH...

Zamu hukunta Ado Gwanja kan sakin wakar Casss da yayi domin haka ya zama izina ga masu yin irin wakokin da basu dace baC...
30/08/2022

Zamu hukunta Ado Gwanja kan sakin wakar Casss da yayi domin haka ya zama izina ga masu yin irin wakokin da basu dace ba

Cewar Afakallahu

LISSAFIN SIYASAR SADDAUNA.. DAGA SADEEQ GETSO..Wani lissafin siyasa na Malam Ibrahim Shekarau dana kasa ganewa shine, ya...
29/08/2022

LISSAFIN SIYASAR SADDAUNA.. DAGA SADEEQ GETSO..

Wani lissafin siyasa na Malam Ibrahim Shekarau dana kasa ganewa shine, yace rashin adalcin da NNPP ne tayi masa yasa zai bar jam'iyyar wanda da alama kuma PDP zai koma toni ina da wasu tambayoyi guda uku kacal dan Allah wanda yake da amsarsu ya bani ina jira.

Babban rashin adalcin da akayiwa shekarau a NNPP shine rashin bawa yaransa takara, wanda yace shi kadai aka bawa takara ba'a bawa yaransa ba.

TA FARKO: To tambayata itace yanzu da zai shiga PDP, kenan PDP zasu bashi takara su bawa yaransa tunda dai shine babban abinda yasa yabar NNPP ko kuwa ya za'ayi?

TA BIYU : Idan kuma maganar Atiku zaiyi masa alkawarin mukami idan yaci zabe ne. To mecece makomar shekarau idan Atiku baici zabe ba ?

TA UKU: Anya kuwa ko Atiku yaci zabe idan bai samu kuri'a masu tsoka a kano ba zai iya cikawa shekarau alkawarinsa ?

Hausawa dai sunce "abincin dake bakinka shine abinci bana kwano ba".

Da Dumi Duminta: INEC ta ja hankalin jamiyyar PDP akan kudirinta na rushe shugabancin jamiyyar PDP karkashin Hon. Shehu ...
29/08/2022

Da Dumi Duminta:

INEC ta ja hankalin jamiyyar PDP akan kudirinta na rushe shugabancin jamiyyar PDP karkashin Hon. Shehu wada sagagi inda ta bayyana mata cewa shine halastaccen shugaban jamiyyar bisa doka da order na babbar kotun kasa, dan haka shi da exco dinshi ta sani bisa doka.

KADAN DAGA  CIKIN GAYYATA DA KUMA TARON DANGIN DA AKAZO YIWA KWANKWASO KANOKowane Mutum Daga Cikin Bakin nan Da S**a Shi...
29/08/2022

KADAN DAGA CIKIN GAYYATA DA KUMA TARON DANGIN DA AKAZO YIWA KWANKWASO KANO

Kowane Mutum Daga Cikin Bakin nan Da S**a Shigo Kano Gurin Karbar Malam Ibrahim Shekarau Sai Da S**a Tarkato Magoya Bayansu kwansu Da Kwarkwatarsu Na Garinsu S**a Taho Dasu Kano

Jiya Mun Soma Ganin Nauyinsu Yau Kuma Bakin Mahalarta Taron Da S**a Shigo Kano Daga Sassan Nigeria Zasu Fito Kwansu Da Kwarkwatarsu Su Karasa Bayyana Mana Nauyinsu

Ga Kadan Daga Cikin Bakin Da S**azo Taron

ATIKU
Tambuwal
Namadi
Okowa
shugaban Jam'iyyar PDPna Ƙasa
Dr. Iyorchia Ayu,
Attahiru Ɗalhatu Bafarawa,
Barr. Ibrahim Shehu Shema CON, Sanata Ahmed Maƙarfi
Sule lamido
Alhaji Adamu Maina Waziri,
Dino Melaye,
Sanata Lea Maeba,
Sanata Ahmed Babba Kaita,
H.E. Mahadi Aliyu Gusau,
Sanata Abdul Ahmed Ningi,
Alhaji Mustapha Khabeeb Zannan Dutse,
Ahmed Dandija Misau,
Salisu Yusuf Majigiri,
Aminu Nuhu Jahun.
Tawagar Shehu Sagagi
Tawagar Gidan Gona
Tawagar Yen Qaulani

Amman Dukda Wannan Tawagar Zan Iya Rantsema Babu Mai Iya Kawowa ATIKU Mazaba Guda Daya Ranar Zaben Shugaban Kasa Na 2023

Allah Ya Taimaki Kwankwaso Akan Makiyansq Ameeen

Nuhu Dambazau

INNALILLAHI WAINNA ILAIHIRRAJU'UN Yanzu haka kenan daga daya daga cikin manyan manyan  kasuwannin jihar kano cikin garin...
29/08/2022

INNALILLAHI WAINNA ILAIHIRRAJU'UN

Yanzu haka kenan daga daya daga cikin manyan manyan kasuwannin jihar kano cikin garin kano kasuwar da ake siyar da kayan sawa, kasuwar kantin kwari,
Allah ya kiyaye wainna s**ai asara Allah ya mayar musu da abinda s**a rasa

Zuwa ga Maigirma Wazirin Adamawa, Alhaji Atiku Abubakar, Tare da girmamawa da maraba da zuwa jahar Kano a yinkurinka na ...
29/08/2022

Zuwa ga Maigirma Wazirin Adamawa, Alhaji Atiku Abubakar,

Tare da girmamawa da maraba da zuwa jahar Kano a yinkurinka na kara samun magoya baya domin tunkarar zaben da ke zuwa na 2023. Na kasance mai cike da fatan ku hada kai da Sen. Rabiu Kwankwaso domin yin aiki tare, kuma har gobe ban sauka daga kan wannan tunanin nawa ba tunda dai a siyasar Najeriya komai mai yiwuwa ne. Na san ka fi ni sanin tasirin Kwankwaso a siyasar Najeriya tunda kuwa ko babu komai kasan kun yi takarar neman tikitin jam'iyar APC domin zaben 2015, inda shugaba Buhari ya zo na daya, Kwankwaso ya zo na biyu, Allah Ya taimaki Waziri, kai kuma ka zo na uku. Gaskiyar ita ce ka na bukatar Kwankwaso, shi ma Kwankwaso ya na bukatarka. Kash! Sai dai wadanda ke kewaye da kai musamman wandanda su ke daga arewa ba za su bari alakarka da Kwankwaso ta yi tasiri ba domin yadda su ke jin haushinshi sabo da farinjinin magoyabaya da Allah ya yi mishi fiye da na su. Ina nan, zan ci gaba da addu'ar Allah Ya hada kanku da Kwankwaso kafin zaben 2023.
Haka kuma, na samu labarin cewar zuwanka Kano na da alaka da karbar Malam Shekarau domin dawowa PDP. Toh, shima wannan wani cigabane a wannan takara ta ka, sai dai kada ko da wasa ka yi tunanin Shakarau zai iya yi maka wani tasiri da al'umar Kano ba za su yi maka ba ko babushi domin Shekarau fa ya tsaya zaben shugabankasa a 2011 a tutar ANPP amma kaso 19% na kuri'ar Kano ya samu, kai kuma da ka tsaya zaben 2019 ka samu kaso 21% na kuri'ar da aka kada ta shugabankasa a Kano.

Haka kuma kar mu manta cewar idan ana batun farinjini da magoya baya a Kano, Arewa da Najeriya, ko kusa ba za a hada Rabiu Kwankwaso da Shekarau ba duk kuwa da cewa su na da abubuwa da su ka yi k**a da juna kasancewarsu tsoffin gwamnoni har karo biyu a Kano, tsoffin ministicin Najeriya kuma kowannansu ya yi sanata. Misali, Shekarau ya zama sanata a 2019 da kuri'a 506,271 amma Kwankwaso ya zama sanata da kuri'a 758, 383 a 2015. Wannan kuri'ar ta Kwankwaso ta ma zarta zarta kuri'a 526,310.

Daga Comr  Auwal Soja Sani MainaggeYANZU-YANZU "Na Lura cewa da Arewa ake fada, sabida haka na hakura da takarata na San...
29/08/2022

Daga Comr Auwal Soja Sani Mainagge

YANZU-YANZU "Na Lura cewa da Arewa ake fada, sabida haka na hakura da takarata na Sanata a NNPP na dawo PDP domin marawa Atiku Abubakar baya"

~ Mal. Ibrahim Shekarau

Cewar sardaunan Kano yamanta sanda ya guji Gen buhari ya koma wajen Jonathan abin duba anan ya yaki arewa kuma yaguji musulmi Dan uwansa kuma aka kadasu zabe yakasa azimi yadawo akai gwamnati dashi lallai sardauna maganganinka sun soma Karo da juna Kar aymaka wai wa ye a gidan redio Amma kutayani nazari ko nine banfahimtaba?

SHIMA WANI MASOYIN MALAM IBRAHIM SHEKARAU MAI SUNA MUBARAK GEZAWA YA BAYYANA A SHAFINSA CEWAR YANANAN A JAM'IYYAR NNPP K...
28/08/2022

SHIMA WANI MASOYIN MALAM IBRAHIM SHEKARAU MAI SUNA MUBARAK GEZAWA YA BAYYANA A SHAFINSA CEWAR YANANAN A JAM'IYYAR NNPP KAMAR HAKA

I’m disappointed in Mallan Ibrahim Shekarau’s decision to dump the NNPP. I’ve been a staunch supporter of him since 2003. I guess “I have to say bye bye oo” Ibrahim Adam and Bello Nuhu Bello a samo mun form din Jam’iyya in yi rijista officially.

YANZU-YANZU: Atiku ya sauka a Kano domin karɓar Shekarau zuwa PDPTsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma dan takarar shugab...
28/08/2022

YANZU-YANZU: Atiku ya sauka a Kano domin karɓar Shekarau zuwa PDP

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma dan takarar shugabancin ƙasa na jam'iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar ya isa Kano.

Atiku, wanda ya samu rakiyar abokin takararsa Gwamna Ifeanyi Okowa, shugaban jam'iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu ya tare shi, ya je Kano domin tarbar tsohon gwamnan jihar, Ibrahim Shekarau zuwa jam'iyyar PDP.

Atiku ya bayyana zuwan sa ne a wani sako da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta a yau Lahadi.

Ya ce: “Na zo cibiyar kasuwanci ta jihar Kano. Kwanaki masu zuwa za su zama na gwagwarmaya.AA ," in ji Atiku.

Address


Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Telephone

+2349035025922

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Absu Hausa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Absu Hausa Reporters:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share