Adamsy Gimbiya News24

  • Home
  • Adamsy Gimbiya News24

Adamsy Gimbiya News24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Adamsy Gimbiya News24, Newspaper, .

Wasu Samari Sun Yi Wa Karamar Yarinya Fyade----------------------------------------------------Ana zargin wasu bara gari...
18/07/2025

Wasu Samari Sun Yi Wa Karamar Yarinya Fyade
----------------------------------------------------
Ana zargin wasu bara garin samari da har wayau ba a san ko su waye ba da yi wa 'yar kankanuwar yarinya fiyade bayan sun jata zuwa wani shago da ke lungu sannan s**a afkamata.

Lamarin ya faru ne a jiya Talata a jihar Ondo da ke Yammacin kasar nan.

Wasu jami'an 'yan sanda ne aka gani s**a dauko yarinyar jina-jina zuwa wani asibiti inda daga bisani s**a yi tafiyarsu ba tare da ma sun bari an sansu ba domin ba sa son su yi wani abu akan lamarin.

Sakamakon Bincike Likitoci da s**a gudanar sun bayyana cewa ga dukkan alamu duka samarin ne s**a yi wa yarinyar fyade domin ba mutum daya bane wanda hakan ya jawo sun buda mata farjinta sossai.

Har yanzu dai ba a san wadan da s**a yi wannan ta'asa ga wannan yarinyar ba.

13/07/2025

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana alhini, ya kuma umarci mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya tafi London don dawo da gawar Buhari zuwa Najeriya .

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN Allah Ya Yiwa Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Rasuwa.
13/07/2025

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN
Allah Ya Yiwa Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Rasuwa.

Kotun Minna ta yanke hukuncin daurin rai da rai ga yarinya mai shekara 16 saboda kisan malama a FUT Minna yayin wani fas...
13/07/2025

Kotun Minna ta yanke hukuncin daurin rai da rai ga yarinya mai shekara 16 saboda kisan malama a FUT Minna yayin wani fashi da makami – lokacin tana da shekara 14.

Wata yarinya mai shekara 16 mai suna Joy Afekafe ta samu hukuncin daurin rai da rai bayan kotu ta same ta da laifin kisan kai wanda ake hukunta shi bisa sashe na 221 na dokar hukunta laifuka (Penal Code).

An yanke mata wannan hukunci ne saboda kashe Dr. Mrs Funmilayo Sherifat Adefolalu, malamar jami’a a Jami’ar Fasaha ta Tarayya Minna (FUT Minna), a ranar 28 ga Oktoba, 2023 a gidanta dake Gbaiko, Minna, Jihar Neja.

Mai shari’a Mohammed Adishetu Mohammed na Kotun Babban Birni Minna mai lamba 4 ne ya jagoranci shari’ar, inda ya bayyana cewa masu gabatar da kara sun tabbatar da laifin fashi da makami da kuma kisan kai da gangan a kan Joy.

A cewar Lauya mai gabatar da kara daga ofishin Antoni Janar na jihar Neja, laifuffukan guda biyu – fashi da makami da kisan kai – suna karkashin sashe na 221 da 298 na dokar Penal Code.

Joy Afekafe ta fara aiki a matsayin yar aikin gida ga marigayiya Dr. Adefolalu daga ranar 2 ga Oktoba, 2023, bayan Pastor Ojo Peters daga coci mai suna Voice of Mercy Church a Minna ya gabatar da ita. Wannan coci ce su Joy da mahaifiyarta da marigayiyar ke halarta.

Bayan ta koma gidan, Joy ta fara sata wasu kadarori da kudin kasashen waje, wanda hakan yasa Dr. Adefolalu ta kore ta daga aiki.

Bayan kora, Joy ta hada kai da wasu abokanta guda biyu – DJ Wallex da DJ Smart – domin daukar fansa. A cikin bayaninta ga 'yan sandan SCIID (Sashin bincike na musamman a Neja), Joy ta bayyana yadda abokanta s**a yi wa malamar yankan wuka sau da dama.

Yayin da Dr. Adefolalu ke kokarin kare kanta da tabarma, s**a karbe tabarmar s**a doke kanta da ita, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarta. Daga nan s**a kwashe wayoyi biyu, kwamfuta da kudi na waje daga dakinta.

Mai shari’a Mohammed ya bayyana cewa bayan duba hujjoji da shaidu, an tabbatar da cewa Joy da abokanta (wanda s**a gudu har yanzu) su s**a kashe Dr. Adefolalu da gangan.

Sai dai saboda Joy tana da shekara 14 a lokacin kisan, dokar ta haramta hukuncin kisa ga duk wanda bai kai shekara 18 ba a lokacin aikata laifi. Don haka kotun ta yanke mata hukuncin daurin rai da rai a cibiyar gyara halin yara saboda kisan kai, sannan kuma shekara 10 saboda fashi da makami.

Lura: Wannan hukunci na daga cikin matakan hana aikata laifi da kare rayuwar al’umma musamman na masu rauni kamar mata da yara.

Wani matashin Dan Siyasa daga Jahar Katsina, AMB Umar Salisu Rimaye yaje har garin Abeokuta, ogun state domin Neman tari...
05/07/2025

Wani matashin Dan Siyasa daga Jahar Katsina, AMB Umar Salisu Rimaye yaje har garin Abeokuta, ogun state domin Neman tarihin Olusegun Obasonjo.

AMB Umar Salisu Rimaye ya bayyana obasonjo a matsayin shugaba na gari Wanda tarihin shi bazai taba gushewa ba.

Matashin dan siyasar ya kuma bukaci matasan Nigeria da su rinka ziyarar libraries din magabatan mu domin ganin irin ayyukan alkhairin da s**a yi a nigeria kuma suyi koyi da su.

Yau Shekaru (118) da Kirkiro Kafi Zabo (Ajino Moto)A Rana Mai kamar ta yau 25 Ga Watan yuli 1908, Kikunae ikeda, Ya kafa...
26/06/2025

Yau Shekaru (118) da Kirkiro Kafi Zabo (Ajino Moto)

A Rana Mai kamar ta yau 25 Ga Watan yuli 1908, Kikunae ikeda, Ya kafa kamfanin Ajinomoto (Kafi Zabo) a Jami'ar Imperial ta Tokyo, shi ne ya gano wani muhimmin sinadari a cikin miya mai dauke da sinadarin monosodium glutamate (MSG), kuma ya ba da izinin yin amfani da shi. Glutamic acid ana samunsa ta halitta a cikin tumatir, inabi, cuku, kaza, da sauran abinci. An fara kirkirarsa ne a shekara ta 1908 ta Hannun Masanin kimiyyar halittu na Japan Kikunae Ikeda.

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Ita Da Jaririn Da Ta Haifa Duk Sun RasuAllah Ya yi wa Nana Fiddausi Dahiru rasuwa a...
15/06/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Ita Da Jaririn Da Ta Haifa Duk Sun Rasu

Allah Ya yi wa Nana Fiddausi Dahiru rasuwa a garin Burra dake karamar hukumar Ningi a jihar Bauchi.

Ta rasu ta dalilin haihuwa bayan an yi mata CS, inda ita da dan da ta haifa Allah Ya karbi rayuwarsu.

Muna barar addu'o'inku. Allah Ya jikanta.

Daga Comr Mu'azu Zubairu Burra

Wani soja ya rasa ransa a hannun mai ƙwacen waya a KadunaWani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan da ya nemi ya miƙ...
09/06/2025

Wani soja ya rasa ransa a hannun mai ƙwacen waya a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan da ya nemi ya miƙa masa wayar da ke hannunsa.

Wata sanarwa da rundunar sojin Div 1 da ke Kaduna ta fitar ta ce Lt Commodre M Buba da ke kwas na shiga layin manyan sojoji ya samu fanco a tayar motarsa abin da ya tilasta masa tsayawa a daidai gadar sama ta Kawo da ke Kaduna, inda fitowarsa ke dawuya sai wani ya zo ya same shi ya nemi ya ba shi wayarsa.

Sai sojan ya nemi sanin dalilin bayar da wayar abin da ya sa mutumin ya fitar da wuƙa ya caka masa a ƙirji.

Wani ɗn sintiri ya yi ƙoƙarin ceton sojan amma shi ma mutum ya daɓa masa wuƙar a hannunsa.

An kai Lt Commodore asibitin Manalal amma kuma rai ya yi halinsa.

Sai dai kuma mutanen da ke kusa da wurin da abin ya faru sun yi wa makashin tara-tara inda s**a hallaka shi shi ma.

DA DUMI DUMI: Duk Waɗanda S**a Yi Sallah jiya Juma'a, Ba Su Yi Sallah Ba, Waɗanda S**a Yi Yanka jiya, Balangu S**a Ci, S...
07/06/2025

DA DUMI DUMI: Duk Waɗanda S**a Yi Sallah jiya Juma'a, Ba Su Yi Sallah Ba, Waɗanda S**a Yi Yanka jiya, Balangu S**a Ci, Sallah Da Yanka Sai yau Ranar Asabar, inji Sheikh El-Zakzaky

Tushen Labari: Wakiliya

AMFANIN GANYEN DALBEJIYA GUDA 16 A JIKIN DAN ADAMGa wasu amfanin dalbejiya a jikin mutum: 1. Ganyen dalbejiya na kare mu...
06/06/2025

AMFANIN GANYEN DALBEJIYA GUDA 16 A JIKIN DAN ADAM

Ga wasu amfanin dalbejiya a jikin mutum:

1. Ganyen dalbejiya na kare mutum daga kamuwa da cutar bugawar zuciya, musamman idan aka dafa ganyen ana shan ruwan kamar shayi.

2. Yana taimakawa wajen tacewa da tsaftace jinin jikin mutum.

3. Ganyen na maganin cutar zazzabin cizon sauro da typhoid.

4. Yana maganin cutar ciwon ciki, musamman idan mutum ya murde saboda wani abinci da aka ci.

5. Ganyen dalbejiya da man shi na gyara fatar jikin mutum.

𝗔𝗗𝗔𝗠𝗦𝗬 𝗧𝗥𝗔𝗗𝗜𝗧𝗜𝗢𝗡𝗔𝗟 𝗠𝗘𝗗𝗜𝗖𝗜𝗡𝗘
𝑊ℎ𝑎𝑡𝑠𝐴𝑝𝑝/Calls
08036066553, 08051115383
08093651535.
🄲🄾🄼🄼🄴🄽🅃, 🅂🄷🄰🅁🄴, 🄻🄸🄺🄴,.

6. Ganyen na maganain saiko, amosanin kai da kuma sa tsawon gashin kai.

7. Ana iya amfani da man dalbejiya a matsayin dabarar bada tazarar iyali.

8. Ganyen na kawar da cutar daji, musamman na nono da ‘ya’yan maraina.

9. Ganyen na maganin cutar gyambon ciki da rauni a jiki.

10. Yana rage kiba a jiki musamman ga masu fama da ita.

𝗔𝗗𝗔𝗠𝗦𝗬 𝗧𝗥𝗔𝗗𝗜𝗧𝗜𝗢𝗡𝗔𝗟 𝗠𝗘𝗗𝗜𝗖𝗜𝗡𝗘
𝑊ℎ𝑎𝑡𝑠𝐴𝑝𝑝/Calls
08036066553, 08051115383
08093651535.
🄲🄾🄼🄼🄴🄽🅃, 🅂🄷🄰🅁🄴, 🄻🄸🄺🄴,.

11. Yana warkar da ciwon gabobi da ciwon kai.

12. Yana kare mutum daga kamuwa da cutukan da ake samu ta hanyar yin jima’ai.

13. Yana warkar da cutar kuturta.

14. Yana maganin ciwon ido.

15. Yana maganin guba da ake samu daga jikin dabba kamar cizon cinnaka, maciji da sauransu.

16. Ganyen na maganin kwari musamman wadanda ke lalata amfanin gona.

𝗔𝗗𝗔𝗠𝗦𝗬 𝗧𝗥𝗔𝗗𝗜𝗧𝗜𝗢𝗡𝗔𝗟 𝗠𝗘𝗗𝗜𝗖𝗜𝗡𝗘
𝑊ℎ𝑎𝑡𝑠𝐴𝑝𝑝/Calls
08036066553, 08051115383
08093651535.
🄲🄾🄼🄼🄴🄽🅃, 🅂🄷🄰🅁🄴, 🄻🄸🄺🄴,.

A shekarar da wasu daga cikin jaruman kannywood s**a shigo kannywood     kamin ka karyata kayi bincike  #
24/05/2025

A shekarar da wasu daga cikin jaruman kannywood s**a shigo kannywood kamin ka karyata kayi bincike #

Wata baturiya ta rasa kazar da tafi so har bikin mutuwa tayi Mata. Kuma tace ta shiga mawuyacin hali akan haka.
22/05/2025

Wata baturiya ta rasa kazar da tafi so har bikin mutuwa tayi Mata.

Kuma tace ta shiga mawuyacin hali akan haka.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adamsy Gimbiya News24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share