The Daily Reality Hausa

  • Home
  • The Daily Reality Hausa

The Daily Reality Hausa Jaridar Hausa = Gaskiya Tsantsa www.thedailyrealityng.com
[email protected]

Kano fa tana da damar cigaba sosaiDaga Dr. Fahad Ibrahim Danladi Komai da jihar Kano take buƙata ta haɓaka tattalin arzi...
07/06/2025

Kano fa tana da damar cigaba sosai

Daga Dr. Fahad Ibrahim Danladi

Komai da jihar Kano take buƙata ta haɓaka tattalin arziƙinta, an yi ko an kafa ɗanba. Kawai abin da ake buƙata a yanzu shi ne haɗin kan gwamnatin Kano, da wakilan federal a Kano k**ar su Ganduje, Barau da sauransu.

Akwai cargo train, jirgin ƙasa mai ɗauko kwantena daga Lagos zuwa tashar Dala Inland Dry Port Kano, har ya fara kawo kaya amma kaɗan, kuma na ji shiru kwana biyu. Idan su Barau s**a mayar da hankali, hakan na nufin idan na siyo kaya a China ko US, sai na zo Kano sannan za a buɗe container. Mutane dubu nawa ne za su yi arziƙi idan wannan aiki ya ɗauki saiti?

Uwa uba manomanmu. Idanfa kwantena ta zo daga Lagos, ba fa haka za ta koma ba, lodin kayan gona za a yi mata zuwa kudu da ƙasashen waje. Babu maganar kayan miya sun ruɓe a hanya ko wasu marasa mutunci sun ƙona su. Harkar noma za ta yi haɓakar da ba ta taɓa yi ba.

AKK pipeline, bututun gas ne da zai zo har Kano, tuni aikinsa ya yi nisa. Idan wannan aiki ya kammala, gwamnatin jiha ita ma ta shigo wajen kai connection ɗinsa industrial zone, hakan na nufin kamfanoninmu za su farfaɗo, sabbi kuma za su shigo. Dubbunan matasa ne za su samu ayyuka masu tsoka.

Ana titunan mota da jirgin ƙasa a Kano ta yadda masu siyayya za su samu sauƙin zuwa Kano hada-hada. Ita kuma gwamnatin Kano k**ata ya yi a ce ta mayar da hankali wajen tsaftace t**i da zirga-zirga a Kano, ta yadda ƴan kasuwa za su shigo su fita salin alin.

Waɗannan da ma wasu ɗinbun ayyukan na haɓaka tattalin arziƙi ba za su yiwu ba, sai ƴan siyasarmu na Kano sun ajiye baƙar siyasar cibaya da ke tsakaninsu zuwa zaɓe, sun mayar da hankali wajen cigaban jihar. Amma dai sam bai k**ata a ce ana irin wannan talaucin ba, alhalin muna kwance a kan tarin dukiya.


Yadda ambaliyar ruwa ta yi sanadiyyar rasuwar iyalai rankatakafDaga Kabir UsmanAmbaliyar ruwan da a yanzu ta yi sanadiyy...
01/06/2025

Yadda ambaliyar ruwa ta yi sanadiyyar rasuwar iyalai rankatakaf

Daga Kabir Usman

Ambaliyar ruwan da a yanzu ta yi sanadiyyar mutane da yawa inda a yanzu suke buƙatar agajin gaggawa da addu'o'in neman taimako daga Allah.

Ya zuwa yanzu dai rahitanni suna bayyana kusan mutane ɗari da sha biyar (115) sun mutu a garin Mokwa jihar Naija a sak**akon ambaliyar ruwa mai ƙarfi.

A wannan hoto, iyalin wani gida guda ne, wanda aka bayyana da gidan Alhaji Umar, waɗanda duk sun mutu a ambaliyar ruwan, gidaje ba adadi sun ruguje, dukiya kam ba a maganarta

Allah ya yi musu rahama ya sa aljanna ce makomarsu, amin.


Fad'uwar Jumu'ah ko Azahar?Daga Shafin Malam Mu'awiyah Ja'afar Hussain 1.Wanda ya halarci sallar Idi a ranar Jumu'a to i...
01/06/2025

Fad'uwar Jumu'ah ko Azahar?

Daga Shafin Malam Mu'awiyah Ja'afar Hussain

1.Wanda ya halarci sallar Idi a ranar Jumu'a to in bai je sallar Jumu'a ba ba shi da laifi, amma dole ne ya sallaci sallar Azahar.

2.Wanda bai sallaci Idi ba to dolensa ya sallaci sallar Jumu'a.

3.Sallatarsu gaba d'aya babu laifi.

4.Magana kan fad'uwa Jumu'ah da Azahar ga wanda ya sallaci Idi magana ce mai rauni, kuma gamsasshen fi'khu yana sa'ba mata.

5.Sallolin da Allah ya farlantawa bayinsa guda biyar ne a dare da yini, k**ar yadda Annabi s.a.w ya sanar da wancan Balaraben 'kauyen, inda ya ce da shi:
خمس صلوات في اليوم والليلة

In Azahar ba wajiba ba ce to ya zama sallolin farilla na wajibi a wannan yinin guda hud'u ne, kuma babu dalili sarihi da yake nuna a wannan yinin salloli hud'u ne wajibai, sai dai tawili mara tushe.

6.Cewar wai Abdullahi Ibn Azzubair ya koma gida bai sallaci Jumu'a ba ba ya nufin bai sallaci Azahar a gida ba, kuma su wad'anda s**a rawaito hadisin ma ba su fahimci hakan ba, shi ya sa s**a yi sallar Azahar a d'aid'aikunsu a rarrabe, kuma da aka sanar da Ibnu Abbas ya ce ya dace ya Sunna .

فعن عطاء بن أبي رباح قال: صلى بنا ابن الزبير في يوم عيد في يوم جمعة أول النهار ثم رحنا إلى الجمعة فلم يخرج إلينا، فصلينا وحداناً، وكان ابن عباس بالطائف فلما قدمنا ذكرنا ذلك له، فقال : (أصاب السنة). رواه أبو داود.

7.Daga cikin manufofi da manufar sallar Jumu'ah akwai taron jama'ar Musulmi wanda an sameta a sallar Idi, dan haka wannan taron Idin ya wadatar da na Jumu'ah, shi ya sa Jumu'ah ta sauka, amma sallar Azahar ba ta fad'i ba, in kuma ta fad'i ina nassi sarihi da ya nuna hakan?

8.Ba ma shakka ko d'ard'ar in Allah ya soke wata sallar, za mu kar'ba hannu bibbiyu , tun da shi ya far man ta a asali, amma sauke wajibcinta ba tare da tabbataccen dalili ba kuskure ne.

9.Sallar Azahar ita ce asali a wannan bigiren, ita aka farlanta a daren Isra'i, Jumu'a kuma aka farlanta ta daga baya; shi ya sa ma wanda ya rasa Jumu'a to dolenshi ya zo da Azahar a gurbinta, haka nan wad'anda aka sauke musu farlancin Jumu'a ba a sauke musu Azahar ba; k**ar su mata, matafiyi. Dan haka a nan ma wanda bai je Jumu'a ba dole ya maye gurbinta da Azahar;(kada wani ya ce na yi 'kiyasi a mahallin nassi, yo ai babu nassin).

10. Imam As-San'ani yake cewa:

قال العلامة الصنعاني رحمه الله في سبل السلام مناقشا نسبة القول بسقوط الظهر إذا اجتمع جمعة وعيد إلى ابن الزبير رضي الله عنهما ما عبارته: قلت: ولا يخفى أن عطاء أخبر أنه لم يخرج ابن الزبير لصلاة الجمعة وليس ذلك بنص قاطع أنه لم يصل الظهر في منزله، فالجزم بأن مذهب ابن الزبير سقوط صلاة الظهر في يوم الجمعة يكون عيدا على من صلى صلاة العيد لهذه الرواية غير صحيح لاحتمال أنه صلى الظهر في منزله بل في قول عطاء إنهم صلوا وحدانا أي الظهر ما يشعر بأنه لا قائل بسقوطه، ولا يقال إن مراده صلاة الجمعة وحدانا فإنها لا تصح إلا جماعة إجماعا.

ثم القول بأن الأصل في يوم الجمعة صلاة الجمعة والظهر بدل عنها قول مرجوح بل الظهر هو الفرض الأصلي المفروض ليلة الإسراء والجمعة متأخرة فرضها، ثم إذا فاتت وجب الظهر إجماعا فهي البدل عنه، وقد حققناه في رسالة مستقلة. انتهى.

Allah ya sa mu dace, amin


Hoto: shin kun san ko shirin me ake yi?
30/05/2025

Hoto: shin kun san ko shirin me ake yi?


Godiya da jinjina daga  🎉 Sadiq Ameenu Danminau, Usman Iliyasu Abdullahi, Idris Shafiu Aliyu, Shamsudeen Hassan
30/05/2025

Godiya da jinjina daga 🎉 Sadiq Ameenu Danminau, Usman Iliyasu Abdullahi, Idris Shafiu Aliyu, Shamsudeen Hassan

Sheikh Daurawa da Malam Ashaka: an samu tattaunawa da fahimtar junaA wani zama da Malam Aisar Fagge ya jagoranta, Sheikh...
30/05/2025

Sheikh Daurawa da Malam Ashaka: an samu tattaunawa da fahimtar juna

A wani zama da Malam Aisar Fagge ya jagoranta, Sheikh Daurawa da Malam Adam Ashaka sun tattauna kuma sun yafi juna a kan maganganu, wadanda s**a faru a sak**akon ziyarar da Malam Ashaka ya kawo domin ganin Malam, kuma aka yi rashin sa'a bai samu ganin Malam din ba.

Dukkanin Malaman biyu sun yafi juna kuma sun tabbatar da cewa za su ci gaba da gudanar da ayyukan da'awa tare.


Hukumomin Saudiyya sun Hana Dr. Gumi shiga kasar domin ibadar aikin HajjiDaga Mukhtar IbrahimA yau ne hukumomi a kasar S...
26/05/2025

Hukumomin Saudiyya sun Hana Dr. Gumi shiga kasar domin ibadar aikin Hajji

Daga Mukhtar Ibrahim

A yau ne hukumomi a kasar Saudiyya s**a hana babban malamin addinin Musulunci Dr. Gumi shiga kasar domin aiwatar da ibadar aikin Hajji.

Hakan dai yana kunshe a sanarwar da shi Dr. Gumin ya yada a shafinsa na fesbuk.

Sai dai tuni jama'a suke ta bayyana ra'ayoyinsu, inda wasu suke ganin matakin da kasar ta dauka bai dace ba, wasu kuma suke bayyana cewa hakam ya yi daidai.

Malam Umar Mansur, ya bayyana a shafinsa cewa; "Ba gaskiya ba ne cewa dalilin case din AbdulMutallib ne Saudi ta hana Dr. Gumi Shiga Saudiyya don sauke farali, domin Dr. ya sake Shiga Saudi yayi Umura a shekarar 2020 tareda limamin masallacin Sultan Bello Dr. Muhammad Sulaiman, wanda hakan ke nuna an rigaya an cire sunanshi daga cikin blacklist na wadanda aka hana Shiga kasar ko dawowa. Ba wani dalili da zai rage sai wancan batu da mu ka yi ishara da shi na cewa kawai dalilin siyasa ne ba wani abu ba, ko da kuwa masu kokarin kare hakan sun dage.

Kuma fa wannan ba wani sabon Abu ba ne ga wadanda su ka san tarihin Saudiyya na hana Yan adawar siyasa aikin hajji, domin akwai da yawa-yawan malamai da kasar ta hana aikin Hajji daga kasashe daban-daban saboda wannan dalili, cikin wadanda zan iya tunawa akwai Muftin Libya Sheikh Sadiq Algiryani, akwai Malamin tarihin nan Sheikh Ali Sallabi, akwai Mufakkirin Tunusia Dr. Rashid Al-Gannushi, da na Kuwait Dr. Tarikh Suwaidan, da Dr. hamid Al-Aly na Kuwait, da list Mai tsayi da ba zai kare ba.

A kasa ga hoton Dr. Tareda Dr. Muhd Sulaiman da aka dauke su a shekarar 2020 a yayin aikin ibadar Umura."


Yara fa suna ta tarandin!Daga Dr. Muhammad Sulaiman AbdullahiTrending = kalmar Ingilishi da take nuna "tashe" ko lokacin...
25/05/2025

Yara fa suna ta tarandin!

Daga Dr. Muhammad Sulaiman Abdullahi

Trending = kalmar Ingilishi da take nuna "tashe" ko lokacin abu, wato abin da ake yayi, musamman a soshiyal midiya.
Tarandin = kalmar Hausa da za ta iya ɗaukar ma'anoni k**ar haka:
1) Tashen hauka/haukacewa
2) Rashin mafaɗi
3) Rashin basira
4) Rashin jajirtacciyar hukuma mai hukunta lalatattu

Yanzu don Allah in ba hauka da rashin hukunci ba, ta yaya mutum zai zo gidan mai ya ɗauki mazubin fetur ya zuba a jikinsa, duk ana kallonsa, har ma ana ɗauka a waya, wai don a yi HAUKA/TARANDIN.

A lokacin da aka ce an biya wa yaron nan, Kabiru 2pac, Makka, a sak**akon bulbula gawayi da ya dinga yi a jikinsa, na tausaya masa, kuma na taya shi murna, amma da ni kwastoman Alajin da ya biya masa Makkan ne, to da daga ranar na daina kasuwanci da shi, don na san ba shi da kyakkyawar manufa a rayuwa.

A Musulunce ma ya k**ata a dinga zane irin waɗannan sakarkarun ko kuma a ɗauki wani matakin ladabtarwar da zai hana kowa haukawacewa.

Kuma in ni ne mai gidan man nan, tabbas wani ko wasu za su iya rasa aikinsu. Domin wannan jefa rayuwar al'umma ne a cikin garari a bisa hauka da ganganci da rashin basira!


24/05/2025

Opay 'ya'yan arziki amma hukumomi sun hana

Daga Ibrahiym A. El-Caleel

Opay ɗinnan kamfanin kasuwa ne. Sun buɗe abinsu, ana samun sauƙi, komai lafiya lau. Ba sa charges, su cire maka kuɗi saboda harkar transfer. Kusan komai free suke yi, yadda ka san za ka kashe kuɗin da gyake aljihun wandonka!

Amma gwamnatin Najeriya tayi uwa, tayi makarɓiya tace Opay basu isa ba! Tilas su fara charges k**ar sauran bankuna. Dole a fara zaftare ₦50 da sunaye iri-iri. Don haka yanzu Opay sun bi dole.

Baƙin rai iyakat baƙin rai. Hassada iya hassada. Alaƙar da ke tsakaninmu da mutanen nan kenan. Duk inda wani sauƙi yake, to sai sun toshe shi. Kai kuma idan lokacin zaɓe yayi, idan aka ce ka natsu ka nuna fushinka da ƴancin ƙuri'arka, sai ka ƙi. Sai ka nuna kai ka san daɗin taliya, ka san zaƙin Maggi.

Ɗanlami, dole fa jikinka ne za ya faɗa maka. Hausawa ne s**a ce wai shi jan biro yana maganin daƙiƙin yaro. Don haka Ɗanlami ba ka da zaɓi fa. Imma dai ka yi hankali nan da shekaru 10, ko kuma ka yi hankali nan da shekaru 50 bayan ka tsufa. Amma dai dole za ka yi hankali, ko kana so ko ba ka so.


19/05/2025

Wasu daga cikin alhazan Najeriya


A mintuna 5 an kashe mutane 50 a GazaDaga shafin Malam Abba LawanDa asuba aka jefa bam a wani gida da ke kusa da mu. Yaw...
19/05/2025

A mintuna 5 an kashe mutane 50 a Gaza

Daga shafin Malam Abba Lawan

Da asuba aka jefa bam a wani gida da ke kusa da mu. Yawancin mutanen cikin gidan sun mutu, sai karar ihun yara da mata daga ƙarƙashin gine-ginen da s**a rushe. Makwabta s**a fito da gaggawa don ceton su. Na yi saurin fita domin taimakawa, sai babbar ’yar uwata ta k**a ni tace: “ Ba mu da kowa sai kai!”

Bayan dakika 30, wani roka ya sake faɗowa kan gidan da aka fara kai wa hari, ya kashe duka waɗanda suke ƙoƙarin ceto. Da ina tare da su, da na mutu.

Bayan minti biyu, gidan da ke kusa da wancan aka buga masa bam – duka mutanen ciki sun mutu.
Bayan minti guda, aka buga gidan da ke gaba dasu su ma.

Mutane guda 50 daga cikin makwabta na – waɗanda na sani da sunayensu – aka kashe a gaban idona cikin minti biyar.

Hamza Musɗafa daga Gaza.


Ha'incin talaka a sana'ar cittaDaga Khadija MuhammadMasu sana'ar sayar da citta sun samo wani sabon wulakanci, wani sabo...
16/05/2025

Ha'incin talaka a sana'ar citta

Daga Khadija Muhammad

Masu sana'ar sayar da citta sun samo wani sabon wulakanci, wani sabon salon ha'inci, na yin algus din citta da bawon doya.

Kamar yadda wata baiwar Allah ta wallafa a shafinta na Fesbuk, Hajiya Naima Danhakimi ta bayyana yadda aka cuce ta a kasuwar Kurmi ta Kano. Ta ce ta sayi citta, amma bayan ta isa gida domin yin abin da za ta yi, sai ta ga fiye da rabin abin da aka ba ta, busasshen bawon doya ne.

Wai ina talaka zai sa kansa ne?


Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when The Daily Reality Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to The Daily Reality Hausa:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share