Yerima shettima Support Group

  • Home
  • Yerima shettima Support Group

Yerima shettima Support Group Yerima Usman Shettima is the National President of Arewa Youth Consultative Forum.

“On this historic day, I, Yerima Usman Shettima, extend warm felicitations to all Nigerians as we mark another Independe...
01/10/2025

“On this historic day, I, Yerima Usman Shettima, extend warm felicitations to all Nigerians as we mark another Independence anniversary. Our beloved nation has come a long way through sacrifice, resilience, and the enduring will of its people. As we celebrate, let us adopt peace, tranquility, and harmony as guiding principles in our national life. Only through unity and shared commitment can we consolidate democracy and secure a prosperous future for generations to come. Happy Independence Day, Nigeria!”

“Fellow Nigerians, today we celebrate our Independence Day with pride and gratitude. This is not just a holiday, but a reminder of our strength as a people and the hope of a brighter tomorrow. I, Yerima Usman Shettima, call on every Nigerian to embrace peace, tranquility, and harmony in our homes, communities, and across our nation. Together, in unity and love, we can build the Nigeria of our dreams. Happy Independence Day!”

As we advocate to celebrate 1st October 2025, tomorrow will be the day we are going to have a mega bikers ride in Kaduna...
30/09/2025

As we advocate to celebrate 1st October 2025, tomorrow will be the day we are going to have a mega bikers ride in Kaduna Metropolis under the watch of the National President of Capacity Movement Shehu Sani Sado.

This Ride is purposefully to celebrate 1st October in a wonderful style and the atmosphere will be so peaceful for all citizens to join it because it will be led by Hon. Yerima Shettima who will show us his biking skills.
Tomorrow is the D-Day, there will be a lot of fun✅✅

Don’t miss this day
29/09/2025

Don’t miss this day

29/09/2025
✅✅😂🇳🇬🇳🇬
28/09/2025

✅✅😂🇳🇬🇳🇬

Are u ready ??1st October will be hot
28/09/2025

Are u ready ??
1st October will be hot

Yerima Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Janaral Ahmad Alhassan A yau Asabar, Ambasada Yerima Usman Shettima y...
28/09/2025

Yerima Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Janaral Ahmad Alhassan

A yau Asabar, Ambasada Yerima Usman Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya ga dangin aminin Janaral Ahmad Alhassan a Rigasa, Kaduna, sakamakon rasuwar matar ɗan’uwan sa, wato Hajiya Laure, matar Malam Sani Alhassan.

Hajiya Laure ta rasu a daren jiya bayan samun matsala sakamakon haihuwa, rasuwar ta girgiza dangi, abokai da maƙwabta baki ɗaya.

Yerima Shettima ya bayyana alhinin sa kan wannan babban rashi mai girma, inda ya yi addu’ar Allah ya jiƙan ta da rahama, ya ba mijin ta Malam Sani Alhassan da ‘ya’yan ta haƙurin jure wannan babban rashi.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya ba Janaral Ahmad Alhassan da dukan dangin su ƙarfin zuciya da kwanciyar hankali a wannan lokaci na jarabawa.

Al’ummar Rigasa sun nuna godiyar su ga Yerima Shettima bisa irin nuna kulawa da ya ke yi kan su, na dukkan abin da ya same su ya na ƙoƙarin wajen ganin ya zo domin jajanta wa da nuna alhini a gare su

Haka kuma sun nuna goyon bayan su a dukkan tafiyar sa ta siyasa.

Allah Ya jiƙan Hajiya Laure da rahamar Sa, Ya sanya ta daga cikin bayin Sa na gari, Ya kuma albarkaci dukkan abin da ta bari.

Yerima Shettima ya halarci ɗaurin auren ‘yar aminin sa Gambo GujunguShahararren ɗan gwagwarmaya, mai rajin kare hakkin a...
27/09/2025

Yerima Shettima ya halarci ɗaurin auren ‘yar aminin sa Gambo Gujungu

Shahararren ɗan gwagwarmaya, mai rajin kare hakkin al'umma kuma mai neman takarar zama sanatan Kaduna ta Tsakiya, Ambasada Yerima Shettima ya kasance cikin manyan baƙin da s**a halarci ɗaurin auren ‘yar aminin sa Alhaji Abdulrahman Ibrahim ‘, wanda aka fi sani da Kwamared Gambo Gujungu, wato A’isha Abdulrahman Gujungu.

An gudanar da ɗaurin auren ne da angon ta Abubakar Sa’ad Malumfashi, a masallacin Juma’a na Sultan Bello, Kaduna, bayan kammala sallar azahar.

Yerima Shettima, wanda ya halarta tare da tawagar sa, ya nuna farin ciki da girmamawa ga abokin sa ta hanyar kasancewa cikin wannan muhimmiyar rana. Halartar sa ya ƙara wa bikin armashi tare da nuna kyakkyawar alaƙa da zumunci tsakanin sa da iyalan Gujungu.

Ɗaurin auren ya kasance cike da farin ciki da taron jama’a, inda dangi, abokai da manyan baƙi s**a yi addu’o’in samun zaman lafiya, albarka, da nasara ga amarya da ango a sabuwar rayuwar da s**a shiga.

Allah ya sanyawa wannan aure albarka, ya basu zuri’a ta gari, ya kuma ɗore da soyayya da fahimtar juna.

Yerima Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya kan rasuwar ’yar’uwar Kakakin Majalisar Jihar KadunaA yau Juma’a, fitaccen ɗan ...
27/09/2025

Yerima Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya kan rasuwar ’yar’uwar Kakakin Majalisar Jihar Kaduna

A yau Juma’a, fitaccen ɗan gwagwarmaya, mai neman kujerar sanatan Kaduna ta Tsakiya, Alhaji Yerima Usman Shettima, ya kai ziyarar ta’aziyya kan rasuwar ƙanwar Kakakin Majalisar Jihar Kaduna, Honarabul Dahiru Liman, a unguwar Maƙera Kakuri na Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Kudu, a gidan su da ke bayan Kaduna Textiles Limited (KTL).

Yerima Shettima ya isa gidan mamaciyar ne tare da tawagar sa, domin jajanta wa Kakakin Majalisar da iyalan mamaciyar kan wannan babban rashi.

A yayin ziyarar, Shettima ya bayyana alhini da tausayin sa ga iyalan mamaciyar, tare da roƙon Allah ya jiƙan ta da rahama, ya gafarta mata kurakuranta, ya kuma sanya ta cikin rahamar Sa mai ɗorewa.

Ya ce, “Wannan rashi babban darasi ne da ke tunatar da kowa cewa rayuwa ta duniya lokaci ce mai iyaka, don haka ya zama wajibi a yi amfani da ita wajen kyautata zumunci da kuma ayyukan alheri.

Haka kuma, Yerima Shettima da tawagar na sa sun yi addu’a ga Kakakin Majalisar da iyalan sa baki ɗaya, Allah ya ba su ƙarfin zuciya da juriya wajen jure wannan babban rashi.

Ziyarar ta kasance cike da natsuwa da tausayi, inda al’umma da dama s**a yaba da irin jajircewar Yerima Shettima wajen nuna goyon baya da ta’aziyya a irin wannan lokaci mai raɗaɗi.

Allah yajikan Musulmi Ameen!!

Yerima Shettima ya gwangwaje Masallacin Juma'a na Jama'atul Islamiyya da 'Yan Kwamitin Masallacin da KuɗiFitaccen ɗan gw...
27/09/2025

Yerima Shettima ya gwangwaje Masallacin Juma'a na Jama'atul Islamiyya da 'Yan Kwamitin Masallacin da Kuɗi

Fitaccen ɗan gwagwarmaya, Ambasada Yerima Usman Shettima, kuma mai neman takarar sanata a 2027, ya halarci sallar Juma’a a Masallacin Jama’atul Islamiyya Central Mosque da ke Layin Shaba.

Bayan kammala sallar, limamin masallacin ya jagoranci addu’o’i na musamman domin neman taimakon Allah ga Yerima Shettima, tare da roƙon masa albarka, lafiya da nasara a dukkan harkokin sa.

A wani ɓangare, Yerima Shettima ya nuna karamci da kyakkyawar niyya ga al’umma ta hanyar bayar da kyautar N500,000 ga ‘yan kwamitin masallacin da kuma N500,000 ga masallacin, wanda jimillar su ta kai N1,000,000 (Miliyan ɗaya).

Wannan aiki na nuna jajircewar sa wajen tallafa wa cibiyoyin addini da kuma ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin jagorori da jama’a.

Allah yabada Ladan niya Ameen!!

Ambasada Yerima Usman Shettima da tawagarsa sun ziyarci jama’ar Gadan Gayan.Ambasada A ci gaba da shirye-shiryensa na tu...
26/09/2025

Ambasada Yerima Usman Shettima da tawagarsa sun ziyarci jama’ar Gadan Gayan.

Ambasada A ci gaba da shirye-shiryensa na tunkarar babban zaɓen 2027, tawagar mai girma ɗan takarar Sanatan Kaduna Central, Ambasada Yerima Usman Shattima, ta ziyarci garin Gadan Gayan domin ganawa da shugabanni da kuma jin ra’ayin jama’a kan matsalolin da ke addabar yankin.

Ziyarar ta fara ne a gidan Hakimin Gadan Gayan, Alhaji Shuaibu Gadan Gayan, inda aka yi masa tarba mai girma. A nan, Yerima Shattima ya bayyana cewa burinsa shi ne ya zama muryar talakawa da kare muradun jama’ar Kaduna Central a majalisar dattawa. Daga nan tawagar ta wuce gidan Sarkin Gadan Gayan, inda aka gudanar da tattaunawa mai ma’ana kan bukatun al’umma.

A lokacin ganawar, Sarkin Gadan Gayan ya jaddada irin wahalar da jama’a ke sha sakamakon rashin ingantacciyar wutar lantarki a yankin. Sarkin ya roƙi jagoran siyasar da ya taimaka wajen kawo sauƙi ga al’umma. Cikin hanzari da nuna kishin ƙasa, Ambasada Yerima Shattima ya amsa kiran jama’a ta hanyar bada gudummawar ₦2,000,000 (Miliyan Biyu na Naira) domin a farfado da aikin gyaran wutar lantarkin da ya daɗe yana jinkiri. Wannan lamari ya tayar da farin ciki a zukatan jama’a, inda aka yaba masa da cewa shi ne ɗan takara na gaskiya wanda ya fi maida hankali kan bukatun mutane kafin komai.

Bayan haka, Sarkin Gadan Gayan ya yi addu’o’i na fatan alheri ga tafiyar siyasar Yerima Shattima, tare da bayyana cewa jama’ar Gadan Gayan sun riga sun ɗauki matsaya na tsayawa masa a gaba ɗaya. Ya ce, “A lokacin zaɓe, ba sai ka dawo neman kuri’a ba. Mutanen Gada Gayan suna tare da kai kashi ɗari cikin ɗari.”

Daga nan, tafiyar ta ci gaba zuwa garin Amana, inda Ambasada Yerima Shattima ya halarci wajen ta’aziyya ga iyalan da s**a yi rashi. Ya jajanta musu tare da yin addu’ar rahama ga mamacin, abin da ya nuna irin tausayi da zuciyar jinƙai da ke cikin tafiyar tasa.

Wannan ziyara ta nuna cewa tafiyar Yerima Shattima ba wai kawai an gina ta ne a kan burin neman kujerar siyasa ba, sai dai a kan tsantsar kishin al’umma, taimakon jama’a, da jajircewa wajen ganin an magance matsalolin yau da kullum. Wannan ya ƙara tabbatar da matsayin Yerima Shattima a idon jama’a a matsayin jagoran da ya dace da zamaninmu mai sauraro, mai aikatawa, kuma mai mutunta jama’a.

Amb. Ya samu damar rakiyarsu Shugaban Capacity movement na kasa, waton Alh. Shehu Sani Sado, mai magana da yawun bakin Capacity Movement, Mallam, Abdulhakeem Mutiu, Hajia Mariya da sauransu.

25/9/2025

Allah yabamu nasara yasa Ameen!!

URMC Bikers in Collaboration with Capacity Movement Set for 1st October Mega Town Ride in KadunaThe Ultimate Riders Moto...
26/09/2025

URMC Bikers in Collaboration with Capacity Movement Set for 1st October Mega Town Ride in Kaduna

The Ultimate Riders Motorcycle Club (URMC Bikers), in collaboration with the Capacity Movement, is proud to announce the 1st October Mega Town Ride, a thrilling celebration of unity, freedom, and community spirit. The event is scheduled to take place on October 1st, 2025, in Kaduna, Nigeria.

The Mega Town Ride promises to be more than just a motorcycle parade. It will feature a Town Ride, Gala Night, and Barbecue, creating a platform for recreation, networking, and positive social engagement. Riders from across Nigeria and beyond will converge in Kaduna, showcasing not only the power of motorcycling culture but also the strength of collaboration in promoting peace, capacity building, and youth empowerment.

Speaking ahead of the event, the organizers emphasized that this initiative is designed to foster unity, camaraderie, and responsible social engagement, especially at a time when communities need renewed hope and collective resilience.

The event will bring together motorcycle clubs, community leaders, students, youth leaders, and civic groups in a display of solidarity, strength, and inclusiveness. Participants will not only enjoy the adrenaline and entertainment but will also engage in meaningful interactions that inspire capacity development and cultural integration.

The Capacity Movement, known for its people oriented philosophy, is partnering in this initiative to reinforce its vision of promoting youth involvement, social cohesion, and community empowerment through diverse platforms of engagement.

With the Town Ride symbolizing freedom, the Gala Night celebrating unity, and the Barbecue strengthening bonds of friendship, this year’s Mega Town Ride promises to be an unforgettable experience for Kaduna and beyond.

Event Details

📅 Date: 1st October 2025
📍 Venue: Kaduna, Nigeria
🎉 Highlights: Town Ride | Gala Night | Barbecue

Address


Telephone

+2347067056078

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yerima shettima Support Group posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Yerima shettima Support Group:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share