Alfallatee

Alfallatee Your vibe attracts your tribe

AL'UMMAH RAHAMA NEA wannan rayuwan idan kaga mutane na tururuwa zuwa gareka, mutane na son zuwa kusa da kai, mutane na s...
21/09/2025

AL'UMMAH RAHAMA NE

A wannan rayuwan idan kaga mutane na tururuwa zuwa gareka, mutane na son zuwa kusa da kai, mutane na son mannuwa dakai toh tabbas Allah ya azurtaka da wata ni'ima ko dai ta dukiya, Ilimi, Mulki ko Sarauta, koma Allah ya hada maka gaba daya.

Ya kai dan'uwa idan Allah yayi maka daya daga cikin ni'imominsa a rayuwa toh ka gode masa ta hanyar anfani da wannan ni'imar da ya maka wurin kyautatawa Al'ummah ko yin abinda Allah yakeso kuma ya aminta dashi.

Kada kayi anfani da ni'imar ko wata dama da Allah ya baka anan duniya ka wulaqanta Al'ummah da kake rayuwa tare dasu, saboda cikin qanqanin lokaci Allah yana iya karbe ni'imar ko damar ya baiwa wani wanda baka taba tunanin zai iya samu ba, dama kai dinma ba wayonka ko dabararka ko qarfinka ne yaba ka.

NI'IMAH TA DUKIYA

Dukiya tana daya daga cikin ni'imomin da Allah ke yiwa wasu daga cikin bayinsa anan duniya kuma daya ce daga cikin ni'imomin da idan Allah yayi maka toh mutane zasuyi tururuwa zuwa gareka musamman ma idan ka kasance mai budadden hannu.

Idan Allah yayi maka ni'ima ta dukiya kayi iyakan qoqarinka ka kyautatawa Al'umma da wannan dukiyar sannan kayi iyakan qoqarinka ganin ka aikata abinda Allah yakeso da wannan dukiyar.

Kada kabi zugin shaidan da shaidanu wadanda zasu riqa fada maka cewa: ''mutanen nan sunzo su qarar maka da abinda ka tara'' ko ''suna daura maka nauyinsu'' ko "kaifa ba Gomnati bane" ko "Mutanen nan basu tayaka tara dukiyar ba'' dss...

Kasani ko kayi abinda ya dace da dukiyar ko karkayi dayan biyu sai ya faru: kodai dukiyar ta qare ta barka ko kuma kai Ka mutu ka bar dukiyar kuma sai Allah ya tambayeka akai gaba daya.

NI'IMAH TA ILIMI

Ilimi shima daya daga cikin ni'imomin da Allah yake yiwa wasu daga cikin bayinsa ne inma na addini ko na wani fanni na rayuwa wanda kuma kesa Al'umma suyi tururuwa zuwa garesu musamman ma idan Ilimin ya zama na addini ne ko na dukka biyu.

Idan Allah ya baka dimbin Ilimi na Addini ko na wani fanni na rayuwa toh kayi iyakan qoqarinka wurin anfanarda al'umma da wannan Ilimin kuma kayi iyakan qoqarinka wurin aiki da wannan Ilimin ta hanyar da Allah yakeso.

Kada Ka yarda iliminka ya samar maka da daya daga cikin wadannan abubuwan acikin rayuwarka
1. Girman Kai
2. Raina kowa
3. Kowa Jahili ne
4. Kaine kadai Masani
5. Too Harsh
6. kowa batacce ne
7. Kowa dan wuta ne, dss...

Ilimin da Allah ya baka abin tambaya ne a gareka a ranar Hisabi, Allah yasa mudace da abinda yake dai dai kuma ya yarda dashi.

Bari mudan kurbi koku mu hadu a Rubutu na gaba .....

✍️: Muhammad Khalid Hussaini
(De GENERAL)
21/09/2025

20/09/2025

It's Now Official Dr Adamu Abdullahi Rarara
Congratulations Rarara
Allah yasa a gama lafiya

19/09/2025

DOKAR WA'AZI A JAHARMU TA NIGER 002

A Rubutu na farko na zayyano wasu tambayoyi wadanda Al'umman Jahar Neja zasu buqaci amsarsu daga wurin DG na Religion affairs Akan wannan dokar

A wannan Rubutun zan bayyana kadan daga cikin abubuwa dana fahimta tun bayan yin Rubutu na farko izuwa yau sannan nayi Kira zuwa ga mai Girma Gwamna

Kadan daga cikin abubuwa dana fahimta:

1. Na fahimci cewa daga cikin Malamanmu na Jahar Neja akwai wadanda suke goyon bayan dokar haka kuma akwai wadanda basa goyon bayanta, Wanda har nake gani kamar wadanda basa goyon bayanta sunfi yawa sosai

2. Wadanda s**a taso da ita ko sukeso a kafata sunayi ne da kyakkyawar manufa tsakaninsu da Allah haka Suma wadanda basa goyon bayanta kuma basa goyon bayan kafata sunayi ne da kyakkyawar manufa tsakaninsu da Allah

3. Wadanda suke son a kafata sunayi ne don a tsabtace wa'azi daga yawan raddi mara anfani ko zage zage ko Kira zuwa ga mummunan Aqeedah ko yin Kira zuwa ga ababenda zasu kawo tashin hankali a Jaha da sunan wa'azi, Wanda kuma wannan abune mai kyau a tsabtace wa'azi daga wadannan ababen.

4. Haka kuma Wadanda basaso a kafata sunayi ne don kar abude kofar cin mutumcin masu wa'azi ko tauye haqqin wasu masu wa'azi, ko sakawa Malamai linzami Akan iya abinda zasu iya fada ko zasu iya karantarwa, Wanda Gomnati (musamman nan gaba) na iya Hana duk wani Wanda baya tare da ita a siyasa daga wa'azi ta hanyar janye lasisinsa, Wanda kuma wannan shima abun lura ne sosai, saboda Yana iya jawo tashin hankali a Jaharmu, Allah ya kiyaye.

KIRANMU GA MAI GIRMA GWAMNA

Mai Girma Gwamna Umar Mohammed Bago kowa a Jahar Neja yasani cewa kanada manufa mai kyau ga Jaharmu dama Al'umman Jahar gaba daya, da wannan nake Kira zuwa gareka kayi duba mai kyau ga wannan dokar, ba don yanzu ba sai don nan gaba musamman lokacinda zai zama ba Kaine Gwamna ba, kai kanada manufa mai kyau na kafa dokar ko reinforcing dokar, Amma wani nan gaba zaizo da nashi manufar yayi anfani da dokar yaci mutumcin duk Malaminda yakeso yaci ko ya gallazawa wasu Malamai da basa ra'ayi daya dashi ko basa goyon bayanshi a siyasa.

Don haka Mai Girma Gwamna ina bada shawora a maimakon wannan dokar a kafa wata commitee Wacce zata hada da Manyan Malamai na ko Wace Qungiyar Addini a Fadin Jahar da Manyan Lauyoyi da Alqalai (masana shariar Musulunci) da Jami'an tsaro

Yazama aikin wannan committee din shine Kula da wa'azozin Malamai a Fadin Jahar gaba daya, duk Malaminda akaga Yana Kira ko wa'azi Wanda zai kawo tashin hankali a Jahar ko Yana Kira zuwa ga wata mummunan Aqeedah sai wannan committee din ta gayyaceshi ta zauna dashi ta nuna masa kurakuransa tare da kafa masa Hujja daga Alqur'ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) da kuma dokan Qasa, idan bayan Zama dashi yaqi ya gyara sai Gomnati ta dauki Mataki na doka akanshi.

Muna Rokon Allah daya dawwamarda zaman lafiya a Jaharmu ya karemu daga dukkan fitina, Ameen.

Mu hadu a Rubutu na 003 in shaa Allah.......

✍️: Muhammad Khalid Hussaini
(De GENERAL)
19/09/2025

GWAMNA ABBA KABIR YUSUF YA AMINCE DA BAIWA KANANAN HUKUMOMI DAMAR KASHE KUDADENSU KAI TSAYE Gwamnan Jihar Kano, Alhaji A...
12/09/2025

GWAMNA ABBA KABIR YUSUF YA AMINCE DA BAIWA KANANAN HUKUMOMI DAMAR KASHE KUDADENSU KAI TSAYE

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana goyon bayansa ga kudurin doka da zai bai wa ƙananan hukumomi 44 na jihar cikakken ‘yanci wajen tafiyar da harkokinsu na mulki da kuɗi.
Sanarwar gwamnatin Kano
Sanarwar hakan ta fito daga bakin Daraktan Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, a ranar Juma’a.

TARON MAJALISAR ZARTASWA
An bayyana matsayar Gwamnan ne yayin taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 31 da aka gudanar a Kwankwasiyya City, inda aka amince da mika kudurin dokar zuwa Majalisar Dokokin Kano domin tattaunawa da kuma ɗaukar mataki a kai.

ANFANIN SABON TSARIN
A cewar Gwamna Abba, wannan kuduri zai bai wa kananan hukumomi damar gudanar da harkokin kuɗaɗensu da kuma aiwatar da ayyukan raya ƙasa cikin sauri, ba tare da dogaro da gwamnatin jiha ta tsakiya ba.
Ya ce wannan sauyi zai taimaka wajen cika muradun jama’a kai tsaye daga tushe, tare da tabbatar da nagartaccen mulki, gaskiya da rikon amana.

ZURFAFA DIMOKRADIYYA
Gwamnan ya bayyana matakin a matsayin wata hanya ta zurfafa dimokuraɗiyya a jihar Kano.
Ya kuma yi tabbacin cewa ‘yan majalisar dokokin jihar za su mara baya ga kudurin, kasancewar manufarsa ta yi daidai da muradin jama’ar Kano gaba ɗaya.

12/09/2025

Proff Mai Capacity
Proff Abubakar Umar Gire Wakilin Lamidon Adamawa at Madako Niger State

Alhaji Hassan Usman Shiroro,Wakilin Fulanin Minna kuma Coordinator na Bago Ruga Ruga,Ya umarta dukkan Shugabannin Kanana...
11/09/2025

Alhaji Hassan Usman Shiroro,
Wakilin Fulanin Minna kuma Coordinator na Bago Ruga Ruga,
Ya umarta dukkan Shugabannin Kananan Hukumomi da Jagororin Ruga Ruga da su tabbatar cewa dukkan al’umman Fulani da ke ƙarƙashin kulawarsu sun mallaki katin zaɓe. Wannan kira ya yi daidai da lokacin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta buɗe sabunta katin zaɓe da kuma yin sabon kati ga waɗanda ba su taɓa yin katin zaɓe ba a baya.

GWAMNA UMARU BAGO YA JADDADA BUKATAR WAYAR DA KAN FULANI SU RUNGUMI KIWON SHANU NA ZAMANI Gwamnan Jihar Neja, H.E RT. Um...
10/09/2025

GWAMNA UMARU BAGO YA JADDADA BUKATAR WAYAR DA KAN FULANI SU RUNGUMI KIWON SHANU NA ZAMANI

Gwamnan Jihar Neja, H.E RT. Umaru Mohammed Bago , ya sake jaddada bukatar wayar da kan Fulani domin su rungumi kiwon shanu na zamani (ranching) a matsayin hanya mafi inganci ta inganta kiwo da kuma rage rikicin manoma da makiyaya.

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da wasu shugabannin Fulani ƙarƙashin Madako Foundation for Conflict Resolution and Empowerment s**a kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Minna.

Amfanin kiwon zamani

A cewar Umaru Bago, tsarin kiwon zamani (ranching) shi ne matakin da yafi dacewa wajen kula da kiwon shanu, domin zai kawo sauƙi, ya ƙara yawan amfanin kiwo, kuma ya samar wa Fulani ƙarin hanyoyin samun kuɗaɗe ta hanyar sarrafa kayayyakin kiwo da sarrafa ababenda Ake samu daga jikin shanu (Madara, Nono, Man shanu, da kashinsu).

Ya yaba da jajircewar Fulani wajen aiki, tare da gargadin waɗanda ke kutse a gonakin jama’a da su daina wannan dabi’a. Haka kuma ya bukaci Fulani da su tabbatar da cewa ’ya’yansu suna samun ilimi, yana mai yabawa ƙoƙarin Madako Foundation na qoqarin dawo da ’ya’yan Fulani makaranta, tare da kiran Fulani masu ilimi dasu taimaka wajen inganta makarantu na makiyaya a jihar.

BAYANIN LAMIDON ADAMAWA

Wakilin Lamidon Adamawa, Dr. Abubakar Umar Girei, ya yaba wa Gwamna Bago bisa soyayya da kulawarsa ga Fulani, inda ya ce Fulani gaba ɗaya suna alfahari da dangantakansu da Gwamna Bago. Ya ƙara da cewa shugabannin Fulani zasu yi aiki tare da gwamnatin jihar wajen gano masu laifi domin tabbatar da zaman lafiya.

GUDUMMAWAR MADAKO FOUNDATION

Shugabar Madako Foundation, Hajiya Hauwa Ibrahim Madako, ta bayyana cewa an kafa cibiyar ne sakamakon darasi da ta samu daga wani Yaro nata Wanda ya samu lalurar tabin hankali inda Al'ummah s**a taimaka Mata daga ko ina Kafin yaron ya rasu. Tace cibiyar na bada tallafi ga iyalai masu yara masu lalura, dawo da waɗanda s**a daina karatu, warware rikice-rikice da kuma ƙarfafa gwiwa, inda sama da yara 2,000 s**a amfana a faɗin ƙasar.

KARIN YABO DAGA JAHAR TARABA

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Taraba, Ibrahim Tukur El-Sudi, ya yabawa Gwamna bisa jajircewarsa wajen tallafawa Fulani da kuma kishin jama’a tun daga lokacin da yake ɗan majalisa a tarayya.

BAYANIN DG NA GYARAN MAKARANTU

Haka kuma, Daraktar Janar na gyaran makarantu, Hajiya Maimuna Mohammed, ta nuna jin daɗinta da ƙoƙarin Madako Foundation na ƙarfafa yara su shiga makaranta, tana mai cewa hakan ya dace da tsarin gwamnatin jihar na samar da sabbin gine-ginen makarantu a cikin Rugagen Fulani a fadin Jahar.

✍️; Muhammad Khalid Hussaini
(De GENERAL)
10/09/2025

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alfallatee posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Alfallatee:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share