Bahrul faidah

Bahrul faidah 𝙬𝙚 𝙖𝙧𝙚 𝙡𝙤𝙫𝙚r𝙨💚💚💚𝙤𝙛 𝙨𝙝𝙚𝙝𝙪 𝙞𝙗𝙧𝙖𝙝𝙞𝙢 𝙣𝙞𝙖𝙨s
𝙞𝙣 𝙖𝙣𝙮 𝙨𝙩𝙪𝙖𝙩𝙞𝙤𝙣💪💪💪 𝙄'𝙢 𝙢𝙪𝙖𝙬𝙞𝙮𝙖 𝙢𝙖𝙨𝙤𝙮𝙞𝙣 𝙜𝙖𝙪𝙨𝙞
𝙄'𝙢 21 𝙤𝙡𝙙 𝙞'𝙢 𝙡𝙞𝙫𝙞𝙣𝙜
𝙞𝙣 𝙠𝙖𝙣𝙤

Na rubuta Sheikh Mal. Tijjani Usman Zangon Bare-bari shi ne farkon wanda ya fara tara jama'a yana karantar da tafsirin A...
13/07/2025

Na rubuta Sheikh Mal. Tijjani Usman Zangon Bare-bari shi ne farkon wanda ya fara tara jama'a yana karantar da tafsirin Alkur'ani mai girma a garin Kano. Akwai daga wasu sashen ƴan uwa Ƙadirawa, suna cewa mu kara bibiyar tarihi. Domin suna ganin Malam Nasiru Kabara shi ne ya fara tafsirin a gidan Ciroma Muhammadu Sunusi I sarkin Kano na goma sha ɗaya a jerin Fulani.

Gaskiya babu tabbacin tafsirin ana tara mutane domin sauraro irin yanda ake yi yanzu. Malam Nasiru Kabara, shi ya fara gabatar da tafsirin Alkur'ani na tara mutane suna sauraro a irin wanda a ke yi yanzu a cikin shekarar 1954, a gidan masarautar Kano.

Shi Sheikh Malam Tijjani Usman Zangon Bare-bari ya fara gabatar da tafsirin Alkur'ani na tara mutane suna sauraro irin wannan na da ke yi a yanzu a cikin shekarar 1950, shekaru 75 kenan .

✍️




KADAN DAGA CIKIN TARIHIN SHEIKH MODIBBO JAILANI YOLAAn haife shi a garin KAFIN IYA a cikin jihar Bauchi a Shekarar 1298 ...
10/07/2025

KADAN DAGA CIKIN TARIHIN SHEIKH MODIBBO JAILANI YOLA

An haife shi a garin KAFIN IYA a cikin jihar Bauchi a Shekarar 1298 Hijira Daidai da 1903 Miladiyya

Sunan Mahaifin sa Modibbo Muhammad Sunan Mahaifiyar sa Fatima

Ya Fara karatu a gaban mahaifinsa Daga nan Sai aka turashi neman Ilimi Waje Alkali Abubakar Gombe da Modibbo garba Nafada

Modibbo Muhammad Limamin Bauchi sai ya wuce Zaria Wajen Mal.Sani Zaria Daga nan ya Tafi kano Wajen Sarkin Malaman kano a nan mandawari da Sheikh Salga Mallam Sani Abdulhamid Duka a birnin kano
Ya samu iliminsa yana Dan Shekara 23 ya wallafa litattafai da Dama Kadan daga Ciki akwai

Khaliphatil Khatamil Awliya'i Jarri
Arumu Bila Dulil Mada
Minka Nazzaratun Ala Gsusul Baraya

Yayi Tafsirai a Cikin harshen Fulatan ci da dama yana da Almajirai da dama k**ar Su Modibbo Hamma Adama jada, Modibbo Muhammad Jawai, Modibbo Dahiru Ganye, Modibbo Muhammadu Jalingo, modibbo Ibrahim daware Dadai Sauransu Yana Da Yara 32 yabar khalifan sa Tijjani Modibbo Ya sami Shekaru 82 a Dunia Raulansa Yana daga dama Da masallacin Juma'ar sa Dake Gidan sa a YOLA

Ya ziyarci kasashe da dama yana kuma Cikin Wanda S**aje taron OIC Zamanin Shugaban Kasan Nigeria na Wannna Lokacin
IBRAHIM BABANGIDA tare da Manyan Malaman Nigeria

Allah Yayi masa Rahma
Ameen 🤲🤲🤲🤲
✍️

✦ FASSARAR "Fakkar Sihiri Na Gaskiya" (Maganin Sihiri Mai Karfi) ✦Daga DrShareef Basiru Tam Ayoyin da ake amfani da su d...
09/07/2025

✦ FASSARAR "Fakkar Sihiri Na Gaskiya" (Maganin Sihiri Mai Karfi) ✦
Daga DrShareef Basiru Tam

Ayoyin da ake amfani da su domin warware sihiri:

1. Wa qul jā’a al-ḥaqqu wa zahaqa al-bāṭilu, innal-bāṭila kāna zahūqā
(Ka ce: Gaskiya ta zo, kuma ƙarya ta ɓace, lallai ƙarya bata da tsayin daka)

2. Innā fataḥnā laka fatḥan mubīnā
(Lallai Mun buɗe maka buɗewa bayyananna)

3. Wa futiḥatis-samā’u fakānat abwābā
(An buɗe sama, ta zama ƙofofi)

4. Fa awḥaynā ilā Mūsā aniḍrib biʿaṣākal-baḥra fa-infalaqa fakāna kullu firqin kaṭ-ṭawdi al-ʿaẓīm
(Sai muka yi wa Musa wahayi, ka bugi teku da sanda, sai ya rabu biyu k**ar dutse babba)

5. Lā ḥawla wa lā quwwata illā billāhil-ʿaliyyil-ʿaẓīm
(Babu ƙarfi da iko sai da Allah Maɗaukaki Mai Girma)

6. Wa qadamnā ilā mā ʿamilū min ʿamalin fajaʿalnāhu habā’an manthūrā
(Mun fuskanci ayyukansu, muka mai da su k**ar ƙura mai yawo)
(A karanta sau 2)

7. Qāla Mūsā lammā alqaw: Mā ji’tum bihis-siḥru, innallāha sayubṭiluh. Innallāha lā yuṣliḥu ʿamalal-mufsidīn. Wa yuḥiqqallāhul-ḥaqqa bikalimātihi walaw karihal-mujrimūn.
(Musa ya ce: Abinda kuka zo da shi sihiri ne, kuma Allah zai warware shi. Lallai Allah baya yarda da aikin masu ɓarna. Kuma Allah zai tabbatar da gaskiya da kalmominsa ko da ‘yan laifi sun ƙi.)

---

YADDA AKE AMFANI DA AYOYIN:

A karanta dukan wadannan ayoyi a kan zuma tsantsa (original honey).

Bayan karantawa, a tufa a kan zuma.

Kullum da safe kafin a ci komai, a ɗauki cokali 1 na wannan zuma.

Kafin shan wannan cokali, a karanta wannan aya sau 3:

> “Yakhruju min buṭūnihā sharābun mukhtalifun alwānuhu fīhi shifā’un lin-nās, inna fī dhālika la-āyatan liqawmin yatafakkarūn”
(Ana samun ruwan da ke magani daga cikinta wanda launinsa ya bambanta – akwai warkarwa a ciki – lallai wannan aya ce ga masu yin tunani.) – [Surat an-Naḥl: 69]

---

✦ Ƙarin Fa'idodin Sirri Da Za Ka Iya Amfani Da Su:

✅ 1. Don Kariyar Gida daga Sihiri:

Karanta Ayatul Kursiyy sau 7 kowane yamma da safe.

Fesa ruwa da aka karanta masa aya na 7 da Suratul Falaq

MAULANA SHEIKH ALIYUL HARAZIMY (RTA)Bawan Allah Ne SadiQi Ma'abocin Himma Akan Dukkanin Lamarin Ambaton Allah Da SHUGABA...
09/07/2025

MAULANA SHEIKH ALIYUL HARAZIMY (RTA)

Bawan Allah Ne SadiQi Ma'abocin Himma Akan Dukkanin Lamarin Ambaton Allah Da SHUGABA (S A W)

Shehy Ya Kasance Mai Tarbiyantar Da Dukkanin Bayin Ubangiji Zuwa ga Ambaton Allah A Koda Yaushe Ta Yadda Zasu Gane Girman Ubangiji

Shehy Ma'abocin Bayar Da Karatune A Dukkanin Lokacin Zaman sa Bazaka Tabajinsa Yana Firar Duniya Ba Baida Wani Aiki Kaman Ambaton Allah da SHUGABA (S A W)

Har Zakaji Mutane Suna Rantsuwa Suna Ikrarin Samun Sufy Irin Maulana Shehu Aliyul HARAZIMY (RTA) Abune Mai Matukar Wahala Zakaji Kowa Idan Zaiyi Magana akansa Yana Fadan Tsantsar Tsantsaninsa Ga Dukkanin Kazantar Duniya Domin Shi Awajansa Kowa Mutumin Kirkine

Har Wata Rana Yana Cewa Idan Yaga Ko Yaji Ance Wani Mutum yana Aikata Wani Mummunan Aiki Yakan Fara Dubane izuwa Karan Kansa Idan Yaga Ya Barranta Da Abun sai Ya sake Godewa Ubangiji Tare Da Sake Tsere Masa
Idan Kuma Yaga Ya Suffantu da Wannan Aikin sai Yayi Ta Rokon Ubangiji Har Ya Sanya Guje Masa A Gareshi

Duk Wanda Yaje Zawiyya Gidan Maulana Sheikh Aliyul Harazimy Kasan Ba wai Gidan Wasa Bane Da Har zaka Keta Shari'a Ka Zauna Lafiya
Kallon Ka Kadai Izuwa Gidan Idan Kayi Tafakkuri Kai kanka kasan Bawai Gidan Wasa Bane Bayan Allah Da Manzon Allah (S A W) Babu Abun Ambato Sama Dasu Domin Kuwa Babban Tambarin Gidan ma Shine Zikirin Allah

Ubangiji Ka Kara Mana Alfarmarsu Bijahi SHUGABA (S A W)

09/07/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Abu Abu Khaidar, Aliyu Habibu, Rabiu Salisu Gambo, Shafi'u Daura, Manniru Surajo, Itz Muhammad, Isyaku Yallabai, Suraj Yusuf, Muhammad Nuhu, Taiwo Ayomide, Abdullahi Sani Zarewa, Abubakar Sadik Ahmed, Auwal A Shehu, Yahaya Muhammed, Ashiru Musa, Ibrahim Sadiq, Abdullahi Salisu, Adamu Babba, Mabel Akade, Abubakar Abba Lawal, Bilkisuibrahim Ibrahim, Aliyu Ibrahim, Umar Aliyu, Tudu Alh Musa, Emma Akpan, Bala Saleh, Gambo Shuaibu, Gambo Suleiman, Ba Ana Tasiu Muhammed, Muhmmad Usman, Baffasanikiyawajgw Sani Baffa Kiyawa, Auwalu Rabiu, Bello Usman, Mohammed Mohammed, Abubakar A Abubakar, Umar Suleiman Suleiman, Alkasim Moriki, Mahadi Isiaka Bisalla, Usuman Baba, Abdullahi Isah Malan, Yahaya Musa Okpu, NaziyBig T Haruna Idris, Laminu Ahmad, Taiwo Ganinu, Olamide Gbemisoye, Usman Musa, Almustapha Ibrahim, Shamsu Ibrahim, Adamu Yakubu, Kabir Ibrahim Rabiu

BATUN ANNABI ﷺ AKE YI******Ina so ku daure ku karanta rubutun nan har ƙarshe domin ku fahimci dalilin da muminai s**a ri...
08/07/2025

BATUN ANNABI ﷺ AKE YI
*
**
***
Ina so ku daure ku karanta rubutun nan har ƙarshe domin ku fahimci dalilin da muminai s**a riƙa.
***

An cusa mana wata mummunar aƙida ta rashin karɓar gaskiya muddin ba daga wurin mutanen mu ya fito ba, wannan kuwa ba tarbiyar Annabi ﷺ bace ga al'umma, domin sahabin sa ya haɗu da shaiɗan, shaiɗan ya bashi fa'ida, yazo ya gaya wa Annabi ﷺ, Annabi ﷺ ya tabbatar lallai fa'idar haka take, amma shi shaiɗan yana nan a matsayin sa na maƙaryaci.

Don haka idan muka ce kar ayi bidi'a iri kaza da kaza, hakan bai sa mun zama wahabiyawa ba don sune s**a yawan amfani da kalmar bidi'a, haka zalika idan muka nuna soyayya ko alhini ga Ahlulbayt, hakan bai sa mun zama yan shi'a ba don sune suke da'awar soyayyar Ahlulbayt ko yaushe.

Ga dalilan mu na nuna alhini kisan Imam Hussaini k**ar haka:

1. Mu musulmai ne Al'ummar Annabi ﷺ, Ayoyi biyu a Qur'ani sun nuna mana darajar Ahlulbayt kai tsaye, hadisai mabanbanta sun nuna girman Ahlulbayt da wajibcin so da girmama su, dubi girman sallah fa, Amma jikan Annabi ﷺ ya hau wuyan sa yayin da yake sujjada a salla, shi ko Annabi ﷺ bai taso ba har sai da jikan nasa ya sauka. Sannan akwai inda Annabi ﷺ ke tabbatar da cewa kar a yarda wa'yannan jikokin nasa suyi kuka, sannan jikokin nan nasa sune shugabannin samarin Aljanna, inda ni da ku muke fatan kasancewa, a haka aka ce maka an k**a ɗaya daga cikin su anyi masa mummunar kisa fa, amma kana cewa meyasa za a nuna rashin jindadin kisan?

2. Mu almajiran Shehu Tijjāni RTA ne, muna da kwakkwarar alaƙa da iyalan Annabi ﷺ domin Shehu Tijjāni RTA Sharifi ne ta tsatson Imam Hassan A.S, sannan ya nuna mana girman sharifai a aikace ta hanyar hana almajiran sa na farko auren mace sharifiya don gudun kar a sanya ta kuka k**ar yadda Annabi ﷺ yayi umurni, sannan a bayyane Shehu Tijjāni in yaji an ambaci sunan yazidu sai ya tsine masa, ba a ranar ashura ba, a'a ko yaushe yake yin haka fa, me kake tsammani daga mabiya Ɗariƙar sa?

3. Mu yan faidha ne, mabiya Shehu Ibrahim Niasse

SHEHU ABUBAKAR ATIKU RTA YANA CEWA Zamanin nan yayi baƙi zukatan mutane sunyi duhu babu haske, babu sauran abinyi sai ib...
07/07/2025

SHEHU ABUBAKAR ATIKU RTA YANA CEWA

Zamanin nan yayi baƙi zukatan mutane sunyi duhu babu haske, babu sauran abinyi sai ibada cikin zawiyya, zawiyyarma ta Shehu Ahmadu Tijjāni (RTA) Don haka nasiha ɗaya ce, ku karɓi Ɗariƙar Tijjaniyya wacce asalin ta daga Annabi Muhammadu (SAW) take kuma an ginata ne akan Al'Qur'ani da hadisi

LAZIMIN SAFE DA YAMMA

Acikin ta akwai umurnin Allah (SWT) da yake cewa: yaku wayanda kukayi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa kuma kuyi masa tasbihi a safiya da maraice kaduba (Suratul Ahzab 41-42) Shi yasa muke Lazumi da Safiya da maraice

ZIKIRIN JUMA'A

Acikin ta akwai umurnin Allah (SWT) da yake cewa: yayin da aka idar da sallah ku tafi ku warwatsu cikin ƙasa kuna nema daga falalar Allah kuma ku ambaci Allah sosai, watakila za ku rabauta (Suratul Jumu'ah 10) Shi yasa ko wacce juma'a bayan sallar la'asar muke ambaton Allah cikin jam'i har zuwa magariba

WAZIFA

Acikin ta akwai umurnin Annabi (SAW) da yake cewa: Idan kukazo wucewa ta dausayin Aljanna, ku tsaya kuyi kiwo, Sahabbai s**a ce ya Rasulilah ina ne dausayin Aljanna yace inda akai da'irar zikiri hadisin (Tirmizi 3510) Shi yasa muke da'ira kullum sau ɗaya muna wazifa

A cikin lazumin mu na safiya da maraice, da zikirin juma'a, da kuma wazifa, babu abinda muke karantawa sai Istigfari Salatin Annabi SAW da La ilaha illallah su kuwa Allah ne yace

ku nemi gafarar Ubangijin ku Lallai shi Allah ya kasance mai yawan gafara (Suratun Nuhu: 10)

Lallai Allah da Mala'iku suna salati ga Annabi (SAW) yaku wayanda kukayi imani kuyi salati a gareshi da aminci (Suratul Ahzab: 56)

Lallai ka sani Ya Rasulallahi La ilaha Illallah wato babu abin bautawa da gaskiya sai Allah (Suratul Muhammad: 19)

Lallai bazaku kubuta daga biyewa son zuciya ba sai kun riki wani shehi masanin Allah kuna kamun ƙafa dashi da bibiyar ayyukan sa, Mafi alkairi da daraja da fifiko cikin Shehunnai da Dariƙu baki daya shine Shehu Ahmadu Tijjāni RTA da Ɗarikar sa💚💚💚
'iman💪💪💪
✍️

05/07/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Hayatu Yahaya, Aliyu Suleiman, Alhaji Sulaiman Minkail Abdullahi, Timothy Agwu, Abubakar Baffa, Yahaya Sani Randy, Malan Na Lawan Muslum, Aliyu Mai Dankunne, Shehu Ali Garba, Zairat Dahiru, Aliyu Isiyaku, Abdullahi Cisse, Masaudu Abdullahi, Bello Ricardo, Isah Bauchi, Muhammad Shafii Aliyu, Aliyu Yusuf, Sani Abubakar Dattijo, Usman Mai Unguwa Gwanji, Nurwa Aee'sha, Alhaji Auwalun Jarma, Ibrahim Yahaya Dambatta, Talban Jamaa, Wali Randa, Alhaji Muhammad Maiha, Ibrahim Barawa, Opphicial Sisty Dan Umma, Sa'adatu Dayyabu, S Isah Riga, Ado Umar, Abdullahi Muhammad Gali Snk, Mohammed Saleh, Isiyaqa Abubakar Mandera, Sulaiman Imiran, Muhammad Yammawa, Yusuf Suleiman, Sagiru Hassan, Isah Ahmadu, Garba Ibrahim, Lawan Ahmed Ahmed Lawan, Igwe Innocent, Zainab M Salihu, Goni Abubakar, Bashir Dauda Yarima, Haruna Namadi Gajida, Auwalu Aminu, Daniella Kwarteng, Musa Salenababa, Abdulsalam Ahmed, Khadija Umar Uba

Wannan Sune Sakonnin Da MANZON ALLAH S.A.W Ya Aikawa Sarakunan Duniya Na Wancan Lokacin Yana Kiransu Zuwa MusulunciKo Za...
05/07/2025

Wannan Sune Sakonnin Da MANZON ALLAH S.A.W Ya Aikawa Sarakunan Duniya Na Wancan Lokacin Yana Kiransu Zuwa Musulunci

Ko Zaku Iya Karantawa Gashi Dai Ba Nuqda Ba Wasali

Yaa Allah Yakara Mana Kaunar Manzon Allah Ameen summa Ameen 🤲🤲🤲🤲

Shehu Ibrahim fardune☝️☝️☝️

03/07/2025

Big shout-out to my newest top fans! Mahammat Sha Aibu, Dan Ladi Abdussalam, abbas abba garga

'KISSA; SHEHU UMARUL-FUTY(R.A)👇👇👇Wata Rana a Birnin Madinatul-Munawwara, Shehu Umarul-Futy(R.A) Ya Kai Ziyara Wajen Sheh...
02/07/2025

'KISSA; SHEHU UMARUL-FUTY(R.A)👇👇👇

Wata Rana a Birnin Madinatul-Munawwara, Shehu Umarul-Futy(R.A) Ya Kai Ziyara Wajen Shehunsa Wato Babban Waliyin Nan Sheikh Muhammadul Ghali(R.A) Dake Zaune a Madina,

Da Ya Je 'Kofar Gidan Sai Ya 'Daure Dokinsa a Waje Ya Shiga Gidan, Yayi Sallama Ya Shiga Ya Zauna Tare Da Shehunsa Suna Zantawa.

Suna Zaune Suna Magana Sai Aka Yi Sallama a 'Kofar Gida, Da Jin Haka Sai Sheikh Muhammadul Ghali(R.A) Ya Fita Waje Ya Ga Waye Yake Sallama.

Ashe Wani Sharifi Ne(Jinin MANZON ALLAH(S.A.W) Bayan Sun Kammala Gaisawa Da Wannan Sharifin, Sharifi Zai Koma Sai Muhammadul Ghali(R.A) Ya Rasa Wacce Hadiya Zai Bashi, Kawai Sai Kunto Dokin Shehu Umarul-Futy(R.A) Ya Bashi a Matsayin Hadiya, Ya Tafi Da Shi, Ba Tare Da Ya Sanar Masa Ba.

Sheikh Muhammadul Ghali(R.A) Ya Koma Gida Bayan Sun Kammala Zantawa Da 'Dalibinsa; Ya Tashi Zai Tafi, Sai Ya Rako Shi Zuwa Kofar Gida.

Sai Shehu Umaru Futy(R.A) Ya Ga Dokinsa Baya Nan Ya Ce;"Ina Doki Na???"

Sai Muhammadul Ghali(R.A) Ya Ce: Na Bawa Wani Sharifi Ne Dokinka Hadiya.

Da Jin Haka Sai Shehu Umarul-Futy(R.A) Ya Ce;

"ALHAMDU LILLAHI! INA MA ACE NI NE DOKIN DA AKA BAIWA WANNAN SHARIFI HADIYA YA HAU BAYA NA".

Take Ya Nuna Farin Cikinsa Da Hakan, Ya Yiwa Shehunsa Godiya S**a Yi Sallama Ya Koma Gida.

To Fa Kun Ji Yanda Manyan Salihan Bayin ALLAH Suke Girmama Sharifai(Jinin ANNABI(S.A.W) Da Shehunansu.

ALLAH Ya 'Kara Mana Soyayyar Ahlul-Bayti(A.S) Da Waliyai Ya Bamu 'Karfin Yi Musu Hidima, Ya Ba Mu Albarkar Masu Albarka Irinsu Mujahid Sheikh Umarul-Futy(R.A) Ameeen👌🙏🙏









#

02/07/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Hayatu Yahaya, Aliyu Suleiman, Alhaji Sulaiman Minkail Abdullahi, Timothy Agwu, Abubakar Baffa, Yahaya Sani Randy, Malan Na Lawan Muslum, Aliyu Mai Dankunne, Shehu Ali Garba, Zairat Dahiru, Aliyu Isiyaku, Abdullahi Cisse, Masaudu Abdullahi, Bello Ricardo, Isah Bauchi, Muhammad Shafii Aliyu, Baba Sule Maqeri, Aliyu Yusuf, Sani Abubakar Dattijo, Usman Mai Unguwa Gwanji, Nurwa Aee'sha, Alhaji Auwalun Jarma, Ibrahim Yahaya Dambatta, Talban Jamaa, Wali Randa, Alhaji Sabiu Kaya, Alhaji Muhammad Maiha, Ibrahim Barawa, Opphicial Sisty Dan Umma, Sa'adatu Dayyabu, S Isah Riga, Ado Umar, Abdullahi Muhammad Gali Snk, Mohammed Saleh, Isiyaqa Abubakar Mandera, Sulaiman Imiran, Yusuf Suleiman, Sagiru Hassan, Isah Ahmadu, Garba Ibrahim, Lawan Ahmed Ahmed Lawan, Igwe Innocent, Zainab M Salihu, Goni Abubakar, Bashir Dauda Yarima, Haruna Namadi Gajida, Auwalu Aminu, Daniella Kwarteng, Musa Salenababa, Khadija Umar Uba

Address

Kano

Telephone

+2347048664095

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bahrul faidah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bahrul faidah:

Share