Muryar ‘Yanci

  • Home
  • Muryar ‘Yanci

Muryar ‘Yanci Domin samun ingantattu, tabbatattun labaru da dumi-dumin su. A biyo mu a wannan shafi don sanin abinda ya shafi labarun yau da kullum.

MURYAR YANCI  "Dole Gwamnatin Tinubu Ta Rage Wa Ƴan Najeriya Raɗaɗin Da Suke Ciki" - Okonjo-IwealaWaɗannan, dama ƙarin w...
15/08/2025

MURYAR YANCI


"Dole Gwamnatin Tinubu Ta Rage Wa Ƴan Najeriya Raɗaɗin Da Suke Ciki"
- Okonjo-Iweala

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

SPONSORED: Gwamnan Jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf Ya Halarci Taron Kamfen na Zaben Cike Gurbi a Bagwai/ShanonoMai Girma...
14/08/2025

SPONSORED: Gwamnan Jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf Ya Halarci Taron Kamfen na Zaben Cike Gurbi a Bagwai/Shanono

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kasance a cikin jerin manyan bakin da s**a halarci taron kamfen na zaben cike gurbi na mazabar Bagwai/Shanono, wanda ake shirin gudanarwa a makonni masu zuwa. Taron, wanda aka shirya a babban filin taro na Bagwai, ya jawo hankalin dubban magoya baya daga yankuna daban-daban na mazabar, ciki har da tsofaffi, matasa, da mata masu kishin jam’iyyar NNPP.

Gwamnan Jihar Kano ya isa wurin taron cikin rakiyar wasu jiga-jigan gwamnati da jam’iyyar, ciki har da ’yan majalisar dokoki na jiha, kwamishinoni, shugabannin kananan hukumomi, da sauran masu rike da mukamai. Wurin taron ya cika da raye-rayen wakokin siyasa, tutoci da alamomin NNPP, inda jama’a s**a nuna farin ciki da karɓar bakuncin gwamnan.

A cikin jawabin sa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga mazauna Bagwai da Shanono da su fito cikin kwarin gwiwa domin kada kuri’a ga dan takarar jam’iyyar NNPP a zaben cike gurbin da ke tafe. Ya yi alkawarin cewa idan jam’iyyar ta samu nasara, mazabar za ta samu ci gaba ta fuskar ayyukan raya kasa, kamar hanyoyi, kiwon lafiya, ilimi, da samar da ruwan sha mai tsafta.

Ya kara da cewa, “Mun zo nan ba kawai don neman kuri’a ba, amma don tabbatar da cewa al’umman Bagwai da Shanono suna cikin jerin wadanda za su more ingantaccen rayuwa a karkashin wannan gwamnati. Wannan zabe dama ce ta tabbatar da cewa ana bin sahihin tafarkin ci gaba.”

Bugu da kari, Gwamnan ya yi nuni da cewa gwamnati tana da shirin bunkasa tattalin arzikin yankunan karkara ta hanyar tallafawa manoma, sana’o’in mata, da horar da matasa kan sana’o’in dogaro da kai.

Taron ya gudana cikin natsuwa, tare da samun tsaro mai kyau daga jami’an tsaro, kuma ya kasance wani dandali na haduwa da juna ga magoya bayan jam’iyyar da s**a fito daga Bagwai, Shanono, da sauran wurare.

‘MURYAR YANCI’ “Tattalin Arziƙin Najeriya Na Samun Ƙarin Daraja A Idon Duniya” – Inji MinistaWaɗannan, dama ƙarin wasu l...
13/08/2025

‘MURYAR YANCI’


“Tattalin Arziƙin Najeriya Na Samun Ƙarin Daraja A Idon Duniya”
– Inji Minista

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

‘MURYAR YANCI’  Jami’an Hukumar EFCC Sun Tsare Aminu Waziri Tambuwal, Tsohon Gwamnan SakkwatoWaɗannan, dama ƙarin wasu l...
12/08/2025

‘MURYAR YANCI’


Jami’an Hukumar EFCC Sun Tsare Aminu Waziri Tambuwal, Tsohon Gwamnan Sakkwato

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

‘MURYAR YANCI’  Atiku Ya Jinkirta Yankar Katin ADC, bayan Raɗe-Raɗin Zawarcin Jonathan Da Aka Ce Jam’iyyar Na Yi Waɗanna...
11/08/2025

‘MURYAR YANCI’



Atiku Ya Jinkirta Yankar Katin ADC, bayan Raɗe-Raɗin Zawarcin Jonathan Da Aka Ce Jam’iyyar Na Yi

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu

https://www.muryaryanci.ng

‘MURYAR YANCI’  Zamfara: Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ta’addancin ‘YanBindigaWaɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk ...
08/08/2025

‘MURYAR YANCI’


Zamfara: Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ta’addancin ‘YanBindiga

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

‘MURYAR YANCI’ Kungiyar NBMOA Ta Yi Allah-Wadai Da Umarnin Gwamnan Jihar Neja Ya Bayar Na Rufe Gidan Rediyon Badeggi FMW...
03/08/2025

‘MURYAR YANCI’


Kungiyar NBMOA Ta Yi Allah-Wadai Da Umarnin Gwamnan Jihar Neja Ya Bayar Na Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

MURYAR YANCI Ɓata Al’adun Hausa: ACF Tayi Kira Ga Tinubu, Abba-Yusuf Da Su Dakatar Da Shirye-Shiryin AREWA24 A Jihar Kan...
02/08/2025

MURYAR YANCI



Ɓata Al’adun Hausa:

ACF Tayi Kira Ga Tinubu, Abba-Yusuf Da Su Dakatar Da Shirye-Shiryin AREWA24 A Jihar Kano

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

Bata Al’adun Hausa: ACF ta yi kira ga Tinubu da Abba Yusuf da su Dakatar da Shirye-shiryen AREWA24 a Jihar Kano Kungiyar...
02/08/2025

Bata Al’adun Hausa: ACF ta yi kira ga Tinubu da Abba Yusuf da su Dakatar da Shirye-shiryen AREWA24 a Jihar Kano

Kungiyar Tuntuba ta Arewa wato ACF ta yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Abba Kabir Yusuf da su dakatar da tashar AREWA24 watsa shirye-shiye a Kano saboda bata sunan Hausawa da al’adunsu a shirye-shryen fina-finai.

Sannan kungiya ta yaba tare wa Hukumar Tace Fina-Finan Kano da ta haramta sanya wasu fina-finan Hausa guda 20 a tashar AREWA24, da sauran tashoshi.

Alhaji Danjuma Hassan daya daga cikin ‘ya’yan Kungiyar daga jihar Kano a wajen taron kwanaki 2 da gidaumiyar tunawa da Sardauna ta shirya a Kaduna, ya yabawa Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano bisa Haramta sanya Fina-Finai sama da 22 da gidan Talabijin na AREWA24 ke shiryawa, tare da yin kira ga maigirma gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf da ya dakatar da AREWA24 daga haramtaccen kasuwancin da take yi a farfajiyar gidan Talabijin na Kano ba bisa ka'ida ba wato ARTV.

Ya kuma kara yin kira da kakkausar murya ga Shugaba Bola Tinubu da ya haramtawa AREWA24 watsa shirye-shiryen da take yi a Najeriya gaba daya, ba tare da mallaki lasisin Hukumar Bayar da Lasisin izinin kafa gidajen WatsA Labarai ta Kasa wato NBC, domin ta karya dokar NBC, da ta Hukumar Tantance Tallace-tallace ARCON Laws, EFCC & Tax Laws Nigerian Local Local Content da Nigeria First Manufofin da za su cutar da Al’ummar Jihar Kano da jama’ar Arewa maso Yamma da Nijeriya baki daya.

Ya ci gaba cewa, bayan sahfe tsawon shekaru masu yawa tashar tana kasuwanci a cikin birnin kasuwanci na Kano tare da kiyasin cewa ta samu kudaden shiga na Talla sama da dala miliyan 200, sannan Bayahuden Amurkan da ya mallaki tashar har yanzu ya ki bin ka’idojin Gwamnatin
Tarayyar Najeriya da manufofin ci gaban ‘yan Najeriya da na al’ummar Hausawan Kano da jama’ar Arewa Maso Yamma a matsayin masu hannun-jari ko shugabannin gudanarwa ko kuma Daraktocin Kamfanonin na AREWA24.
Sannan Hassan ya kara cewa, fina-finan da Hukumar Tace Fina-Finan Kano ta haramta sanya su, ana kallonsu sosai a tashar talabijin ta AREWA24 da kuma kafafen sada zumunta na zamani, wadanda sun sa jama’a na ta gunani game da rawar da ya kamata Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Kasa da cibiyoyin kula da tallace-tallace ke takawa wajen hana samun ‘yancin.

A kamar yanda na fada a baya ne, kwanakin baya Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano ta dakatar da sanya wasu jerin fina-finan Hausa guda 22 da s**a hada da Labarina da Dadin Kowa. Wannan ya dogara ne akan zarge-zargen keta dokokin da aka kafa tashar.
Shugaban wannan hukumar Abba El-Mustapha, ya sanar da wannan umarni kwanakin baya.

A wata tattaunawa ta kai-tsaye da jami’in yada labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya bayyana cewa bangarorin da abin ya shafa sun gaza ne wajen kin yarda da tantancewar da dokar jihar ta bukata kafin rabawa ko watsa shirye-shiryen a kafafen sadarwa.

"Hukumar ta dakatar da jerin fina-finan Hausan ne guda 22 saboda saba wa ka'idojin mu, wanda ke bukatar a gabatar da dukkan fina-finan a gaban hukumar don tantancewa kafin a sake su shiga kasuwanni da cikin jama’a," in ji Sulaiman.

Daga cikin jerin fina-finan da abin ya shafa sun hada da: Dakin Amarya da Mashahuri da Gidan Sarauta da Wasiyya da Tawakkaltu da Mijina da Wani Zamani da Labarina da Mallaka da Kudin Ruwa ad Boka Ko Malam da Wa Yasan Gobe da Rana Dubu da Manyan Matada da Fatake da Gwarwashi ad Jamilun Jiddan da Shahadar Nabila da Dadin Kowa da Tabarma da Kishiyata da kuma Rigar Aro.

Sulaiman ya jaddada matsayin Hukumar na hakki kula da duk wani nau'i na labarun da za a maida shi na gani don amfanin jama'a a ciki da wajen iyakokin Kano.
Daga nan sai ya kara da cewa, “An umurci furodusoshi da su daina watsa shirye-shiryensu ko yada su a talabijin ko wasu hanyoyi na yanar gizo har sai sun gabatar da su an tantance daga ranar Litinin, 19 ga Mayu, 2025.

Tsawatarwa

Ya ce, rashin bin umarnin hukumar cikin wa’adin da aka kayyade, to lallai zai haifar da shigowar daukar mataki na shari’a.

“Sannan kuma ya yi kira ga tashar AREWA24 TV da dukkan gidajen Talabijin da Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Kasa (NBC) da su goyi bayan kokarin Hukumar, na ganin an bi wadannan ka’idoji da kuma taimakawa wajen ciyar da masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood gaba.

Hukumar ta kuma yi kira ga hukumomin kasa da su farka don gudanar da ayyukansu kan kafafen watsa labarai don tallafawa aiwatar da ka’idojin tantancewa domin samun ci gaba.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Muna kira ga gidajen Talabijin da Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Najeriya (NBC) da su tallafa wa kokarin da muke yi na tabbatar da bin ka’idojin, wanda hakan zai kawo ci gaba da kuma bunkasa a masana’antar Kannywood.

Wannan mataki na daya daga cikin sabbin yunƙurin da gwamnatin jihar Kano ke yi na tsaftacewa da sake fasalin masana'antar fina-finai ta Kannywood, tare da sanya da’a a tsakanin masu samar da fina-finan na talabijin da kafafen sada zumunta na zamani.

Fina-finan da abin ya shafa, wanda aka fi kallo a tashoshi na gida da kuma dandalin sada zumunta, wadanda s**a haifar da muhawara tsakanin jama'a game da rawar da doka ke takawa kan barin irin su suna shiga cikin jama’a barkatai.

Kuma hukumar ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da bin ka’idojin da da’a da kuma kiyaye bin al’adu wajen samar da abubuwan da s**a shafi Hausa da Hausawa.

Liberty TV National Studio& Liberty FM Stations in Kaduna Abuja and Kano Presents INA-DALILIASSESSING SARDAUNA MEMORIAL ...
31/07/2025

Liberty TV National Studio
&
Liberty FM Stations in Kaduna Abuja and Kano
Presents INA-DALILI

ASSESSING SARDAUNA MEMORIAL FOUNDATION 2025 PARLEY

Today Thursday 31st July 2025
Time:11am

In English at 4pm in Liberty politicsNow

*Universal Streaming on LibertyTVR page

LIBERTY TV DA FM RADIO “TASHOCIN YANCI” A KADUNA, ABUJA, DA KANOZasu Gabatar muku da Shiri na Musamman akan Gwamnatin Ma...
25/07/2025

LIBERTY TV
DA
FM RADIO “TASHOCIN YANCI” A KADUNA, ABUJA,
DA KANO

Zasu Gabatar muku da Shiri na Musamman akan Gwamnatin Malam Uba Sani mai suna

“MATAKIN NASARA”

Wanda SAY ya ɗauki nauyi domin nuna abubuwan cigaba da Mai girma Gwamnan yake yi

Ran Asabar 26 July da Karfe 2pm-3pm

Maimatwa Lahadi 27 July 2025 da Karfe 2pm-3pm

Za a nuna ne a

Liberty TV
A Kan Decoders na
*Startimes Channel 180,
*GOTV Channel 137,
*FGN FreeTV Channels
*NIGCOMSAT Free-to-Air


Da kuma shafukan mu na sada zumunta

- FB Tashar Yanci TVR

- YOUTUBE Liberty TV

- Tiktok Liberty TV Radio

- Liberty Radio Kaduna Kano Abuja (Radio Garden)

Da kuma tashoshin Liberty Radio dake Kaduna, Kano da birnin Abuja

- Tashar yanci 103.1fm Kaduna
Liberty Radio 103.FM Abuja
Liberty Radio 103.3FM kano

MURYAR YANCI  Jam'iyyar APC Na Gab Da Samun Gagarumin Rinjaye A Majalisar ƘasarWaɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ...
24/07/2025

MURYAR YANCI


Jam'iyyar APC Na Gab Da Samun Gagarumin Rinjaye A Majalisar Ƙasar

Waɗannan, dama ƙarin wasu labaran duk za ku same su a adireshinmu
https://www.muryaryanci.ng

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar ‘Yanci posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Muryar ‘Yanci:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share