Zamfara Online

  • Home
  • Zamfara Online

Zamfara Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Zamfara Online, Newspaper, .

Kudiri da hangen nesan Danfulani na cigaba da farfado da daraja da kimar hukumar NAIC, in ji kungiyar masu ruwa da tsaki...
30/07/2025

Kudiri da hangen nesan Danfulani na cigaba da farfado da daraja da kimar hukumar NAIC, in ji kungiyar masu ruwa da tsaki kan noma

Wata kungiya mai suna Forum of Agricultural Stakeholders in Nigeria ta jinjina wa Dr. Yazid Shehu Umar Danfulani, Shugaban Hukumar Inshorar Harkokin Noma ta Nijeriya NAIC, bisa yadda ya dawo da kima da msrtabar hukumar.

Yayin wani taron manema labarai, Shugaban Kungiyar, Mr Olayinka Omolaye, ya bayyana shugabancin Dr. Danfulani a matsayin mai kawo sauyi kuma mai hangen nesa.

Ya ce hukumar NAIC, wadda a da ta sha fama da matsalolin karancin kudi da kayan aiki, a yanzu haka tana fuskantar wani cigaba na musamman karkashin jagorancin Danfulani.

“Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi zabin shugaban hukumar cikin hikima da ya nada Dr. Danfulani. Jagorancinsa mai cike da kwazo da jajircewa yana dawo da darajar hukumar NAIC,” in ji Omolaye.

A cewarsa, ma’aikatan hukumar NAIC da kansu sun tabbatar da canje-canje masu ma’ana da ake samu a cikin hukumar.

Kungiyar ta bayyana cewa gyare-gyaren da Danfulani ke aiwatarwa na kan tafarkin sake gina hukumar NAIC don ta zama wata muhimmiya a yaki da rashin abinci a kasa.

An bukaci manoma daga sassa daban-daban na Nijeriya da su goyi bayan hangen nesan Danfulani yayin da yake kokarin kafa sahihin yanayi mai dorewa da ke cike da sabbin dabarun inganta harkar noma.

Kungiyar ta kuma bayyana cikakken goyon bayanta ga sauye-sauyen da hukumar NAIC ke yi, tare da kira ga duk masu ruwa da tsaki a harkar noma da su mara wa hukumar baya.

Tare da Danfulani a matsayin shugaba, kungiyar ta bayyana tabbacin cewa NAIC za ta ba da gudunmuwa sosai wajen tabbatar da wadatar abinci a lungu da sako na Nijeriya.

Kungiyoyin fararen hula sun yi jinjina ga Ministan tsaro Matawalle kan kyakkyawan jagoranci wajen yakar matsalolin tsaro...
30/07/2025

Kungiyoyin fararen hula sun yi jinjina ga Ministan tsaro Matawalle kan kyakkyawan jagoranci wajen yakar matsalolin tsaro

Kungiyar nan mai rajin tabbatar da dimokradiyya da shugabanci na adalci 'Democracy and Good Governance Group' ta jinjina wa Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Dr. Bello Mohammed Matawalle, MON, bisa irin tsarin da ya kawo wajen fuskantar kalubalen tsaron da ke addabar wasu sassan Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da kakakin kungiyar, Mr Daniel Samuel, ya fitar a Abuja ranar Alhamis, ya yaba wa Dr. Matawalle bisa yadda ya bullo da "tsari mai kyau da aiki yadda ya k**ata" tun bayan da ya hau kujerar, lamarin da kungiyar ta bayyana a matsayin juyin juya hali a harkokin tsaron cikin gida a kasar.

Kungiyar ta nuna jin dadinta kan yadda Ministan ya gaza zaune ya gaza tsaye a ayyukan soji da ke kan gaba da kuma yadda yake sa ido kan dabarun tsaron cikin gida, tare da cewa hakan ya haifar da sak**ako mai gamsarwa a yankunan da ke fama da tashin hankali.

“Tun da aka nada Dr. Matawalle wannan mukami, ya yi jagorancin da aka samu gagarumar nasara a ayyukan soji da ake gudanarwa a Arewa maso Yamma, Arewa maso Gabas, da wasu yankunan da ke fama da balahirar tsaro,” in ji sanarwar. “An samu daidaito, tare da samun dabarun tura jami’ai masu kwarewa, da hadin guiwa tsakanin hukumomin tsaro, wanda hakan ya rage hare-haren ‘yan ta’adda, satar mutane da sauran aikata manyan laifuka.”

Haka kuma kungiyar ta yaba da yadda Ministan ke mai da hankali kan amfani da bayanan sirri da kuma hada kai da al’umma, abin da ya taimaka wa hukumomin tsaro wajen hana manyan barazana kafin su auku.

Kungiyar ta kuma yi yabo tare da jinjina ga kokarin Dr. Matawalle na karfafa dangantaka tsakanin fararen hula da jami’an tsaro da kuma mayar da hankali wajen tatso bayanai sahihai daga al'umma, wadda ta ce hakan ya taimaka wajen kwantar da hankula mutane da aminci tsakanin jama’a da shirin gwamnatin tarayya na tabbatar da tsaro.

Ƙungiyar ta ce kuma fafutikar Ministan wajen kyautata rayuwar jami’an tsaro ba ta wuce a banza ba. Bisa sanarwar, karin kudaden aiki, inganta yanayin zama a barikin soja, da biyan hakkoki a kan kari sun taimaka wajen karfafa guiwar sojoji a daidai lokacin da kalubalen tsaro ke ci gaba da bayyana.

A bangaren huldar kasashen waje kuwa, Dr. Matawalle yana kara himma wajen habaka diflomasiyyar tsaro ta Nijeriya, musamman ta hanyar hadin guiwa da kasashen makwabta domin fuskantar barazanar da ke kan iyakoki, k**ar safarar mak**ai da ayyukan ta’addanci.

“Jagorancinsa na nuna manufar gwamnati da ke da nufin dawo da zaman lafiya, oda da kuma karfafa amana a cikin ikon gwamnati na kare rayuka da dukiyoyi,” in ji kungiyar.

A karshe, kungiyar ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su ci gaba da mara wa Rundunar Sojoji da sauran hukumomin tsaro baya, tana mai jaddada cewa “zaman lafiya na dindindin yana bukatar hadin kan al’umma, kuma da shugabanni irinsu Dr. Matawalle a sahun gaba, Nijeriya za ta dawo da aminci da martabarta ta fuskar ingancin tsaro.”

29/07/2025

Yan Majalissar Dokokin Zamfara ta koka da halin-ko-in da Gwamna Dauda ke nunawa kan matsalar tsaro

MAZAUNA KAURA NAMODA SUN YI ALLAH-WADAI DA GWAMNA DAUDA LAWAL DARE KAN RASHIN WANI KATABUS DA GWAMNATINSA TA YI YAYIN DA...
29/07/2025

MAZAUNA KAURA NAMODA SUN YI ALLAH-WADAI DA GWAMNA DAUDA LAWAL DARE KAN RASHIN WANI KATABUS DA GWAMNATINSA TA YI YAYIN DA 'YAN BINDIGA S**A HALLAKA MUTANE 38 DA S**A SATA

Al'ummar yankin karamar hukumar Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara sun sake fadawa cikin jimami da alhini. A yankin Banga da ke Kaura Namoda, an tabbatar da mutuwar mutune sama da 35 daga cikin mutane 53 da 'yan ta’adda s**a sace kusan watanni uku da s**a gabata. Duk da cewa an sako ragowar mutanen, al’ummar yankin na cikin bakin ciki, kunci har sun fara jin tamkar babu gwamnati a tattare da su.

Wannan kisan kiyashin ya sake nuna gazawar Gwamna Dauda Lawal Dare, wanda har yanzu ke nuna halin ko-in-kula, rashin tausayi, da kuma gazawa wajen daukar matakin da ya dace tun daga lokacin da ya hau mulki. A matsayinsa na Babban wanda nauyin kare rayukka da dukiyoyin al'ummar Jihar Zamfara, gwamnan ya dai gaza matuka wajen hana aikata wannan ta’asa, ya ma yi biris da duk halin da al'umma ke ciki. Tsawon watanni uku, iyalan wadanda aka sace suna neman agaji, suna neman taimako, amma gwamna bai ce uffan ba, ya yi gum da bakinsa. Yanzu haka an yi asarar rayukan mutune 38, an yi musu yankan rago, yayin da gwamnatin jiha ke kallo ba tare da ta yi komai ba.

A cikin shekaru biyu da s**a gabata, dubban mutane a fadin jihar Zamfara aka yi garkuwa da su, inda 'yan bindiga s**a karbi fiye da naira bilyan hudu N4bn a matsayin kudin fansa daga iyalan wadanda aka sace. Duk da wadannan alkaluman masu razani da rikitarwa, Gwamna Dauda Lawal Dare bai taba kai ziyara ko tura wakilai zuwa wuraren da abin ya shafa domin jajantawa ko ba da tabbacin wani mataki ba daga gwamnatin jiha ba. Wannan ba kawai gazawa ba ce, cin amanar jama’a ce kai tsaye, da kuma saba wa rantsuwar da ya sha ta ofis.

Ya k**ata a tunatar da jama’a cewa kafin zaben 2023, Dauda Lawal ya sha alwashin kawo karshen matsalar rashin tsaro a fadin jihar Zamfara cikin makonni biyu, ko kuma akalla wata guda, idan aka zabe shi. Yanzu shekara fiye da biyu kenan da ya hau mulki, amma lamarin tsaro ma sai kara tabarbarewa yake yi. Alkawuransa sun zama shafa labari shuni ne kawai na an yi su ne don yakin neman zabe a lokacin. Mutanen Kaura Namoda, da ma jihar Zamfara gaba daya, sun gaji da yaudarar da Dauda ke musu.

Amma sabanin haka, jama’a na yabawa tare da godiya ga irin kokarin da Gwamnatin Tarayya ke yi, musamman matakan da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kuma ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Dr. Bello Muhammad Matawalle ke dauka. Ayyukansu na dawo da zaman lafiya a Arewa maso Yamma a bayyane suke kuma ana yaba musu. Sai dai wannan kokari na fuskantar cikas daga rashin hadin kai, rashin kulawa, da rashin jajircewar Gwamnatin Jihar Zamfara.

Mutanen Kaura Namoda ba wai cewa a yi sha yanzu, magani yanzu ba ne, a'a, suna neman shugabanci, daukar nauyi da kuma daukar matakin da ya dace. Gwamna Dauda Lawal Dare ya k**ata ya fuskanci cewa ya gaza, ya amsa kiran jama’a kan jin kudurinsa da alkawuran da ya saba, da kuma rayukan da ake ci gaba da rasawa a karkashin mulkinsa.

Tura ta kai bango, ya isa haka. Lokacin bayar da uzuri ya wuce. Jama’a na neman tsaro, adalci, da gwamnati mai kulawa. Cewar Abubakar Sani Salisu

Mazauna yankin Sabon Birni sun yaba wa Shugaba Tinubu, Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Matawalle da Janar Mus...
28/07/2025

Mazauna yankin Sabon Birni sun yaba wa Shugaba Tinubu, Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Matawalle da Janar Musa bisa kakkabe sanannen dan bindigar nan Kachalla Dan Dari Biyar da karin wasu

An samu karin gagarumar nasara a yaki da 'yan bindiga a Jihar Sokoto, yayin da jami'an tsaro s**a yi nasarar halaka wani shahararren dan bindiga da aka fi sani da Dan Dari Biyar a wani samame da aka gudanar a yankunan Turtsawa, Mazau da Zango na karamar hukumar Sabon Birni. Jami'an tsaron dai sun yi nasarar kashe shi ne a lokacin da yake kokarin karbar kudin fansa daga iyalan wasy da aka sace aka yi garkuwa da su.

Dan Dari Biyar ya samu wannan mummunan suna ne saboda munanan kalamansa da ya saba furtawa ga wadanda ya k**a yake garkuwa da su, yana cewa ya fi son naira dari biyar fiye da rayuwar wanda ya k**a ya tsare. Ya dai shahara ne wajen aikata ta’asa a dazukan Tidibale, Lalle, Tsamaye har cikin dazukan Goronyo da Gundumi. Shi ne kuma ya jagoranci mummunan hari da kone kauyen Gidan Sale.

Wannan nasara ta biyo bayan ziyarar manyan jami’an tsaro zuwa Sokoto, ciki har da Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle da Babban Hafsan Tsaro na Ƙasa, Janar Christopher Musa. A yayin ziyarar, Matawalle ya bukaci dakarun soji da su tabbatar da dawo da zaman lafiya mai dorewa ba kawai a Sokoto ba, har da dukkan yankin Arewa maso Yamma. Tun daga lokacin, dakarun soji s**a kara azama wajen zafafa farmaki a fadin yankin, wanda ya haifar da hallaka da dama daga cikin fitattun ‘yan ta’adda, ciki har da Halilu Sububu.

Wannan jerin nasarori na nuni da ingantacciyar dabarar soji a karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, Minista Matawalle da CDS Janar Musa.

Masu sharhi kan harkokin yau da kullum dai na ganin ‘yan Nijeriya sun fara jin tasirin gwamnati mai kishin kare rayuka da dukiyarsu. S**a yi addu'ar Allah ya ci gaba da ba su nasara wajen tabbatar da zaman lafiya, adalci da tsaro a kasar nan.

Matawalle ya kai ziyara kamfanin kera mak**ai na MKE a birnin Istanbul na kasar TurkiyyaMinistan kasa a ma'aikatar tsaro...
27/07/2025

Matawalle ya kai ziyara kamfanin kera mak**ai na MKE a birnin Istanbul na kasar Turkiyya

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya kai ziyara kamfanin kera mak**ai na kasar Turkiyya, Makine ve Kimya Endüstrisi (MKE), da ke birnin Istanbul, a wani bangare na halartar bikin baje kolin masana'antar tsaro na duniya, IDEF 2025.

Kamfanin MKE, daya daga cikin manyan kamfanonin gwamnati masu kera mak**ai a Turkiyya, ya shahara wajen samar da manyan mak**ai, harsasai da kuma tsarin kare kasa na zamani da s**a zama ginshikin tsaron kasar.

Matawalle, wanda ya jagoranci tawagar manyan jami'ai daga Nijeriya zuwa baje kolin, ya samu tarba daga Shugaban kamfanin MKE, Ilhami Keleş. Sun kuma tattauna kan sabbin kirkire-kirkiren aikin soja, dogaro da kai a fannin kera kayan tsaro, da kuma yiwuwar hada guiwa tsakanin Nijeriya da Turkiyya a fannin masana'antar tsaro.

Wata sanarwa daga mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Ahmad Dan-Wudil, ta tabbatar da cewa ziyarar na da nufin nazarin sabbin fasahohin da ke tasowa tare da gano wuraren da za a iya yin hadin guiwa da Turkiyya don amfanin Nijeriya.

Kamfanin MKE yana da matukar muhimmanci a kokarin da Turkiyya ke yi na dogaro da kai a bangaren tsaro. Ya zama daya daga cikin manyan ginshikai a kasuwar kayayyakin tsaro ta duniya, inda ke samar da sabbin hanyoyin tsaro na kasa da kasa a fannonin kasa, sama da teku.

Ya ce, “Hadin guiwar Nijeriya da kamfanin MKE na nuna burin Nijeriya na farfado da masana’antun kera kayan tsaro a cikin gida tare da rage dogaro da kasashen waje wajen samun mak**ai.”

“Ziyarar na daya daga cikin muhimman ayyuka da Nijeriya ke gudanarwa a wannan baje koli karo na 17 na IDEF 2025, wanda ke tattara kamfanoni fiye da 900 daga Turkiyya da wasu kamfanoni 400 na kasashen waje daga kasashe 44.”

Tawagar Nijeriya ta hada da Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Amb Gabriel Tanimu Aduda; Mataimakin Shugaban Hukumar Leken Asirin Soji, wakilin Shugaban Hafsan Hafsoshin Sojin Sama AVM Yusuf; Manjo Janar B.I Alaya; da Darakta-Janar na kamfanin DICON, Birgediya Janar M.L Abubakar.

A yayin ziyarar, tawagar ta zagaya rumfunan baje koli domin duba sabbin fasahohi da kuma gano hanyoyin hadin guiwa nan gaba a fannin tsaro da kariya.

Matawalle kuma na shirin ci gaba da wasu muhimman tattaunawar bangarori biyu da shugabannin tsaro daga wasu kasashe, ciki har da takwarorinsa na Azerbaijan da Turkiyya, a yayin wannan baje koli.

HAZIƘIN ƊAN MAJALISAR JIHA A ZAMFARA YA RABAWA MUTANE 14 NAIRA MILIYA 10 DON SU KARA JARIN KASUWANCI.Haziƙin ɗan majalis...
26/07/2025

HAZIƘIN ƊAN MAJALISAR JIHA A ZAMFARA YA RABAWA MUTANE 14 NAIRA MILIYA 10 DON SU KARA JARIN KASUWANCI.

Haziƙin ɗan majalisar dokokin jihar Zamfara Hon. Shamsudden Hassan Basko ya rabawa matasa daga yankin da ya ke wakilta na Talata Mafara ta Arewa, kyautar kuɗi har Naira miliyan 10 don sun ƙara jari a kasuwancinsu.

Matashin ɗan majalisar ya bayyana cewa "bayar da wannan jari ya biyo bayan nazarin da ya yi na na ganin cewa a wannan zamani ba abin da za ka yi wa matashi irin ka koya masa hanyar da zai dogara da kansa. Wanda haka ne ya sa na zaƙalo matasa 14 da na san suna kan kasuwanci amma suna da ƙaramin jari na raba masu waɗannnan kuɗaɗe.

Ɗan majalisar ya ƙara jaddada cewa wasu sun amfana da Naira miliyan ɗaya-ɗaya wasu kuma dubu ɗari biyar-biyar wasu dubu ɗari biyu-biyu.

Ɗan majalisar ya bayyana cewa wannan soman taɓi ne akan ƙoƙarin da ya ke yi na taimakon matasan da su ke yankin nasa. Don haka ya yi kira ga waɗanda s**a amfana da su yi amfani da waɗannan kuɗaɗe domin cigaban kasuwancinsu ta yadda nan gaba za su iya taimakon wasu.

Daga nan ya yi kira ga waɗanda ba su samu ba da su yi hakuri su ma sannu layi zai kawo gare su.

Matasan da s**a amfana ɗin sun bayyana matuƙar jin daɗinsu ga wanann ɗan majalisar tare da roƙon Allah ya ɗaukaka shi. Tare da masa fatan alheri da alƙawarin yi masa biyayya da jam'iyarsa ta Apc.

Matawalle da Güler sun jaddada dangantakar tsaro tsakanin Nijeriya da TurkiyyaKasashen Nijeriya da Turkiyya sun sake jad...
25/07/2025

Matawalle da Güler sun jaddada dangantakar tsaro tsakanin Nijeriya da Turkiyya

Kasashen Nijeriya da Turkiyya sun sake jaddada kudurinsu na ci gaba da karfafa dangantakar soji, bayan wata ganawa a bikin baje kolin kayan aikin tsaro na duniya karo na 17 (IDEF 2025) da ke gudana a birnin Istanbul.

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya gana da Ministan tsaron kasar Turkiyya, Yaşar Güler, a ranar Laraba, domin zurfafa hadin guiwar tsaro tsakanin kasashen biyu.

An gudanar da ganawar a yayin taron IDEF 2025, inda s**a tattauna kan manyan fannoni k**ar hadin guiwa a bangaren masana’antar tsaro, musayar fasaha da kuma sayen sabbin kayan aikin soja na zamani.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Matawalle kan harkokin yada labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar ta bayyana cewa an tattauna kan sayen motocin yaki, jiragen yaki, jiragen ruwa na yaki, jiragen yaki marasa matuki (UAVs), tsarin radar da kuma kunshin horo da gyare-gyare na kayan aikin soja.

Ministocin biyu sun jaddada muhimmancin karfafa ikon masana’antar tsaro a cikin gida, tare da bayyana sha’awar hadin guiwa ta dogon lokaci a fannin masana’antu domin cimma cin gashin kai ta fuskar fasaha.

Dr Matawalle ya bayyana kasar Turkiyya a matsayin amintacciya kuma abokiyar hadin guiwa a kokarin Nijeriya na sabunta tsarin tsaronta, yana mai cewa ci gaba da wannan hadin guiwa zai amfanar da kasashen biyu musamman a wannan lokaci da duniya ke fuskantar kalubalen tsaro.

Daga cikin wadanda s**a halarci taron akwai manyan jami’an tsaron Nijeriya, ciki har da Amb Gabriel Tanimu Aduda, babban sakatare na ma’aikatar tsaron Nijeriya; AVM Yusuf, wakilin Shugaban Hafsan Sojin Sama; Manjo Janar B.I. Alaya, Darakta Janar na Kamfanin Kera Kayan Aikin Soja na Nijeriya (DICON); Birgediya Janar M.L. Abubakar, Jakadan Tsaro na Nijeriya a Turkiyya; da kuma Mataimakin Shugaban Harkokin Leken Asirin Soja.

A halin yanzu, baje kolin bikin IDEF 2025, daya daga cikin manyan baje kolin kayan aikin soja na duniya, ya fara ne a ranar 22 ga Yuli kuma zai ci gaba har zuwa 27 ga Yuli a birnin Istanbul. Taron yana tattaro masana’antun kayan soji, jami’an soja da masu tsara manufofi daga sassa daban-daban na duniya domin karfafa hadin guiwar kasa da kasa.

Mazauna yankin karamar hukumar Maru sun yabi Shugaba Tinubu, Ministan Tsaro Matawalle da babban hafsan soji Janar Musa k...
25/07/2025

Mazauna yankin karamar hukumar Maru sun yabi Shugaba Tinubu, Ministan Tsaro Matawalle da babban hafsan soji Janar Musa kan dawo da tsaro a yankinsu

Mazauna yankin karamar hukumar Maru da ke jihar Zamfara sun bayyana godiyarsu ta musamman ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, da Babban Hafsan Tsaro na Ƙasa, Janar Christopher Musa, bisa gagarumar gudunmawarsu wajen kawo karshen matsalar tsaro da ta dade tana addabar yankin.

A cewar jama'ar yankin, tun daga shekarar 2023, karamar hukumar Maru na fama da hare-haren ‘yan bindiga ba kakkautawa, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, garkuwa da fararen hula da kuma kona majalisar masarautar Maru. Har ila yau, ‘yan ta’addar sun kashe Babban Limamin karamar hukumar.

Duk da koke-koken da s**a sha yi ga gwamnatin jihar, mazauna yankin sun ce ba su ga wani mataki na a zo-a-gani ba. Sai dai al’amura sun fara canzawa ne bayan sun kai koke-kokensu kai tsaye ga Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Matawalle, wanda ya dauki matakin gaggawa wajen tura jami’an tsaro zuwa yankin.

Zuwan jami’an tsaron da fara gudanar da ayyukansu ya kawo kwarin guiwa ga mazauna yankin. Mazauna yankin sun tabbatar da cewa an kashe da dama daga cikin ‘yan bindigar, tare da kwato manyan mak**ai masu yawa a yayin samamen.

Jama’ar karamar hukumar Maru sun mika godiyarsu gare su Shugaba Tinubu, Dr. Matawalle da Janar Christopher Musa bisa wannan gaggawar da s**a dauka da kuma nasarar da ta fara bayyana wajen dawo da zaman lafiya a yankin da aka dade ana fama da matsalolin tsaro.

Mazauna wasu yankuna da dama a karamar hukumar Gusau ta jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Laraba,...
24/07/2025

Mazauna wasu yankuna da dama a karamar hukumar Gusau ta jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Laraba, suna neman daukin gaggawa daga gwamnati don dakile karuwar hare-haren 'yan bindiga a yankunansu.

Zanga-zangar, wadda ta fara da misalin karfe goma sha biyu na rana, ta hada da gungun jama’a masu yawa, wasu a kan babura, wasu cikin motoci, da kuma wasu na tafiya a kasa, s**a ratsa birnin Gusau har s**a isa kofar gidan gwamnatin jihar.

Kauyuka da s**a hada da Mada, Ruwan Bore, Fegin Baza, Bangi, Lilo, Wonaka, da Fegin Mahe sun fuskanci hare-hare sau da dama, inda mazauna yankunan s**a ce sama da mutum 100 ne aka kashe cikin watannin da s**a gabata.

Daya daga cikin masu zanga-zangar, Malam Abubakar Abdullahi daga Fegin Mahe, ya bayyana cewa ya rasa 'yan'uwansa da dama sak**akon rikicin, kuma an kwashe masa kaya da darajarsu ta haura naira miliyan daya daga shagonsa, ciki ha da buhunan taki guda 500.

Haka zalika, rashin tsaro ya dakile harkokin noma, inda mazauna yankunan ke cewa ya zama hadari matuka su fita noma a gonakinsu k**ar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Gabanin taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC (NEC), Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da gwamnoni na jam’iyyar APC a...
23/07/2025

Gabanin taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC (NEC), Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da gwamnoni na jam’iyyar APC a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, a ranar Laraba, 23 ga Yuli, 2025.

23/07/2025

Yan Majalissar zamfara sun koka da rikon sakainar kashin da Gwamna ke yiwa matsalar tsaro da salwantar da dukiyar jihar

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamfara Online:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share