Zamfara Online

  • Home
  • Zamfara Online

Zamfara Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Zamfara Online, Newspaper, .

Matawalle ya nemi agaji da goyon bayan Amurka wajen kula da lafiyar sojojin Nijeriya Ministan kasa a ma'aikatar tsaron N...
23/09/2025

Matawalle ya nemi agaji da goyon bayan Amurka wajen kula da lafiyar sojojin Nijeriya

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Dr Bello Matawalle, ya bukaci Amurka da ta ci gaba da tallafa wa ƙoƙarin ƙarfafa fannin kiwon lafiyar rundunar sojojin Nijeriya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya sanya wa hannu, da aka raba wa manema labarai a Abuja ranar Litinin.

Matawalle ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi tawagar rundunar bincike da ci gaban kiwon lafiyar sojojin Amurka (U.S. Army Medical Research and Development Command) a ma’aikatar tsaron Nijeriya, Ship House, Abuja.

Tawagar, ƙarƙashin jagorancin babbar kwamandar rundunar, Manjo Janar Paula C. Lodi, ta ziyarci Nijeriya ne domin bikin cika shekaru 20 na haɗin gwiwa tsakanin shirin kiwon lafiyar ma’aikatar tsaro ta Nijeriya (MODHIP) da cibiyar binciken rundunar sojojin Amurka ta Walter Reed Africa (WRAIR Africa).

Janar Lodi ta nuna godiya ga minista da Darakta Janar na MODHIP, Brig Janar Solebo, bisa jajircewarsu wajen ci gaba da haɗin gwiwar.

Ta bayyana cewa haɗin gwiwar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta bincike a fannin kiwon lafiyar sojoji da kuma ƙarfafa matakan magani a Nijeriya.

Da yake mayar da jawabi, Matawalle ya yaba wa Amurka bisa ɗorewar haɗin gwiwarta da Nijeriya, inda ya jaddada cewa irin wannan dangantaka na ci gaba da ƙarfafa tsarin kiwon lafiyar tsaron ƙasar.

“Nijeriya da Amurka na da alaƙa mai ƙarfi da ɗorewa, kuma wannan zumunci na ƙara ƙarfi ta hanyar haɗin gwiwa k**ar na MODHIP da WRAIR Africa,” in ji shi.

Ministan ya kuma yi kira na musamman ga ƙarin taimakon Amurka a fannin haɓaka ƙwarewar ma’aikata, wanda ya ce zai ƙara inganta kwarewar kwararrun likitoci na Nijeriya.

Ya kuma yaba wa Janar Solebo bisa jagorancinsa da ya taimaka wajen samun nasarar shirin MODHIP.

A yayin ziyarar, tawagar Amurka za ta ziyarci asibitin soja na 44 da ke Kaduna domin tattaunawa da jami’an lafiya tare da duba ayyukan da ake aiwatarwa.

Sauran mambobin tawagar sun haɗa da Shannon Lucy, Darakta WRAIR – Africa; Monnet Bushner, Command Sergeant Major MRAIR; Ashleigh Roberds, Manjo XO ga babban kwamandan runduna; Sandhya Vasan, VPHJF Global ID (USA); Helina Meri, Darakta WRAIR – Nigeria; Zubairu Aliyu Elayo, Darakta mai rikon kwarya na HJFMRI; da Yakubu Adamu, Mataimakin Darakta ƙasa, WRAIR – Africa-Nigeria.

Matawalle ya tabbatar da ingancin tsaro bayan wata fashewa da aka faru a kamfanin DICON na KadunaMinistan kasa a ma'aika...
22/09/2025

Matawalle ya tabbatar da ingancin tsaro bayan wata fashewa da aka faru a kamfanin DICON na Kaduna

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, a ranar Lahadi ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa kamfanin kera mak**ai na kasa DICON yana nan cikin tsaro da aminci kuma yana aiki yadda ya k**ata duk da fashewar da ta faru a masana’antar a Kaduna.

Matawalle, wanda ya kai ziyara wurin a ranar Asabar, ya ce lamarin yana “cikin cikakken iko da tsari tun bayan fashewar,” tare da rokon jama’a da su yi watsi da rahotannin da ke yawo da ba su da tushe bare mak**a kan abin da ya faru.

Wata sanarwa daga mai taimaka masa a harkokin yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ta bayyana cewa Ministan ya samu bayani daga Darakta Janar na kamfanin DICON, Manjo Janar B.I. Alaya, da kuma Daraktan da ke kula da kere-kere, Air Commodore E. Benson.

A yayin duba wurin, Matawalle ya tabbatar cewa fashewar ta takaita ne a cikin wani dan tsuki da ke dauke mak**an da s**a rigaya s**a lalace ko kuma wa'adin aiki da su ya kare da tuni tawagar kwararru ta shawo kan lamarin cikin gaggawa.

“Babu wata ko da tagar window da ta samu matsala a yayin da lamarin ya faru,” in ji Ministan, ya ƙara da cewa gine-ginen masana’antar, ɗakunan ajiya, rijiyar adana dizal da al’ummomin da ke kewaye ba su sami wani lahani ba.

Ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare lafiya da tsaron ma’aikata, tare da shan alwashin cewa abin da ya faru zai haifar da ƙara tsaurara matakan tsaro bisa tsarin ƙa’idodin duniya.

A halin yanzu, an kafa kwamitin bincike don gano musabbabin fashewar.

Matawalle ya taya matar shugaban kasa Remi Tinubu murnar cika shekaru 65 a duniya...ya bayyana ta a matsayinsu n nagarta...
21/09/2025

Matawalle ya taya matar shugaban kasa Remi Tinubu murnar cika shekaru 65 a duniya
...ya bayyana ta a matsayinsu n nagartacciyar mace da ya k**ata a yi koyi da halayenta...

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Matawalle, ya yi murna da farinciki da kuma yabo ga matar shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, inda ya bayyana ta a matsayin nagartacciya uwar kasa mai tausayi, juriya da karfin hali.

Matawalle ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan hulɗa da manema labarai, Ahmed Dan Wudil, ya fitar a Abuja, ranar Lahadi, domin taya ta murnar zagayowar ranar haihuwarta ta shekara 65 a duniya.

A cewarsa, jajircewar Sanata Remi Tinubu wajen ci gaban ƙasa, karimci da kishinta sun ba ta matsayi mai girma a tarihin Nijeriya.

“Duk lokacin da aka dauko tawwada da alkalami na rubuta tarihin wannan ƙasa mai albarka a kuma mulkin Shugaba Tinubu, tarihin ba zai cika ba, sai sunanki ya bayyana a ciki,” in ji shi.

Ministan ya yaba wa gudummawar Sanata Remi Tinubu a fannin ƙarfafa mata, bunƙasa matasa, ilimi da kuma kula da talakawa, yana mai cewa kulawarta ta kawo cikakkiyar fata da karfafa guiwa a tsakanin mutane masu tarin yawa.

“Karfin hali, juriya da sadaukarwarki ga ƙasarmu mai daraja suna ƙarfafa mu baki ɗaya. Ba wai kawai kin tsaya a matsayin uwargida ba ce, ke ainihin abin koyi ce ga mata da sauran al'umma,” in ji Matawalle.

Ya ƙara da yaba wa haɗin gwiwarta da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, wanda ya bayyana a matsayin jigo kuma ginshiki na ci gaba ga ƙasar nan.

“A yayin da k**e bikin wannan muhimmiyar rana, ina yi miki addu’ar samun lafiya, zaman lafiya da ci gaba da hidimta wa Nijeriya,” in ji Matawalle.

Kungiyar matasan Arewacin Nijeriya ta yabi salon diflomasiyyar inganta tsaro da Matawalle ya bullo da ita .....Jagora ne...
19/09/2025

Kungiyar matasan Arewacin Nijeriya ta yabi salon diflomasiyyar inganta tsaro da Matawalle ya bullo da ita

.....Jagora ne na gudanar da aiki, ba na ba da uzurorin karya ba....in ji kungiyar

Kungiyar matasan Arewacin Nijeriya mai suna Northern Youth Concert Citizen ta bayyana jin daɗinta da nutsuwa ga ire-iren ayyukan da ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawallle ke aiwatarwa, tana mai kiran sa “jagoran gudanar da aiki tukuru, ba na ba da uzurorin babu gaira babu dalili ba” saboda jajircewarsa wajen ƙarfafa diflomasiyyar inganta tsaron Nijeriya.

Shugaban ƙungiyar, Dr. Ibrahim Garba daga Karamar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna, ya ce, “Matawalle ya sake fasalin diflomasiyyar inganta tsaro ta hanyar nuna batutuwan gyaran tsaro a aikace. Daga Turkiyya zuwa China, daga Pakistan zuwa Amurka, ƙoƙarinsa ya samar da kayayyakin aiki na zamani, inganta fasaha da kuma horo na zamani ga rundunar sojinmu.”

Sanarwar ta kuma nuna muhimmancin sababbin jiragen sintiri masu nisan zango, inda ta bayyana su a matsayin wani hangen nesansa da burin kare Nijeriya ta ƙasa, sama da ruwa da Minista Matawalle kebda shi.” Sanarwar ta ƙara da cewa hakan sadaukarwa ce wajen kare kima da martabar ƙasar.

Dr. Garba ya ƙara da cewa, “Ga matasan Arewacin Nijeriya da ke rayuwa a kullum da matsalar tsaro, jagorancin Matawalle ya dawo musu da cikakkiyar fata cewa Nijeriya za ta iya, kuma za ta shawo kan ƙalubalen tsaronta ta hanyar haɗin gwiwar dabaru da kuma ƙarfafa ƙarfin cikin gida.”

A ƙarshe, ƙungiyar ta sake tabbatar da cikakken goyon bayanta ga Ministan Matawalle, tana mai jaddada cewa
“Jajircewarsa na kara sanya kwarin gwiwa a zukatan miliyoyin ’yan kasa, musamman matasa, waɗanda ke fatan ganin ƙasa mai tsaro, ƙarfi da kuma cigaba.”

Kungiyar da ke rajin an gudanar da shugabanci nagari a jihar Zamfara ta ZGGF ta bukaci  Shugaba Tinubu ya daina ba jihar...
17/09/2025

Kungiyar da ke rajin an gudanar da shugabanci nagari a jihar Zamfara ta ZGGF ta bukaci Shugaba Tinubu ya daina ba jihar kudin dauni na tarayya, sannan ya kakaba dokar ta-baci bayan kalaman Gwamna Dauda Lawal

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ZGGF da ke rajin tabbatar da shugabanci na gari a jihar Zamfara ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta dakatar da raba kuɗaɗen tarayya ga jihar Zamfara tare da kafa dokar ta-baci, bisa ga abin da ta bayyana a matsayin mummunar furucin Gwamna Dauda Lawal wanda ya bayyana cewa yana da masaniya kan matsugunnai da maboyar manyan ‘yan bindiga da ke addabar jihar.

Sakataren kungiyar, Muhammad Ibrahim Mafara, ya faɗa wa manema labarai a Gusau cewa wannan ikirarin gwamnan ya zama “cin amanar kasa da kuma babbar gazawa a shugabanci.”

Ya ce “ba wai kawai ganganci ba ne wannan; wannan furuci na nuna tsantsar masaniya dumu-dumu a cikin aikata laifukan ‘yan ta’adda. Idan gwamna mai ci ya fito fili ya ce yana da masaniya kan inda waɗannan ‘yan ta’adda ke rayuwa da yin ta’addanci, amma bai ɗauki mataki ba, to wannan kadai ya tabbatar da laifinsa a gaban jama’a kuma ya tabbatar wa da jama'a zarge-zargen da suke yi a kansa game da ta'addanci.”

Kungiyar ta nuna cewa duk da fiye da Naira miliyan 600 da ake ware wa kowane wata a matsayin kudin tsaro na "security votes" babu wata hujja da gwamna zai ba da cewa ba zai iya kare jama’a ba alhali ana kashe mutane kullum a jihar Zamfara. Mafara ya ce “abin da muke gani yanzu tamkar ciyar da ‘yan ta’adda daga gidan gwamnati ne. Wannan abin kunya ne ga sadaukarwar sojojinmu, kuma abin kunya ga gwamnati da ta gaza kare iyalai da sauran jama'ar da s**a rasa ‘yan uwansu a hannun ‘yan bindiga.”

Kungiyar ta kuma zargi gwamnan da zama bisa tsarin da ake wawushe kuɗaɗen kananan hukumomi, yayin da shugabannin kananan hukumomi ke zaune a Gusau maimakon yin hidima a yankunansu. Mafara ya bayyana furucin gwamnan a matsayin wata dabara ta karkatar da hankali daga gazawar gwamnatinsa da kuma tura laifin kan gwamnatin tarayya.

Saboda haka, kungiyar ZGGF ta goyi bayan kira da aka yi na gudanar da bincike daga hukumomin EFCC, DSS, da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaro, tare da binciken majalisar tarayya kan yadda gwamnan ke tafiyar da sha'anin tsaro da dukiyar jama’a.

Mafara ya ce idan binciken ya tabbatar da cewa Gwamna Lawal na da hannu wajen ba da dama ga ‘yan bindiga, to wajibi ne gwamnatin tarayya ta ɗauki matakin kafa dokar ta-baci domin dawo da zaman lafiya, tsari, da mutunci a jihar.

Ya ƙara da cewa “Jihar Zamfara ta zama filin zubar da jini a lokacin mulkin Gwamna Dauda Lawal. Ana kashe bayin Allah, ana rusa ƙauyuka, gonaki duk sun yi sabra, ba a iya nomawa. Ba za mu ci gaba da shan wahala yayin da gwamna ke buga siyasa da rayukan jama’a ba. Wannan kungiya za ta ci gaba da magana da muryar marasa ƙarfi har sai an ga an yi adalci.”

Kungiyar Arewa Forum ta yaba da jinjina ga shugaban hukumar NAIC Yazid Danfulani kan cikarsa kwanaki 100 a ofisKungiyar ...
15/09/2025

Kungiyar Arewa Forum ta yaba da jinjina ga shugaban hukumar NAIC Yazid Danfulani kan cikarsa kwanaki 100 a ofis

Kungiyar manoma ta Arewa Forum ta yaba wa shugaban hukumar inshorar noma ta kasa NAIC, Yazid Shehu Umar Danfulani, bisa abin da s**a bayyana a matsayin kyakkyawan farko a cikin kwanaki 100 na farko da ya yi a ofis.

Kungiyar ta lura cewa Danfulani ya shimfida sahihin jagoranci ga hukumar, yana daidaita shirye-shiryen NAIC da shirin noma na Renewed Hope na Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, wanda ya ba da fifiko kan samar da isasshen abinci, faɗaɗa noman rani da kuma inganta noma ta hanyoyin zamani.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja, Shugaban ƙungiyar, Farfesa Hassan Muhammed, ya yaba da yadda Danfulani ya tunkari batun kawo sauyi a fannin noma, inda ya ambaci ƙoƙarinsa na farfaɗo da ƙarfin hukumar, ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi, tare da jawo jarin kamfanoni masu zaman kansu cikin harkar noman rani da na damina da ma noma a zamance.

“Yazid Danfulani ya nuna cikin kwanaki 100 kacal cewa shugabanci da aka gina bisa hangen nesa da gaskiya na iya sake sanya hukumar NAIC a matsayin ginshiƙi wajen bunƙasar ƙasa,” in ji ƙungiyar.

“Himmarsa ta faɗaɗa filayen noman rani, tallafa wa manoma da kuma shigar da hanyoyin noma na zamani suna cike da daidaito da manufofin inganta noma na Shugaban Ƙasa Tinubu.”

Haka kuma, sun yaba da jajircewarsa kan gaskiya, ƙarfafa matasa da kuma ƙara wa mata shiga harkar noma, inda s**a nuna shirin horarwa da tallafa wa manoma da aka kaddamar a ƙarƙashin jagorancinsa.

A cewar shugabannin kungiyar Arewa Forum, gyare-gyaren da Danfulani ya fara sun riga sun ba manoma kwarin gwiwa tare da gina tubalin juyin juya halin noma na dogon lokaci a fadin Nijeriya.

Sun roƙe shi da ya ci gaba da ƙara ƙaimi ta hanyar faɗaɗa ayyukan hukumar NAIC a sassa shida na kasar nan, domin tabbatar da cewa al’ummomin karkara da ƙungiyoyin manoma sun amfana sosai daga noman rani da ci gaban noma a zamanance.

“Arewacin Nijeriya, da ma ƙasar baki ɗaya, na alfahari da nasarorin da Dr Yazid Danfulani ya cimmawa cikin wannan ɗan gajeren lokaci,” in ji sanarwar.

“Ƙoƙarin da ya fara na ba mu tabbacin cewa hukumar NAIC a ƙarƙashin jagorancinsa za ta taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar karancin abinci da kuma haɓaka samar da amfanin gona.”

Sakaci na karshe: Mutanen Zauma a karamar hukumar Bukuyum sun dora alhakin kara tabarbarewar tsaro a jihar Zamfara kan G...
15/09/2025

Sakaci na karshe: Mutanen Zauma a karamar hukumar Bukuyum sun dora alhakin kara tabarbarewar tsaro a jihar Zamfara kan Gwamna Dauda Lawal Dare.

Sani Salisu kabiria Zauma

Al’ummar yankin Zauma a karamar kukumar Bukkuyum ta Jihar Zamfara sun bayyana bacin rai da takaicin da suke ji bisa gazawar da ake ta gani ta Gwamna Dauda Lawal Dare wajen magance tabarbarewar tsaro a jihar. Sabon harin da aka kai a Birnin Zarma, inda ’yan bindiga dauke da muggan mak**ai s**a kai farmaki da asuba, s**a halaka mutum ɗaya, s**a raunata matarsa, sannan s**a yi awon gaba da mata da yara su 18, ya zama abin takaici kan yadda rayuwar al’ummar jihar Zamfara ta koma cikin halin tsaka mai wuya.

Shaidun gani da Ido sun bayyana cewa maharan sun kutsa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 5:00 na asuba a lokacin da jama’a ke shirin tashi sallar asuba. Sun harbe mutumin nan har lahira, s**a jikkata matarsa, sannan s**a sa mata da yara fita daga ƙauyen cikin firgici da tashin hankali. Rahotanni sun nuna cewa maharan sun fito daga yankin Anka, inda suke da sansanoni a dazukan da ke kusa, s**a aiwatar da wannan mummunan aiki ba tare da sun samu wata tirjiya ba. Sojojin da ke Bukkuyum sun kasa ketarawa zuwa Birnin Zarma domin ba da ɗauki saboda ruwa ya kawo kogin da ya raba ƙauyukan babu kuma jirgin da zai iya ɗaukar su. Wannan ya sake bayyana irin ƙarancin shiri, dabaru da kuma jajircewar gwamnatin jihar wajen kare yankunan karkara masu rauni.

Abin da ya kara tsananta wannan ibtila’i shi ne shiru da rashin nuna halin ko in kula daga Gwamna Dauda Lawal Dare da gwamnatin sa. Tun bayan faruwar lamarin, gwamnan bai je duba waɗanda abin ya shafa ba, haka kuma bai aiko wakilin sa domin ya tausaya ko ya tsaya tare da iyalan da abin ya rutsa da su ba. Wannan sakaci ya nuna ba wai kawai rashin jagoranci ba ne, har ma da rashin tausayi ga al’ummar jihar Zamfara da ke cikin halin ƙunci. Al’ummomin Bukuyum da sauran yankunan jihar sun bar wa ƙaddara rayuwarsu, babu wani taimako daga gwamnatin jihar da aka zaɓa domin kare su.

Mutanen Zauma sun jaddada cewa rayuwa a Birnin Zarma da sauran ƙauyukan da ke kewaye na kara zama cikin wahala. Idan ba gwamnatin tarayya ta sa baki ba, rayuwa a yankunan nan za ta gagara gaba ɗaya. Gaskiya tana da daci, gwamnatin jihar Zamfara a ƙarƙashin Dauda Lawal Dare ta gaza cika kundin tsarin mulki na kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Maimakon nuna jarumta, jajircewa da dabaru na musamman wajen kawo ƙarshen rashin tsaro, gwamnan ya ma manta da rayukan mutanen karkara.

Wannan sanarwa na zama gargadi da kuma roƙo a lokaci guda. Na farko, tana zargin Gwamna Dauda Lawal Dare da barin ƙauyuka irin su Birnin Zarma da Zauma a hannun ’yan bindiga da ke kashewa, yin garkuwa, satar dukiya da lalatata. Na biyu, tana roƙon Shugaba Bola Ahmad Tinubu da gwamnatin tarayya su gaggauta kawo agaji a Jihar Zamfara. Sai dai matakan gaggawa na gwamnatin tarayya ne kawai za su iya ba wa jama’ar Bukuyum, Anka, Gummi da sauran wuraren da abin ya shafa damar samun sauƙi daga hare-haren da s**a mayar da rayuwarsu tamkar mafarki mai ban tsoro.

Mutanen jihar Zamfara sun sha wahala ƙwarai. Kisa, garkuwa da mutane da tilasta jama’a yin hijira. Gwamnatin Dauda Lawal Dare ta nuna gazawa wajen kawo ƙarshen wannan ibtila’i. Saboda haka, wajibi ne gwamnatin tarayya ta yi gaggawar ɗaukar mataki kafin a share dukkanin ƙauyukan jihar daga doron kasa.

Rikon sakainar kashin da Gwamna Dauda ya yi wa bangaren kiwon lafiya ya sa ma'aikatan jinya na 'nas' tsunduma yajin aiki...
12/09/2025

Rikon sakainar kashin da Gwamna Dauda ya yi wa bangaren kiwon lafiya ya sa ma'aikatan jinya na 'nas' tsunduma yajin aiki a jihar Zamfara, in ji wata kungiya mai rajin tabbatar da shugabanci na gari

Ƙungiyar mai rajin tabbatar da shugabanci na gari mai suna Zamfara Good Governance Forum ta bayyana matsananciyar damuwa da ɓacin rai kan yajin aikin da kungiyar ma'aikatan jinya ta 'nas' a jihar Zamfara ta tsunduma, inda ta danganta lamarin kai tsaye ga rikon sakainar kashi da Gwamna Dauda Lawal Dare yake gudanarwa a sashen kiwon lafiyar jihar.

A cikin wata sanarwa da Sakatarenta, Kabiru Ibrahim Gusau ya sanya wa hannu, Ƙungiyar ta la’anci ware malaman jinya a asibitoci daga cikin sabon tsarin albashi da aka amince da shi, wanda aka aiwatar ne kawai ga likitoci, duk da roƙo da gargaɗin da aka yi akai-akai daga ɓangaren waɗanda abin ya shafa.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa irin wannan wariyar ba wai kawai tana keta mutuncin malaman jinya da sauran ma'aikatan lafiya ba, har ila yau tana jefa miliyoyin al’ummar Zamfara cikin haɗari, musamman a daidai lokacin da jihar ke fama da mummunar annobar kwalara wato amai da gudawa.

“Shirin gwamnatin na yin watsi tare da fifita likitoci kawai, babbar shaida ce ta amfani da mulki ba da gaskiya ba, kuma zalunci ne mai girma. Malaman jinya su ne ginshiƙin tsarin kiwon lafiyarmu, kuma yi musu wannan raini ba wai kawai rashin dattaku ba ne, illa ce kai tsaye ga rayukan al’ummarmu,” in ji Kabiru Ibrahim Gusau.

Ya ƙara da cewa rashin tausayi da nuna halin ko-in-kula na gwamnan yana jefa fannin kiwon lafiya na jihar Zamfara cikin hatsari. “A bayyane a fili, idan annobar kwalara ta ƙara muni kuma rayuka s**a salwanta sak**akon wannan yajin aiki, alhakin zai rataya ne a wuyan Gwamna Dauda Lawal Dare. Gazawarsa na gaggauta ɗaukar mataki cikin adalci cin amanar jama’ar da s**a ba shi amanar shugabanci ne,” in ji Gusau.

Ƙungiyar Zamfara Good Governance Forum ta yi kira ga Gwamna Dauda Lawal da ya gaggauta tsoma baki ta hanyar umartar Ma’aikatar Lafiya da ta gyara tsarin albashin da aka aiwatar cikin son rai, tare da haɗa malaman jinya a cikin biyan watan Satumba.

“Lokacin bayar da hujjoji ya wuce. Jama’ar jihar Zamfara ba za su iya jure rugujewar tsarin kiwon lafiya a daidai lokacin da aka fi bukatarsa ba. Dole ne Gwamna Lawal ya yi gaggawa yanzu, idan ba haka ba tarihi zai tuna da shi a matsayin mutumin da ya yi watsi da kiwon lafiyar jama'arsa a lokacin da s**a fi buƙatar sa,” in ji Kabiru Ibrahim Gusau.

Kungiyar manoma ta yaba wa Shugaban hukumar NAIC, Danfulani, bisa ƙoƙarinsa na inganta wadatar abinciMasu ruwa da tsaki ...
10/09/2025

Kungiyar manoma ta yaba wa Shugaban hukumar NAIC, Danfulani, bisa ƙoƙarinsa na inganta wadatar abinci

Masu ruwa da tsaki a harkar noma daga sassa daban-daban na Nijeriya sun yaba wa Shugaban Hukumar Inshorar aikin gona ta Nijeriya NAIC, Yazid Danfulani, bisa jagorancinsa na kawo sauyi da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da wadatar abinci.

Masu ruwa da tsakin, ƙarƙashin inuwar Agricultural Stakeholders Forum, sun gode wa Danfulani saboda yadda ya sake daidaita hukumar ta NAIC ta zama cibiya mai muhimmanci a tsarin darajar noma a Nijeriya.

Sun ce gyare-gyaren da ya jagoranta suna ƙara wa manoma kwarin gwiwa, suna samar da muhimmancin inshora, tare da rage haɗarin da ke tattare da saka hannun jari a harkar noma.

Shugaban kungiyar, Dr. Inuwa Zakari Yau, ya bayyana a wata sanarwa ranar Laraba cewa Danfulani ya nuna “ƙwazo na musamman” tun daga lokacin da ya hau kujerar, inda ya kawo sabbin kirkire-kirkire a ayyukan hukumar NAIC.

Masu ruwa da tsakin sun jaddada cewa ƙoƙarinsa ya yi daidai da Ajandar Sabuwar Fata ta Renewed Hope Agenda ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman wajen magance matsalar ƙarancin abinci da kuma ƙarfafa juriya a harkar noma.

“Alhaji Danfulani ya bai wa manoma kariya da suke bukata domin faɗaɗa aikin noma. Shirin nasa na da matuƙar muhimmanci ga hangen nesa na shugaban ƙasa na ganin Nijeriya ta tsira daga yunwa,” in ji kungiyar.

Ƙungiyar ta kuma lura cewa rawar da hukumar NAIC ƙarƙashin Danfulani ke takawa zai kare manoma daga haɗarin da sauyin yanayi da kasuwanci ke haifarwa, tare da ƙarfafa matasa da masu saka hannun jari na musamman wajen shiga harkar noma.

Sun yi alƙawarin ci gaba da tallafa wa hukumar NAIC tare da kira ga masu ba da rance, da ƙungiyoyin manoma da su yi aiki kafada da kafada da jagorancin Danfulani domin tabbatar da noma shi ne ginshiƙin wadatar abinci a Nijeriya.

Masu ruwa da tsakin sun kammala da cewa, tare da sabon salo da hukumar NAIC ta ɗauka, ƙasar na kan hanya madaidaiciya wajen shawo kan ƙarancin abinci da kuma cimma bunƙasar harkar noma.

Kungiyar matasan Arewa maso Yamma ta yi jinjina da yabo ga Minista Matawalle kan jagorancin sauye-sauye da kudurin karew...
10/09/2025

Kungiyar matasan Arewa maso Yamma ta yi jinjina da yabo ga Minista Matawalle kan jagorancin sauye-sauye da kudurin karewa da inganta tsaron Nijeriya

Kungiyar matasa ta Arewa maso Yammacin Nijeriya ta jinjina wa Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Dr Bello Muhammad Matawalle, MON, bisa kokarinsa wajen gyare-gyare masu ma'ana da kuma jagoranci na kishin kasa da ke sauya tsarin tsaro a Nijeriya tare da karfafa kariyar kasa.

A cikin sanarwa da Sakataren Kungiyar, Muhammad Ibrahim Malumfashi daga Jihar Katsina, ya fitar, matasan sun bayyana Matawalle a matsayin “shugaban da ke da hangen nesa, wanda shirye-shiryensa ke dawo da kwarin gwiwa ga dakarun Nijeriya, kare kasa da kuma karfafa fata ga miliyoyin matasa a Arewa maso Yamma da kasar baki daya.”

Kungiyar ta jaddada muhimmancin gudunmuwar Ministan wajen tabbatar da yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin Defence Industries Corporation of Nigeria (DICON) da kamfanin samar da kayan tsaro daga kasar Sin. Wannan hadin gwiwa zai baiwa Nijeriya damar cin gajiyar canjin fasaha, samar da mak**ai a cikin gida a Kaduna da Kachia, da kuma horar da jami’an Nijeriya a fannin sabbin fasahohin samar da tsaro.

A cewar kungiyar, wannan mataki ba wai kawai zai kara karfin sojojin Nijeriya ba ne, har ma zai samar da guraben ayyukan yi da gina masana’antu masu dorewa a kasar.

Malumfashi ya ce “Dr Matawalle ya tabbatar da kansa a matsayin mai gyara. Ba wai magana kawai yake yi kan tsaro ba, yana gina masana’antu, hada-hadar kasa da kasa da tsare-tsaren da za su tabbatar da dorewar zaman lafiya da dogaro da kai a Nijeriya. A matsayinmu na matasa, muna ganin shi a matsayin wata fitila da ke haskawa a kasa.”

Kungiyar ta kara jinjina wa Matawalle bisa tsarin da ya kawo na mayar da kamfanin DICON zuwa tsarin hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, wanda ya kara yawan samar da mak**ai kanana, kayan kariya da kuma sassan jiragen yaki marasa matuki a cikin gida. Sun bayyana wannan gyara a matsayin mataki na jarumta daga dogaro da masu sayar da mak**ai daga kasashen waje zuwa gina masana’antar soji a cikin gida.

Dangane da tsaro a fagen gaba, kungiyar ta jaddada nasarorin Ministan da s**a hada da: kawar da sama da ’yan ta’adda 8,000, cafke sama da masu tayar da kayar baya 11,600, kwato mak**ai 10,000, da kuma karin kaso 46 cikin dari na wadanda aka kubutar daga garkuwa.

Malumfashi ya ce “Wadannan alkalumma ba wai kididdiga ce kawai ba; suna wakiltar rayukan da aka ceto, al’ummomin da aka dawo da su da kuma makomar da aka tsare. A karkashin jagorancin Matawalle, ’yan Nijeriya sun fara ganin ingantaccen ci gaba a yaki da rashin tsaro.”

Kungiyar ta kuma yaba da rawar da Matawalle ya taka wajen tsaron teku, musamman wajen kafa Gulf of Guinea Maritime Task Force da kaddamar da jiragen sintiri masu dogon zango tare da hadin gwiwar kasar Turkiyya. Sun ce wannan zai karfafa zaman lafiya a yankin tare da kare hanyoyin ruwa masu muhimmanci ga Nijeriya.

Sanarwar ta kuma yaba da kirkirar da ya yi na tura fiye da motocin sojoji 80 masu amfani da iskar CNG, suna bayyana shi a matsayin “mataki na hangen nesa wanda ya nuna hikimar tattalin arziki da kulawa da muhalli.”

A karshe, kungiyar ta tabbatar da goyon bayanta da cewa “Kungiyar Matasa ta Arewa maso Yamma na tsayawa kyam da Dr Bello Matawalle. Kudurinsa na tabbatar da zaman lafiya, tsaro da ci gaban masana’antu a Nijeriya ba shi da tamka. Muna kira ga ’yan Nijeriya, musamman matasa, da su mara masa baya yayin da yake ci gaba da kare makomar mu da tabbatar da tsaron kasa.”

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum Ta yi Allah-wadai da yadda Gwamnan Dauda ke lalata dukiyar jama'a da siyasantar d...
08/09/2025

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum Ta yi Allah-wadai da yadda Gwamnan Dauda ke lalata dukiyar jama'a da siyasantar da matsalar tsaron jihar Zamfara

Kungiyar nan mai rajin tabbatar da shugabanci na gari wato Zamfara Good Governance Forum ta yi tir da kakkausar murya kan wasu kalaman da Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi kwanan nan, inda ya bayyana cewa yana sane da inda ’yan bindiga suke, hanyoyin da suke bi da kuma maboyarsu.

Kungiyar ta bayyana wannan magana tasa a matsayin ta rashin tunani da raahin tausayi kuma abin kunya, inda ta ce idan har da gaske gwamnan yana da irin wannan muhimman bayanai, amma ya ki daukar mataki, hakan na nuni da gazawar shugabanci. Kungiyar ta jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne babban alhakin gwamna, don haka babu wani uzuri da zai dace a yi yayin da rayukan jama’a ke ci gaba da salwanta kullum.

Da yake jawabi a madadin kungiyar, sakataren ta, Kabiru Ibrahim Gusau, ya ce
“Idan Gwamna Dauda Lawal Dare na da sahihan bayanai kan inda ’yan ta’addar nan suke k**ar yadda ya yi ikirari, to me ya sa bai dauki mataki ba? Me ya sa bai mika bayanan ga jami’an tsaro domin su hallaka su ba? Sai kawai ya rika fakewa da cewa ba shi da ikon umartar sojoji ko ’yan sanda, alhali gwamnatinsa na kashe sama da Naira biliyan 3 a duk wata a kan tsaro. Ina kuɗin suke zuwa? Ana kashe mutanenmu, ana sace su, ana raba su da muhallansu, shi kuma yana siyasa da rayukan mutune.”

Kungiyar ta zargi gwamnan da rashin gaskiya, tana mai cewa da zarar jami’an tsaro sun yi nasara sai ya yi ta ikirarin cewa shi ne ya yi nasara, amma idan matsalar tsaro ta ta’azzara, shi ne farkon mai fara babatu a kafafen yada labarai yana maganganu na siyasa. Kungiyar ta ce hakan ya nuna cewa gwamnan ya fi sha’awar tallata kansa fiye da ceton rayuka.

Kungiyar ta tunatar da jama’a cewa kafin zaben 2023, Dauda Lawal ya yi kyamfe yana zargin tsohon gwamna Bello Matawalle da gazawa kan tsaro, tare da yin alkawarin kawo karshen ’yan bindiga cikin makonni biyu idan aka zabe shi. Sai dai fiye da shekaru biyu bayan hawan mulkinsa, matsalar tsaro ta kara tsananta, ana lalata kauyuka, hare-haren ’yan bindiga sun karu, kuma iyalai na ci gaba da rayuwa cikin tsoro.

Baya ga matsalar tsaro, kungiyar ta yi kakkausar s**a ga barnar kudade a gwamnatin Dauda. Kungiyar ta zarge shi da bayar da kwangiloli da sake bayar da su cikin tsada ta barna wadda ba ta kawo wani amfani ga jama’a, abin da ya haifar da asarar biliyoyin kudi da za a iya amfani da su wajen inganta ilimi, kiwon lafiya ko samar da ayyukan yi. Kungiyar ta kuma kawo misali da aikin filin jirgi, wanda a karkashin Matawalle aka tsara gudanar da shi kan kuɗin Naira bilyan 11.8 tare da kammala kashi 60%, amma Dauda ya sake bayar da kwangilar kan kuɗin Naira bilyan 62.9. Daga baya kuma ya kara wata Naira bilyan 30 a matsayin wasu sauye-sauye da jimillar kudin ta kai ta kai zuwa Naira bilyan 90.9, abin da s**a bayyana a matsayin dabara ta wawure kudaden jama’a da sunan ci gaba.

Kabiru Ibrahim Gusau ya ƙara jaddada cewa, “Wannan ba batun siyasa kawai ba ne, batun tseratar da rayukan mutane ne. Mutanen jihar Zamfara na cikin mawuyacin hali Maimakon Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi shugabanci cikin tausayi, sai ya zaɓi yin siyasa da rayuwar mutanen da ba su ji ba su gani ba. Ya yi kyamfe da alƙawuran da bai cika ɗaya ba, yau kuma yana mulki da uzuri da yaɗa farfaganda, alhali jama’a na biyan kuɗin hakan da jinin su.”

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ta yi kira ga jama’a da su ƙi amincewa da yaudara su kuma nemi a riƙa dora wa gwamnan alhakin aiki na aikace-aikacen da ya gaza. Kungiyar ta bukaci hukumomin yaƙi da cin hanci, ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tarayya da su binciki yadda ake yi wa kuɗaɗen jihar Zamfara rikon sakainar kashi.

“Mutanenmu sun cancanci zaman lafiya ba farfaganda ba. Sun cancanci kariya ba uzuri ba. Sun cancanci shugabanci ba wasa da siyasa ba. Dole ne a riƙa ɗora wa Gwamna Dauda alhakin siyasantar da rayukan da ya rantse zai kare,” in ji Gusau a ƙarshe.

An k**a Boka da ya ke sayen kwaroron roba da aka yi amfani da su daga ƴan mata masu zaman kansuAn k**a wani boka a jihar...
07/09/2025

An k**a Boka da ya ke sayen kwaroron roba da aka yi amfani da su daga ƴan mata masu zaman kansu

An k**a wani boka a jihar Anambra bayan da ya amsa cewa yana karɓar kwaroron roba da aka yi amfani da su daga wajen ‘yan mata masu zaman kansu domin shirya tsafi.

Wanda ake zargin, mai suna Anagbo Emeka daga garin Umugbo a karamar hukumar Ayamelum, matasan ne s**a k**a shi a unguwar Echara, Awka North.

Wani bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook na Dr. Uche Nworah ya nuna lokacin da Emeka ya amsa laifinsa a fili.

Ya ce: “Na yi yarjejeniya da ita ta sayar min da kwaroron roba da aka yi amfani da su. Ta kawo min, amma daga baya ta kai rahotona. Wannan shi ne kuskuren da na yi,” in ji shi a cikin bidiyon.

A cewarsa, ya kulla yarjejeniya da wata karuwa da ta rika kawo masa kwaroron roba daga gidajen karuwai. Amma daga baya ta fasa alkawarin, ta tona asirin sirrin da s**a ɓoye.

Emeka ya kuma bayyana cewa waɗannan kwaroron roba na da matuƙar amfani wajen harkokin tsafi da yake yi.

Ya ce: “Ina amfani da kwaroron roba wajen yin tsafi don sihiri, husuma, rikicin filaye, har ma da shari’ar ‘yansanda.”

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamfara Online:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share