Taskar Al'ummah Online TV

Taskar Al'ummah Online TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Taskar Al'ummah Online TV, Kano.

Wannan Kafa ce da zata ke kawo muku kallar wainar da ake toyawa a fadin duniya, ku dai ku kasance da Taskar Al'ummah dan sanin abinda duniya ke ciki a duk inda kuke.

Hukumar Binciken Sararin Samaniya ta Kasa (NASRDA) ta tabbatar cewa za a ga sabon jinjirin wata na farko a shekarar 2025...
23/02/2025

Hukumar Binciken Sararin Samaniya ta Kasa (NASRDA) ta tabbatar cewa za a ga sabon jinjirin wata na farko a shekarar 2025 a Najeriya ranar 28 ga Fabrairu. A cewar sanarwar da Daraktan Sadarwa da Hulɗa da Jama'a na NASRDA ya fitar a ranar Asabar, an bayyana cewa jinjirin zai bayyana ne da ƙarfe 1:45 na safe agogon Najeriya (WAT).

Wannan lokacin, da ake kira "Crescent Zero Hour," shi ne mafi ƙarancin lokacin da za a iya ganin jinjirin ƙarƙashin yanayi mafi kyau ta amfani da kayan hangen nesa kamar gilashin bincike ko na'urar hangen nesa. Duk da haka, ga waɗanda ba su da kayan binciken wata , za su iya ganin jinjirin da ido kawai da yamma ranar Juma'a, 28 ga Fabrairu, tsakanin ƙarfe 6:17 na yamma zuwa 7:35 na yamma a sassa daban-daban na ƙasar.

A Kachia, Jihar Kaduna, ana sa ran ganin jinjirin tsakanin ƙarfe 6:38 na yamma zuwa 7:12 na yamma. NASRDA ta ba da shawarar amfani da gilashin bincike ko na'urar hangen nesa idan ya zama dole, tare da tabbatar da cewa an zaɓi wurare masu faɗi ba tare da cikas ba a gabar yamma bayan faɗuwar rana. Hakanan, yanayi mai kyau na sararin samaniya yana da muhimmanci don ganin jinjirin yadda ya kamata.

MUGU BAI DA K**ASunansa Abdulrahman Muhammad Ballo, yana yin Facebook, ya hadu da wannan yarinya a Facebook mai suna Haf...
16/02/2025

MUGU BAI DA K**A

Sunansa Abdulrahman Muhammad Ballo, yana yin Facebook, ya hadu da wannan yarinya a Facebook mai suna Hafsa Lawal inda s**a kulla soyayya s**ayi musayen nambar waya

Kwanaki shida da s**a wuce wato ranar 10-2-2025 Abdulrahman ya kira Hafsah akan su hadu, tunda daga wannan ranar aka nemeta aka rasa

'Yan sanda sun karbi nambar wayan Hafsah s**a duba last call da last location dinta wanda hakan ya taimaka aka gano da Abdulrahman tayi waya na karshe, sai akayi tracking dinsa aka kamashi

Da farko ya musa cewa shi ya ka$heta, yace wai cutar asthma ne yayi aja|inta, da akaje searching gidansu sai aka tarar da g@warta a wani daki ya daddat$a ta ya cire wasu sa$$a na jik!nta, akwai bidiyo a Telegram ta nan
👇
https://t.me/DattiassalafiyTech

Irin wadannan abubuwa da suke faruwa ya kamata ya zama babban darasi ga 'yan matan social media, ku shiga taitayinku, ku dinga sanin wadanda zaku hadu da su

Kuma ma imba lalacewa ba babu dalilin da zai sa mace budurwa tabi saurayi hotel ko gidansa, idan aure ne da gaske yake to ya je gidanki ba wai ke ki bishi ba

Allah Ya kare mu daga sharrin cin amanar wadanda muka basu aminci

05/02/2025

Yar gwagwarmaya kuma mace Mai kamar Maza tace bazata Kanye kalamanta ba Kan Nuhu Ribado.

An dakatar da Bin Uthman daga limancin masallacin Sahaba Masallacin Jami’ur Rahman, wanda a da ake kira da Masjid Sahaba...
31/01/2025

An dakatar da Bin Uthman daga limancin masallacin Sahaba

Masallacin Jami’ur Rahman, wanda a da ake kira da Masjid Sahaba, ya dakatar da Sheikh Muhammad Bin Uthman daga limanci biyo bayan hudubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu.

Asalin masallacin, wanda Bin Uthman ke jagoranta tsawon shekaru 24, na kusa da sabon wanda AY Maikifi ya sayi filin.

Bayan Maikifi ya samu mallakar filin a hannun gwamnati don gina sabon masallacin Sahaba, sai ya tuntubi Bin Uthman inda s**a amince da cewa tshohon masallacin Sahaba zai dawo sabon gini.

Sai dai kuma a yayin huɗubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu, wacce ta haifar cece-ku-ce, Bin Uthman ya ba da labarin yadda aka rage masa matsayi wajen gudanar da harkokin masallacin.

A cewar sa, an nada shugabanni uku masallacin amma ba a nada shi a jagora ba.

Daily Nigerian ta gano cewa huɗubar ta ranar 24 ga watan Janairu ta fusata masallata, inda s**a kusa dukan sakataren kwamitin amintattu na masallacin, Abdulkadir Isawa.

Hukumar kula da masallacin, a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun daraktan gudanarwa, ta dakatar da Bin Uthman har sai baba-ta-gani, tare da umartar shi da ya mika dukkan kayan masallacin da ke hannunsa.

A ranar Litinin ne kuma hukumar tsaro ta farin kaya, SSS, da majalisar malamai s**a gayyaci Malam Bin Usman da wanda ya assasa sabon masallacin, Maikifi.

Hukumar SSS, a cewar majiyoyi, ta gargadi Bin Uthman kan huɗubar da su ka ce ka iya haifar da rikici ko hari a cikin masallacin.

CopyNAJI KUNYA MATUKA LOKACIN DA NAKE JIN BAYANAN SAKATAREN KWAMIYIN SABON MASALLACIN JUMA'A NA KUNDILA. Assalamu alaiku...
30/01/2025

Copy

NAJI KUNYA MATUKA LOKACIN DA NAKE JIN BAYANAN SAKATAREN KWAMIYIN SABON MASALLACIN JUMA'A NA KUNDILA.

Assalamu alaikum.

Wato wallahi naji kunya matuka yadda naji bayanan sakataren Kwamitin masallacin Juma'a na Jami'ur Rahma dake Kundila.

WALLAHI AN YAUDARI KUMA ZALUNCI MALAM SOSAI. GA ZALUNCIN DA AKAYIWA MALAM BAYAN SAURARON KOWANNE BANGARE.

1. Hana Malam Jawabi koda na godiyane ranar da aka bude wannan Masallacin.

2. Amince da cewa za'a sabunta Masallacin Sahaba wanda baro baro gashinan a SIGN BOARD an rubuta "PROPOSED SAHABA JUMA'AT MOSQUE"

3. Canza sunan Masallaci bayan Malam ya rushe nasa.

4. Kwace wasu daga cikin Karatuttukan Malam.

ABUBUWAN DA S**A BANI KUNYA KUWA SUNE.

1. A Jawabin Sakataren Kwamitin masallacin yace lokacin da za'a bude sun tambayi Alh. Adamu Mai Kifi ko yana da wani tsari. Mutumin da yayi fisabilillah meye na tambayarsa?

2. Tambayar da Malaman Kwamitin masallacin ne yasa har yace yanaso ayi Limamai guda Uku masu Mataki daya. Ina ruwanka idan Dan Allah kayi?

3. Idan anaso ayi Limamai Uku shin Masallacin Sahaba Malamai nawane dashi?

4. Abun Mamaki wai Malam yace zaiyi Karatu guda Uku amman Alh. Adamu Mai Kifi yace bai amince ba. Wannan maganar tafi bani Mamaki da kunya saboda sam yama rainawa mutane hankali.

5. Saka Alh. Adamu Mai Kifi a cikin wanda zai riqa shiga harkar Malunta yafi komai zama Matsala domin makwadaita bazasu iya fadamasa gaskiya ba.

SHAWARA GA MALAM BIN UTHMAN, MALAMAI DA GWAMNA

MALAM

1. Kayi hakuri ka cigaba da addua iya maganar da kayi ta wadatar domin mugun rami akayi maka.

2. Kada ka yarda dalibai su tunzura ka domin gudun fadawa tarkon masharranta.

3. Idan zama a sabon Masallacin bazai yiwu ba cikin hikima da Kwanciyar hankali ka koma Masallacinka domin anaso kayi tashin hankali saboda tsohon masallacin ma a hanaka sallah.

MALAMAI

1. Kusani kune ababen koyi garemu

2. Kuyi Kokarin yiwa Shaykh Muhammad Bin Uthman adalchi da al'ummar dake ibadah a wannan masallacin.

3. Malamai su wakilta Sheikh Abdulwahab Abdallah domin gudanar da Allah gobe domin gudun fitina kafun komai ya lafa

ALH ADAMU MAI KIFI

1. Kaji tsoron Allah domin Allah yakarbi wannan aiki naka

2. Ka miqe domin yaqar shaidanun masu baka shawara.

GWAMNATI

1. Gwamnati tayi Kokarin ganin anyiwa Jama'a adalchi.

2. Gwamnati ta bawa Malam umarnin bude sabon Masallacinsa domin samun zaman lafiya.

ALLAH KA BAMU LAFIYA DA ZAMAN LAFIYA. ALLAH KA KARE IMANINMU DA MUTUNCINMU.

30th January, 2025.
Copyright

Cikakken labarin abunda ya faru tsakanin Seaman Abbas da matarshi Hussaina. Seaman Abbas ya yiwa matarsa Hussaina dukan ...
30/01/2025

Cikakken labarin abunda ya faru tsakanin Seaman Abbas da matarshi Hussaina.

Seaman Abbas ya yiwa matarsa Hussaina dukan tsiya har sai da aka yi mata karin jini bisa zargin ita ce sanadiyyar korarsa a aiki sannan kuma da batun cewa an tara mata kudi Naira milyan 20 ta ɓoye bata bashi ba, abun ya kai ga har ta koma gida....

Sea Man Abbas ya dake Hussaina kafin ya sake ta, Damuwar Hussaina shine Seaman Abbas ya futo ya shaki iskar yanci Koda bayi da kudi tana sonshi a haka.

Damuwar Seaman Abbas shine an baiwa Hussaina kudade Masu yawa Kuma Taki ta bashi, a fahimtar sa itace tayi sanadiyar rasa Aikin sa.

Hussaina Tasan Halin Mai Berkete Family baya wargi, shiyasa take taka tsantsan, shi Kuma Seaman Abbas a fahimtar sa Brekete Family yaki Tara Masa kudin da yayi alkawari, Kuma mutane sun ce zasu Tara ya hau su da fada, shiyasa ya fake da cewa Hussaina ce taci kudin da aka Tara Masu.

Har yanzu dai Hussaina tana son Seaman duk da akwai abubuwan da ba za a ma fada maku ba

Tun farko wayensu sun dauka munki mu Goya wa Seaman baya ne Amma duk Wanda yasan gidan Soja, akwai discipline din da idan har kaga mutum bayi dashi, to asali a rayuwar Sa akwai matsala.

Hankali seaman daidai ne yanzu, kada wani yace maku Yana da ta'bun hankali.

26/01/2025

Allah yasa Gfresh yaji wannan nasihar ta Matan kannywood 여자친구 G-Friend Gfresh Alameen

19/01/2025

Allahu Akbar!! Abul Fatahi Ya kalubalanci Marigayi Shek Jaafar Mahadud Adam, kuma ya samu amsar kalubalen daga bakin Marigayi Shek Jaafar Mahadud Adam.

20/11/2024

To fa!! Murja Kunya ta fara ganin ishara da idanunta.

Wai Jami'an Tsaro Šùn Ýi Nàsaŕar Ķàşhè Bèĺlo Țùrjì?Ana ŕàďe-radin cewa jami'an tsaron Nijeriya sun yi nasarar ķàshe Ďañ ...
20/11/2024

Wai Jami'an Tsaro Šùn Ýi Nàsaŕar Ķàşhè Bèĺlo Țùrjì?

Ana ŕàďe-radin cewa jami'an tsaron Nijeriya sun yi nasarar ķàshe Ďañ ta'aďďa Beĺĺo Tùŕjì a jihar Šokoto a daren jiya.

Mazauna yankin Sabon Birni suna zargjn Beĺlo ya mùťù ne tun bayan wani kofar rago da jami'an tsaro s**a yi masa a ranar Àsabar din da ta gabata.

Tuni dai wasu mazauna yankunan da lamarin ya auku s**a soma yada labarin a shafukan su na twitter.

Muna rokon Allah Ýa tabbatar da waññan labarì.

Daga Ishaka Usman Wali

Alhamdulillah!! Alhamdulillah!! Allahu Akbar!!!Wannan bawan Allah yau juma'ah 30-08-2024 ya karbi addinin musulunci tare...
30/08/2024

Alhamdulillah!! Alhamdulillah!! Allahu Akbar!!!
Wannan bawan Allah yau juma'ah 30-08-2024 ya karbi addinin musulunci tare da iyalansa wato matarsa da dansa karami. Kuma cikin ikon Allah sun biyo ta hannu nane, ni kuma na sada su da masallacin juma'ah na Tudun Yola dake karamar hukumar Gwale s**a karbi kalmar shahada agurin lima. Yanzu dai sunansa Ibrahim, sunan matarsa kuma sunanta Fatima, dansu kuma Muhammad. Ina rokon Allah ya dawwamar dasu acikin wannan addini nasa Amin 🙏

Yanzu dai baki ne su a jihar Kano, sun baro jiharsu ta asali dan suzo garin Kano su karba musulunci da Kuma ci gaba da zama acikin yan uwansu musulmai. Dan haka duk mai burin karfafasu ta hanyar taimakonsu to kofa abude take gurin hadashi dasu kai tsaye. Allah ya bada ikon karfafawa da ko nau'in taimako mutum yayi niya Amin 🙏Allahu Akbar!!!
Wannan bawan Allah yau juma'ah 30-08-2024 ya karbi addinin musulunci dashi da iyalinsa wato matarsa da dan karamin dansa. Kuma cikin ikon Allah sun biyo ta hannu nane, ni kuma na sada su da masallacin juma'ah na Tudun Yola dake karamar hukumar Gwale s**a karbi kalma. Yanzu dai sunansa Ibrahim, sunan matarsa kuma sunanta Fatima, dansu kuma Muhammad. Ina rokon Allah ya dawwamar dasu acikin wannan addini nasa Amin 🙏🙏

Domin karin bayani akansu dama inda suke a halin yanzu ga contact number dina.
Kabeer Isah Manga:- 08064894586.

10/02/2024

Zamin Suites come one come all.

Address

Kano

Telephone

+2349024725022

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskar Al'ummah Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Taskar Al'ummah Online TV:

Share