Yau da Gobe online

  • Home
  • Yau da Gobe online

Yau da Gobe online Labaran Hausa da dumi duminsu. We created, this platform just to share, some articles, news, and others.

The Platform For Sharing What Is Happening Weather Government Or NG'Os.

Labari Da Dumi Duminsa Lauya mai fafutikar kare hakkin dan Adam, Femi Falana zai daukaka kara kan hukuncin kisa da Kotun...
03/09/2020

Labari Da Dumi Duminsa

Lauya mai fafutikar kare hakkin dan Adam, Femi Falana zai daukaka kara kan hukuncin kisa da Kotun Musulunci ta yanke wa matashin da ya yi batanci ga Manzon Allah (SAW).

Muna Rokon Allah Ya Yi Wa Kasarmu Nijeriya Jagoranci Wajen Gyaruwarta, Duk Abun Da Ya Fi Karfin Mu, Allah Ya Wuce Mana G...
03/09/2020

Muna Rokon Allah Ya Yi Wa Kasarmu Nijeriya Jagoranci Wajen Gyaruwarta, Duk Abun Da Ya Fi Karfin Mu, Allah Ya Wuce Mana Gaba, Yaa Hayyu Yaa Qayyum

Addu'ar Ministan Sadarwa Sheikh Pantami Ga Kasarmu Nijeriya

Daga Comr Abba Sani Pantami

NAZARI: Yankin Arewa Maso Gabas Ne Kadai Yankin Da Ba Su Taba Mulkar Nijeriya BaDaga Comr Abba Sani PantamiJadawalin Yan...
02/09/2020

NAZARI: Yankin Arewa Maso Gabas Ne Kadai Yankin Da Ba Su Taba Mulkar Nijeriya Ba

Daga Comr Abba Sani Pantami

Jadawalin Yankunan Da S**a Mulki Kasar Nijeriya;-

Yankin Arewa ta Tsakiya, sun dau tsawon shekaru 18 suna mulkar kasar Nigeria.

1. Yakubu Gowon, ya shekara 9 yana mulkar kasar Nigeria.
2. Ibrahim Babangida, ya shekara 8 yana mulkar kasar Nigeria.
3. Abdussalami Abubakar, ya dauki tsawon shekara 1 yana mulkar kasar Nigeria.

Yankin Arewa Maso Yamma sun dau tsawon shekaru 22.6 suna mulkar kasar Nigeria.

1. Shehu Shagari, ya dau tsawon shekara 4 yana mulkar kasar Nigeria.
2. Murtala Muhammad, ya dau tsawon watanni 6 yana mulkar kasar Nigeria.
3. Muhammadu Buhari, zuwa yanzu yadau tsawon shekaru 6 yana mulkar kasar Nigeria......
4. Sani Abacha, yadau tsawon shekara 4, da wata 7 yana mulkar kasar Nigeria.
5. Umaru Musa Yardu'a, yadau tsawon shekara 2 yana mulkar kasar.

Yankin Kudu Maso Yamma, sun dauki tsawon shekaru 14 suna mulkar kasar.

1. Olusegun Obasanjo - shekara, yadau tsawon shekaru 11 yana mulkar kasar Nigeria.
2. Earnest shonekan yadau tsawon wata 3 yana mulkar kasar Nigeria.

Yankin Kudu maso Kudu sun dau tsawon shekaru 6 suna mulkar kasar Nigeria.

1. Godluck Jonathan, yadau tsawon shekaru 6 yana mulkar kasar Nigeria.

Yankin Kudu Maso Gabas sun dau kimanin shekaru 3.3 suna mulkar kasar Nigeria.

1. Nnamdi Azikiwe, yadau tsawon shekaru 3 yana mulkar kasar Nigeria.
2. Aguiyi Ironsi, yadau tsawon wata 4 yana mulkar kasar Nigeria.

Yankin Arewa Maso Gabas, itace yankin da har yanzu basu taba mulkar kasar Nigeria ba.

Shin wai Yankin Arewa Maso Gabas su ba 'yan Nigeria bane💁🏻‍♂️💁🏻‍♂️💁🏻‍♂️

DA DUMINTAFarashin Litan Man Fetur Ya Koma Naira 151.1 A NijeriyaDaga Comr Abba Sani PantamiFarashin man fetur ya karu z...
02/09/2020

DA DUMINTA

Farashin Litan Man Fetur Ya Koma Naira 151.1 A Nijeriya

Daga Comr Abba Sani Pantami

Farashin man fetur ya karu zuwa N151.1 ga lita, a cewar kamfanin kasuwancin man fetur PPMC, wani sashen kamfanin man feturin Nijeriya NNPC.

A takardar da jaridar Vanguard ta bayyana cewa ta samu gani, D.O Abalaka na kamfanin PPMC yace: "Ku sani cewa mun daura sabon farashin mai a shafin rubuta kudi.

A yanzu, farashin man fetur zai koma naira dari da hamsin da daya, da kwabo hamsin da shida ga lita.

Za'a fara aiki da sabon farashin daga 2 ga Satumba, 2020.

BATANCI GA ANNABI(S.A.W): Kotun Jihar Kano Ta Hana Yahaya Sharif Daukaka Kara Kan Hukuncin Kisan Da Aka Yanke MasaDaga C...
02/09/2020

BATANCI GA ANNABI(S.A.W): Kotun Jihar Kano Ta Hana Yahaya Sharif Daukaka Kara Kan Hukuncin Kisan Da Aka Yanke Masa

Daga Comr Abba Sani Pantami

Kokarin daukaka kara akan hukuncin kisan da aka yankewa mawaki, Yahaya Sharif Aminu ya kara samun cikas a ranar Talata, bayan shugabannin kotun Shari'a ta jihar Kano sun ki bayar da takardun shari'ar na gaskiya.

Sharif Aminu wanda aka yankewa hukuncin kisa a ranar 10 ga watan Agusta, 2020, bisa laifin batanci ga Annabi Muhammadu (SAW), an bashi kwanaki 30 ya daukaka kara akan wanan hukunci da aka yanke masa, hakan na nufin ranar Laraba 9 ga watan Satumbar nan ranekun zasu kare.

Kafin a amince a karbi korafin shi, ana bukatar mai lafin ya sanya hannu akan takardar daukaka karar, inda kuma za a sanya ainahin takarun hukuncin da aka yanke masa a ciki.

Sai dai jaridar PUNCH ta gano cewa an hana Sharif-Aminu ganin lauyansa, yayin da kuma kotun Shari'ar ta ki bayar da takardun hukuncin da aka yanke masa.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga wakilin PUNCH a ranar Talata, Lauyan dake rajin kare hakkin dan adamm Mr Femi Falana (SAN), ya ce yana kokari wajen ganin an gabatar da shari'ar.

Ya ce akwai bukatar a gabatar da komai cikin gaggawa, tunda gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, a makon da ya gabata yace zai sanya hannu akan hukuncin kisan da aka yankewa mawakin da zarar lokacin da aka diba masa na daukaka kara ya cika.

Sun ki sakin takardun hukuncin da aka yanke masa, kuma lokaci na wucewa. Idan har bamu samu takardun ba baza mu iya daukaka kara ba. Kullum cewa suke takardun basu kammalu ba, kuma lokaci kara kurewa yake," cewar Falana.

Mace Mai Aikin FentiDaga Comr Abba Sani PantamiYadda wata matashiya ke gudanar da sana'ar fenti, domin ta rufawa kanta a...
02/09/2020

Mace Mai Aikin Fenti

Daga Comr Abba Sani Pantami

Yadda wata matashiya ke gudanar da sana'ar fenti, domin ta rufawa kanta asiri ba tare da ta roki samarin zamani kudin kashewa ba.

Hakan ya yi matukar jan hankalin al'umma mafi yawan al'ummar suna ta jinjina mata tare da sanya mata Albarka tare da yi mata fatan Alkhairi.

Na Yi Adabo Da Masana'antar Finafinan Hausa, Cewar Maryam A.B YolaDaga Comr Abba Sani PantamiFitacciyar jarumar finafina...
02/09/2020

Na Yi Adabo Da Masana'antar Finafinan Hausa, Cewar Maryam A.B Yola

Daga Comr Abba Sani Pantami

Fitacciyar jarumar finafinan Hausa, Maryam AB Yola, ta fitar da sanarwa a shafinta na Instagram inda ta ce daga ranar 1 ga watan Satumban 2020, ta fice daga masana'antar Kannywood.

Daga karshe ta mika godiyarta ga masoyanta, kawaye da abokan arziki a kan irin kaunar da ake gwada mata.

Kamar yadda ta wallafa a shafin nata, "Assalamu alaikum. Ni Maryam AB Yola ina mai sanar da ku cewa daga yau daya ga watan Satumban 2020, na daina yin fim kuma na bar Kannywood.

Kuma ina matukar godiya da kaunar da kuke nuna min. Allah yasa mu dace, Ameen.

Jarumar wacce tsohuwar mata ce ga fitaccen jarumi Adam A. Zango, mazauniyar garin Abuja, ba ta sanar da dalilin ta na yanke wannan hukuncin ba.

'Yan Bindiga Da Masu Garkuwa Da Mutane, Sun Addabi Al'ummar Karamar Hukumar Doguwa Dake Kusa Da Dajin Falgore....Kungiya...
01/09/2020

'Yan Bindiga Da Masu Garkuwa Da Mutane, Sun Addabi Al'ummar Karamar Hukumar Doguwa Dake Kusa Da Dajin Falgore
....Kungiyar "Arewa Media Writers" tana kira ga Gwamnatin Nigeria da ta kai musu daukin gaggawa.

Daga Kungiyar Arewa Media Writers

Masu bin titin dajin Falgore dake karamar hukumar Doguwa dake jihar Kano suna cikin fargaba da tashin hankali da fuskantar barazana ta rashin tsaro.

Kungiyar Arewa Media Writers ta samu rahoton yadda abubuwa ke kazanta a yankin, ko a kwanakin baya saida aka sace Kansiloli 4.

Anfi samun wannan matsalar a titin daya fito daga Jos zuwa Kano duk da dumbin jami'an tsaron da suke jibge a cikin dajin aqallah akwai gate/Checkpoint fiye da goma, amma hakan bai hana aiwatar da miyagun ayyuka na ta'addanci ba a hanyar.

Ko jiya mun sami rahoton yin garkuwa da wasu bayin Allah da har yanzu bamu tabbatar da adadinsu ba, sakamakon a mota suke makare amma hakan 'yan ta'addan s**ai garkuwa dasu.

A makon daya gabata anyi garkuwa da wasu tare da yin fashi da makami a tsakanin tazarar kwana biyu tsakanin su.

Al'ummar yankin suna cikin firgici matuka baya ga fashi da makami, garkuwa da mutane, tare da satar shanu da sauran ayyukan ta'adanci da 'yan bindiga ke yi ayankin yanzu takai jama'ar yankin basu da ikon yin walwala.

Kungiyar "Arewa Media Writers" take kira ga gwamnatin Tarayya da kuma gwamnatin jihar Kano, karkashin jagorancin mai girma Gwamnan Jihar Dakta Abdullahi Umar Ganduje dasu waiwayi halin karancin tsaron da al'ummar kusa da dajin Falgore ke ciki tare da yankunan karamar hukumar Doguwa.

Da fatan jami'an tsaro za su tashi tsaye su yaki wa 'yannan bata garin, a karshe muna addu'a Allah ya tabbatar da zaman lafiya a yankinmu na Arewa, dama kasar Nigeria baki daya. Amin Amin

Kada Ka Sake Baiwa Buhari Damar Karbo Bashi Daga Kasashen Waje, Gargadin Atiku Ga Ahmad Lawan.....Daga 2015 zuwa bana Bu...
01/09/2020

Kada Ka Sake Baiwa Buhari Damar Karbo Bashi Daga Kasashen Waje, Gargadin Atiku Ga Ahmad Lawan
.....Daga 2015 zuwa bana Buhari ya karbo bashin tiriliyan 12, zuwa yanzu bashin ya ninku sai uku har ya kai tiriliyan 28, a cewar Atiku

Daga Comr Abba Sani Pantami

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya aike wasika ga shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, inda ya bukaci majalisar kada ta sake baiwa Buhari daman karban basuss**an da ba zasu haifar da 'da mai ido ba.

A wasika mai ranar watan 25 ga Agusta, Atiku ya yi kira da yan majalisar dokokin tarayya su tsagaita baiwa Buhari daman karban bashin da ba zai kawo kudi ba.

Ya ce Najeriya za ta iya shiga mawuyacin hali idan aka cigaba da karban basuss**a saboda wadanda aka karba ba abubuwan kwarai akayi da su ba.

A cewar ofishin kula da basuss**an Najeriya DMO, bashin da ake bin Najeriya kawo Maris 2020 ya kai $79.3 billion.

Za ku tuna cewa a watan Yuni, Ahmad Lawan ya sanar da cewa mambobin majalisan dokokin tarayya sun amince Buhari ya karbi bashin $28 billion.

A wasikar Atiku yace: "A ranar 29 ga Mayu, 2015, bashin da Najeriya taci ya kai Tiriliyan 12. Amma yanzu Agusta 2020, bashin ya ninku sau uku zuwa N28.63 trillion.

Abin damuwa a nan shine wadannan basuss**a basu da muhimmanci kuma ba'a bukatarsu. Binciken da akayi kan abubuwan da akayi da kudaden ya nuna cewa ba wasu ayyukan kirki masu kawo kudi akayi da su ba.

Saboda haka, a matsayinku na masu duba abubuwan da sauran bangarorin gwamnati ke yi, ina mai bukatan daga yanzu, kada majalisar dokokin tarayya ta kara bada daman karban sabon bashin da za'a yi amfani wajen ayyuka maras kawo kudi ko marasa amfani.

Gwamnatin Nijeriya Za Ta Kashe Naira Bilyan 600 Don Inganta Harkar Noma A Dukkanin Fadin KasarDaga Comr Abba Sani Pantam...
01/09/2020

Gwamnatin Nijeriya Za Ta Kashe Naira Bilyan 600 Don Inganta Harkar Noma A Dukkanin Fadin Kasar

Daga Comr Abba Sani Pantami

Ministan noma Sabo Nanono, ya ce gwamnatin tarayya na shirin ware naira bilyan 600 domin taimaka wa kanana da matsakaitan manoma na kasar, wanda hakan zai karfafa masu guiwa a daidai wannan lokaci da annobar COVID-19 ta shafi fannoni da dama dake samarwa kasar ci gaba.

Bunkasa fannin noma dai na daga cikin muhimman kudurorin da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin ingantawa, da zummar kai kasar matakin ciyar da kanta da kuma makwafta.

Ana iya cewa shirin na gwamnatin Nijeriyar na daga cikin yunkuri mai girma wajen bunkasa noman da aka gani a tarihin kasar.

Sai dai wasu masharhanta na kallon shirin ka iya fuskantar kalubale, la’akari da cewar a baya bayan nan cikin watan Agusta, kungiyar Amnesty International ta zargi hukumomin tsaron Nijeriya ta gazawa wajen baiwa mazauna yankunan karkara tsaro, inda ‘yan bindiga s**a halaka akalla mutane dubu 1 da 126 a arewacin kasar, daga watan Janairun 2020 zuwa Agustan shekarar.

JARIDAR "MUSLIM NEWS NIGERIA" TA BAYYANA MINISTA DR PANTAMI A MATSAYIN GWARZON SHEKARA A SAHUN MINISTOCIN NIGERIA Dr Isa...
31/08/2020

JARIDAR "MUSLIM NEWS NIGERIA" TA BAYYANA MINISTA DR PANTAMI A MATSAYIN GWARZON SHEKARA A SAHUN MINISTOCIN NIGERIA

Dr Isah Ali Ibrahim Pantami shine Ministan a cikin Ministocin shugaba Buhari da yake tafiya gurin aiki bisa ka'ida na karantarwan addinin Musulunci wanda ya zama abin kwatance, inji jaridar Muslim News Nigeria

Jaridar Muslim News Nigeria ta lura sosai tare da bin bahasin ayyukan majalisar zartarwa na tarayyar Nigeria wato Ministoci , inda daga bisani jaridar ta bayyana Maigirma Ministan Sadarwa da tattalin arzikin zamani Dr Isa Ali Ibrahim Pantami a matsayin Minista Musulmi da yafi dukkan Ministocin shugaba Buhari aiki, kwazo, gaskiya da kuma jajircewa

Idan za'a tuna Dr Pantami tayi rantsuwar zama Minista a gwamnatin tarayyar Nigeria ranar 21-8-2019 a karon farko tare da sauran ministoci da shugaba Buhari ya zaba don su ja ragamar ma'aikatu, wa'adin mukaminsu na Minista zai kare a shekarar 2023 tare da wannan gwamnatin

Binciken jaridar Muslim News Nigeria ya gano wasu abubuwa game da Dr Isah Ali Ibrahim Pantami masu tarin yawa:
Dr Isah Ali Ibrahim Pantami kafin ya zama Minista a 2019 shine shugaban hukumar bunkasa fasahar sadarwan zamani na Nigeria ( NITDA), a yanzu hukumar ta NITDA tana karkashin kulawar ma'aikatar sadarwa da tattalin arzikin zamani bisa jagorancin Minista Dr Isah Ali Ibrahim Pantami

Muslim News Nigeria ta gano cewa Dr Isah Ali Pantami Minista ne mai tsoron Allah wanda yake bin karantarwan addininsa wajen kokarin jaddada gaskiya da adalci wa kowa a ma'aikatar sadarwa, ya samu manyan nasarori a shekara daya kacal da yayi a mukamin Minista, wadannan nasarori da ya samu, ya samesu ne bayan tsaruka masu kyau da ya kawo akan yadda tattalin arzikin Nigeria zai habbaka, tare da magance manyan matsalolin da suke addabar ma'aikatar sadarwa fiye da karni guda wato sama da shekaru 10 da sula gabata

A shekara daya; Dr Pantami ya kawo sauyi mai ma'ana a ma'aikatar sadarwa kuma yana ta kokarin tabbatar da kudurorin da zaisa ma'aikatar ta tsayu da kafafunta domin tayi gogayya da sauran ma'aikatun sadarwa na kasashen duniya da s**a cigaba, kuma yana jagorancinsa ne bisa koyarwan addininsa da yayi umarni akan ayi gaskiya tare da yin adalci wa kowa, duk da kasancewarsa mai addini kuma Malamin addini bai taba nuna banbancin addini wa kowa ba a ma'aikatar sadarwa, abinda ya saka gabansa shine a yiwa kowa adalci musulmi da wanda ba musulmi ba, duka 'yan Nigeria ne suna da hakki bisa doka

Farfesa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami duk da kasancewarsa Minista wanda a kullun kowace rana sai ya fita aiki amma yana da lokaci na musamman da ya ware yake jan ragamar karantar da addinin Allah domin ya nunawa Musulmai da wanda ba Musulmai ba sahihiyar hanya ta samun tsira anan duniya da kuma lahira, jaridar Muslim News Nigeria ta bayyana cewa a lokacin Azumin watan Ramadan kullun sai Minista Dr Isah Ali Ibrahim Pantami ya gabatar da tafsirin Al-Qur'ani Maigirma a lokacin da akayi fama da yaduwar cutar Coronavirus (COVID-19), wanda yawanci darussa na addini da yake gabatarwa da Hausa yana yadawa a kafofinsa na sada zumunta

Ku tuna cewa wannan jarumin Minista mai tsananin rikonsa da addinin Musulunci sai daya zama mutum cikin mutane 5 a Nigeria da s**a fi kowa sanuwa a kafofin sada zumunta da na yada labarai a shekarar 2019, inda Maigirma gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Zulum ya zama na farko a cikin mutane 5, Ministan sadarwa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami baiyi kasa a gwiwa ba, ya cigaba da aiki tukuru wanda zuwa yanzu ya zarce kowa a sanuwa, ya sanu ya kuma samu lambar yabo da shaida a cikin Nigeria da wasu kasashen duniya

Wakilin jaridar Muslim News Nigeria Malam Rasheed Abubakar ya taya murna wa Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami bisa kokarin da yake yi, sannan ya shawarceshi da ya cigaba da kokari don tabbatar da shugabanci na gari a ma'aikatar sadarwa, Mallam Rasheed Abubakar yaci gaba da cewa duk da kokarin da makiya suke don ganin sunyi batanci wa Dr Pantami, hakan bai sanyaya gwiwarsa ba, ya tabbatarwa duniya cewa shi Musulmi ne na kwarai, kuma ya wanke Musulmi daga bakin fenti da makiya s**a yiwa Musulmai

Malam Rasheed Abubakar yayi kira ga sauran masu rike da madafun iko da suyi koyi da Dr Isah Ali Pantami, "..kamar yadda yake a cikin tsarin mu na Muslim News Nigeria, na yabon 'yan uwa Musulmai da s**a nuna jarunta da aiki tukuru bisa doron gaskiya da adalci, ya zama wajibi garemu muka zabi Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami a matsayin Ministan da yayi fice a cikin Ministocin Nigeria saboda aiki da kokarinsa a ma'aikatar sadarwa..", inji Malam Rasheed Abubakar

Yaci gaba da cewa; Ma'aikatar sadarwa da Dr Isah Ali Ibrahim Pantami yake jagoranta tana da matukar tasiri da muhimmanci da jan hankalin duniya zuwa matakin habbaka tattalin arzikin zamani a bangaren harkokin sadarwa na fasahar zamani da suke da matukar tasiri a wannan zamanin, Dr Pantami ya kawo baiwar ilmin harkokin sadarwa da Allah Ya masa yana shayar da al'ummah a zaman aji da kuma cibiyoyi na al'umma domin a samu kwarewa a ma'aikatar sadarwa, mutum ne mai saukin kai, ga kyautata mu'amala, yana da kula sosai gurin karban bayanai, sannan kullun yana cikin bincike da lalubo hanyar da za'a samu cigaba kamar yadda ake nunawa a kafofinsa na sada zumunta.., inji Malam Rasheed Abubakar

Yaci gaba da cewa; Ba kowani Ministan bane zai tsaya bata lokaci wajen mayar da amsar tambayoyin da ake masa a Twitter kamar Dr Isah Ali Ibrahim Pantami Ministan Sadarwa, zabarsa da akayi a matsayin gwarzo na wannan shekaran zai kara masa jajircewa wajen kyautata wa 'yan Nigeria a ma'aikatar sadarwa, ina tayashi murna, inji Malam Rasheed Abubakar mawallafin jaridar Muslim News Nigeria

Nan da wasu kwanaki kadan, jaridar Muslim News Nigeria zata wallafa muku manyan ayyuka da Dr Isah Ali Pantami yayi a ma'aikatar sadarwa da bunkasa tattalin arzikin zamani a tsakanin shekara daya da yayi a mukamin Minista

Muna fatan Allah Ya masa jagoranci, Ya kara masa taimako da nasara da kuma hakuri Amin

INA AKA KWANA GAME DA DAUKAN MA'AIKATA 774,000 A NIGERIA? ....Kungiyar "Arewa Media Writers" tana kira ga Gwamnatin Nige...
31/08/2020

INA AKA KWANA GAME DA DAUKAN MA'AIKATA 774,000 A NIGERIA?
....Kungiyar "Arewa Media Writers" tana kira ga Gwamnatin Nigeria data dubi tsarin yadda ake daukar ma'aikatan a yankinmu na Arewa, domin talakawan Arewa basu san an fara dauka ba.

Daga Kungiyar Arewa Media Writers

Kamar yadda Gwamnatin tarayya tayi alkawarin daukar ma'aikata 1000 a kowacce karamar hukuma a Nigeria mun sami labarin cewa yanzu haka an fara aiwatar da wannan shiri.

Kungiyar Arewa Media Writers ta sami korafe-korafe daga jihohi da dama musammanma Jihohin Arewa, kan yadda wakilan da aka nada don aiwatar da wannan shiri ke tafiyar dashi.

Yanzu haka wakilan da aka dauka dan yin wannan aiki sun kasa zuwa su rabawa Al-ummah haqqinsu, mun sami tabbacin cewa mafi akasarin abinda suke shine rabawa 'yan uwansu da makusantansu ba tareda bawa talakawa ba.

Da yawa daga cikin Al-ummar jihohin Arewa sunji yadda ake tsarin daukar ma'aikatan a yankin kudancin Nigeria cikin yanayi mai kyau, amma mu a Arewa saidai kaji dan Arewa na cewa baisan yadda ake daukar aikin ba.

Mafi yawanci matasan Arewa ma basu da labarin yadda ake rabawa bare takai ga an basu wanda yanzu haka tsarin yayi nisa a Nigeria.

A zantawar da kungiyar Arewa Media Writers tayi da mutane da dama daga sassa daban daban na Arewacin Nigeria kowa ya nuna rashin jin dadinsa na yadda aka danne hakkin talakawa aka kasa basu, alhalin Kuma ance anyi tsarin ne domin rage radadin talauci ga marassa qarfi daga dukkanin sassan Nigeria.

Kungiyar "Arewa Media Writers" tana kira ga gwamnatin Nigeria da shugabannin kwamitin da gwamnatin tarayya ta kafa don daukan ma'aikata dasu sanya ido kan wakilansu na jihohi musamman Arewa game da yadda suke gabatar da ayyukansu domin talakawan yankin Arewa suna korafi sosai.

Haka zalika Kungiyar Arewa Media Writers tana sake kira ga shugabannin da aka dorawa alhakin wannan aiki da suji tsoron Allah domin talakawan Arewa wanda a mune akafi samun matsalar Suna cikin halin rashi daya kamata ku tabbatar kun basu hakkin da gwamnatin Nigeria tace a basu.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yau da Gobe online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share